WAIWAYE ADON TAFIYA - IslamHouse.com
WAIWAYE ADON TAFIYA - IslamHouse.com
WAIWAYE ADON TAFIYA - IslamHouse.com
You also want an ePaper? Increase the reach of your titles
YUMPU automatically turns print PDFs into web optimized ePapers that Google loves.
١<br />
<strong>WAIWAYE</strong> <strong>ADON</strong> <strong>TAFIYA</strong><br />
(Wannan sako ne zuwa ga shuwagabanni da masanan harkokin yau da kullum na<br />
Turawan yamma, daga dakin taro na girmama hurumin Musulunci wanda a ka yi ka<br />
Kasar Kuwait)<br />
Wanda ya fassara zuwa harshen Hausa:<br />
Abdurrahman Sani Yakubu Zaria<br />
(Jami'ar Musulunci ta Madinah)
ﻢﻴﺣﺮﻟﺍ<br />
٢<br />
ﻦﲪﺮﻟﺍ<br />
ﷲﺍ<br />
ﻢﺴﺑ<br />
GABATARWA<br />
Muna farawa da sunan Allah, Ubangiji Daya, wanda babu<br />
abin bauta bisa cancanta sai Shi, Shi ne Ubangijin dukkan<br />
Annabawa: Ibrahima, da Musa, da Isa, da CikaMakonsu, Annabi<br />
Muhammad, tsira da amincin Allah su tabbata a gare su daki<br />
daya.<br />
Wasu Malamai da masana harkokin yau da kullun cikin<br />
Musulmi suka rubuta wannan sako, sun taru ne domin duba<br />
hanyar da ta fi dacewa wurin alaka da Turawan yamma, da<br />
kuma duba hanyar magance ta'addanci da suke yiwa Musulmi<br />
da Musulunci, musamman ga shi kullun karuwa abin yake yi, ga<br />
shi masu yin hakan wasu mutane ne, da kuma kungiyoyin<br />
gwamnati da na addini da na 'yan jarida. Ga sako nan zuwa ga<br />
masana harkokin yauda kullum da shuwagabannin addini da na<br />
jama'a saboda wannan abu, muna fada musu cewa: A duk<br />
lokacin da ta'addanci ya yi yawa a kan wata al'umma daga wasu<br />
mutane to dolene ta fara ramuwar gayya, kuma ta ji dalinin da<br />
ya sa hankan ke faruwa, duk da cewa abin da kowa yafi so shi<br />
ne gaba da zalunci su tsaya.<br />
Yau a duniya babu wata al'umma da take gamuwa da<br />
zalunci da kuma mamayar Turawa kamar yadda al'ummar<br />
Musulmi ke gamuwa da shi, kuma a duniyar yau babu wata<br />
al'umma da take gamuwa da izgili da wulankanci game da<br />
hurumominta da addininta, kamar yadda wannan al'umma take<br />
gamuwa da shi, wannan al'umma baza ta karbi wannan al'amari<br />
ba, musammam ita al'umma ce wadda take da sako daga sama,<br />
kuma take da cigaba da tarihi mai asali, kuma ga mutanenta sun<br />
fi daya bisa hudu (25 %) na mutanen duniya. Shi ya sa muka ga<br />
ya wajaba mu jawo hankalin mutane da su waiwaya baya su<br />
kalli abubuwan da suke faruwa, ko a samu a gyara kurakuran da<br />
suke faruwa, daga nan sai tafiya ta yi kyau.
٣<br />
YA ALAKARMU DA TURAWA TAKE YANZU?<br />
Mun sani tun lokacin da musulmi suka fara gogayya da<br />
turawa alakar da take tsakaninsu ta yi tsami, saboda dalilai masu<br />
yawa, daga cikin dalilan: Lalle turawa ba su yin mu'amala da<br />
Musulunci gaba da gaba, koda yaushe suna cikin fargaba da<br />
tsoro, wannan shi ya sa su ka yi kokarin hada kawunansu don su<br />
yaki Musulunci, duk da cewa akwai rashin jituwa kai a<br />
tsakaninsu, daga nan sai Musulunci ya zama babban abokin<br />
gabansu, duk da cewa da sun kasance a rarrabe suna yakar juna,<br />
dukkanmu mun san cewa ba dai-dai ba ne yiwa kowane abu<br />
kudin goro, kuma mun sani cewa a karnonin da suka shude<br />
Amurkawa da sauran Turawan yamma sun yi kokarin rabuwa da<br />
aiboban da ke cikin al'adunsu, wurin mu'amala da wasunsu, sai<br />
dai kash! Yanzu sun manta da wannan al'amari, saboda haka<br />
wannan wasika ba tana magana da musu kiyayya da musulunci<br />
ne kawai ba, tana magana ne da duk wani bature, musamman<br />
masu adalci a cikinsu, kuma mun sani ba duka Turawan suka<br />
taru suka zama daya ba.<br />
MISALAN TA'ADDANCI DA CIN MUTUNCI DA<br />
SUKEWA MUSULMI DA MUSULUNCI.<br />
Lalle muna jan kunnen shuwagabanni Turawan yamma<br />
game da abubuwan da suke ta faruwa, muna kallo a cikin kasa<br />
da shekaru uku an keta huruminmu ba sau daya ba, fara daga<br />
ALKUR'ANI MAI GIRMA, ta yadda suke buka su watsa wasu<br />
litattafai wadan da a zatonsu makwafin Alkur'ani ne, a cikinsu<br />
akwai izgili ga Annabimu da addininmu da akidarmu da<br />
halayenmu da tarihinmu. Bayan haka sai suka kara da cin<br />
mutunci Annabinmu (S.A.W) suna kamanta shi da kamannu<br />
marasa kyau, suna zana hotonsa zane na wulakanci da izgili.<br />
Jaridar kasar "Denmark" ta fara hakan, sai sauran kasashen suka<br />
koya daga wurin ta, wasu wa sa albarka suka yi a cikin aikin.<br />
Daga nan sai ciwon ya kara girmama yayin da "Papa Roma" ya<br />
fito fili ya soki Alku'ani da Manzon Allah (S.W.A) suka irin na<br />
rashin kunya.<br />
Kuma ba mun manta da abin da sojojin Amurka suke yi ba<br />
ne a kurkukun "Abu Guraib" na kasar Iraki, da kuma kurkukun<br />
"Gointanamo" na kasar "cuba" ta inda suke wulakanta Musulmi
٤<br />
da Littafinsu (Alkur'ani). A gefe daya kuma koma yana ganin<br />
abin da ke faruwa a manyan garuruwan Turai na cin zalun<br />
musulmi mazauna wadannan garuruwa. Kuma ba zamu iya<br />
manta abin da ke faruwa Iraki da Afganistan ba, wanda Amurka<br />
ta mamaye, kullum ana kai wa masallatai hari, hakanan kurun,<br />
ko da hujjar wai ana neman masu rike da makamai, wani lokaci<br />
a kashe duk wanda yake cikin masallacin.<br />
Kuma akwai maganganu na kiyayya da shuwagabannisu<br />
suke yawan furtawa, ko abin da marubutansu suke rubutawa, ko<br />
abubuwan da suke watsawa a gidajen Talabijin da radio ko<br />
jaridunsu da mujallu, wadanda suke kamanta Musulmi da<br />
nakasu da ta'addanci.<br />
Lalle shirun da manyaku suke yi a kan wadannan abubuwa<br />
yana bamu tsoro! Mun rasa ina zama sa ku? Wannan shine<br />
'yancin dan adam din? Ko dai rashin 'yanci? Shin kuna<br />
wulakanta Annabawan Allah da suna 'yancin ra'ayi?<br />
SUNA WULAKANTA MANZON ALLAH (S.A.W)!<br />
Duk da cewa akwai al'ummomin da suka yaki Musulmi,<br />
amma duk da haka ba a same su da gadon kiyayya ga Annabin<br />
Musulmi ba, kamar yadda a ka samu kasashe da coci-coci na<br />
turai suna yi masa ba, hakika kiristocin Turai, sun kafa gaba da<br />
Musulmi da Annabinsu gaba na tarihi, har abin ya kai haddin<br />
tunawa juna idan an hadu a coci a lokacin bukukuwan addini.<br />
Wannan abu ya cancanta mutsaya mu duba sababinsa da hanyar<br />
magance shi.<br />
Wai menene ya sa wasu muatane a Turai suke kokarin sai<br />
mun manta da manyanmu kuma abin koyinmu? Lalle ne duk<br />
wanda ya rayuwa ba shi da na gaba, to, tababbe ne shi! Kuma<br />
duk al'ummar da ta manta da tarihinta, to, kamar gini ne babu<br />
asasi, (wadan nan su ne dalilanmu) to, saboda haka ne kuke<br />
walakanta Annabinmu? Lalle mun sani cewa abin da lalatattu a<br />
Turai suke so shi ne mutane su manta tarihinsu, musamman<br />
musulmi, babban misali a kan haka shi ne abin da ke faruwa<br />
yanzu na yiwa Annabawa izgili. To ya kamata su sani cewa<br />
munanan daram dakam wurin tare wa Annabinmu, da ma sauran<br />
Annabawa baki daya, wannan abin ba zai samu karbuwa a wurin
٥<br />
mu ba, wai da sunan 'yancin bayyana ra'ayi, ba zai taba yiwuwa<br />
ba, Musulmi su yarda da dattin tunanin Turawa ba, kamar yadda<br />
suma basu yarda da namu 'yancin dan adam din.<br />
Lalle muna kira da babban murya cewa, masu hankalin<br />
Turai su tsaya su kalli wannan lamari da idon basira, kuma mun<br />
sani a cikin su akwai masu kwadayin duk abin da zai gyara<br />
tarihin su a wurin mutane, ba abin da wasun su suke yi na cin<br />
mutunci mutane ba, musamman Annabawa.<br />
TA'ADDANCI GA MASLLACIN KUDUS (Masallacin duk<br />
annabawa)<br />
Mamaye masallacin Kudus da yin ta'adda gare shi, lalle<br />
yana daga cikin ta'addanci ga murumin musulmi, kuma hakan<br />
yana faruwa da taimakon wasu gwamnatocin Turai ne, da kuma<br />
goyon bayan wasu kungiyoyin addini a can, hakika hakkin<br />
"veto" a majlisan dinkin duniya, ya zama hakkin Yahudawa, su<br />
kadai yake karewa, kuma yake goyon bayan ta'addancin su, da<br />
mamayar su ga "Palastine" da masallacin Kudus, wanda har<br />
gobe baza mu taba barin musu shi ba! Kuma muna sake<br />
tambayar masu hankali cikin Turawa, wai menene kuka yi wurin<br />
magance zalucin da a ke yiwa Musulmi a "Palastine", da keta<br />
huruminsu, da kuma hana musu hakkokinsu.<br />
Abin a kwai tukka da warwara, kullum suna kiran<br />
musulmi da su zo su yi "Democracy" (dimukradiyya) lokacin da<br />
Falasdinawa suka zabi hukumar da suke so ta mulke su, sai ga<br />
shi sun fito fili suna fada da hakan. Lalle shirun da manyansu<br />
suke yi akan hakan, to abin kunya ne a goshin duk wanda yake<br />
da'awar 'yanci da dimukradiyya a duk duniya. Saboda haka<br />
muke kira gare su da su yi kokari wajen share wannan abin<br />
kunyan da yake tare da su, wurin hada kai da masu adalci, kuma<br />
masu kare hakkin dan adam na gaskiya, masu kokarin sai sun ga<br />
an baiwa kowa hakkinsa.<br />
IZGILI GA HIJABIN MACE MUSULMA.<br />
'Yancin kai yana da goyon baya a dimukradiyyar Turai,<br />
kamar yadda suke shela koda yaushe, saboda haka mace tana da<br />
hakkin sanya abin da take so, idan dai bai sabawa al'adun<br />
mutanen kwarai ba, sai dai abin mamaki shi ne, an sami wasu
٦<br />
suna walakanta hijabi da mace mai hijabin, wanda wannan shi<br />
ne ainihin tikka da warwara, kullum suna kokarin yada<br />
dimukradiyya, amma wannan ya sabawa abin kira a kai, kuma<br />
babu wata kungiyar kare hhakkin mata ta duniya da ta sa baki<br />
warin abin da yake faruwa. Shin 'yancin fita tsirara shine 'yanci<br />
kuma za a kare shi, amma 'yancin kamun kai da kunya ana<br />
yakan shi?!<br />
Ya kamata masu kokarin yada hakkin dan amdam na Turai<br />
su yi kokarin tsarewa mutum asalinsa da al'adansa ne, ba yakan<br />
su ba, ta ya suna kallo ana yakan Musulmi mazauna can. Wurin<br />
zabar kayan da suke so? Ko sun manta da abin da suka gada<br />
daga addinin su da al'adun su ne? har yanzu ana samun wasu<br />
matan turawa masu kunya suna sa kayan mutunci, wanda yana<br />
kama da hijabin Musulmi, kamar matan kauye, da matan da<br />
suka rike addini. Shin idan su sun saki wadannan al'adu, sai ya<br />
zama dole mu ma sai mun saki na mu? Hakika muna kyamar<br />
yaki da ake yi da kamun kai, kuma wannan bai kamata a ce shi<br />
ne sakamakon wayewa da cigaba ba, shin wai hijabi shi ne ya<br />
zama alamar kama kai da a ke yaka a Tirai? Hakika dokokin da<br />
ake kafawa saboda hakkin mace saboda tasa hijabin Musulunci,<br />
to a mafi yawan kasashe Turai a na kafa su ne domin daga baya<br />
a hanata sa hijabin; wai wannan duk saboda gaba da Musulunci<br />
ne, kama yadda ya bayyana kwanannan? Ko saboda gaba<br />
dakamun kai ne? ko saboda 'yan iskan gari su ji dadi? Ga<br />
tambayoyi suna bukatar amsa daga wurin masu tunani a Turai,<br />
kuma wajibi ne su bayyana tukka da warrar da take cikin<br />
wannan lamari.<br />
YAKAR TUNANI.<br />
Hakika manyansu da shuwagabannin addininsu sun fito fili<br />
su tuhumci Musulunci da tuhunce-tuhumce da baban-daban a<br />
kwanannan, kamar: "Lalle Mususlunci bai wasu ba sai da tilasci<br />
da takobi" ko kuma "ba a amfani da hankali a cikinsa" ko kuma<br />
"Lalle Musulunci addinin ci baya da ta'addanci ne" da sauran su,<br />
wannan sako ba zai maida hankali warin karyata wadannan<br />
tuhumce-tuhumcen ba, sai dai za mu yi bayani cewa lalle<br />
wadannan tuhumce-tuhumcen ba su dacewa da yadda a ke
٧<br />
muhawara a ilmance, sun yi kama ne da kokarin yakan tunani da<br />
wasu kungiyoyi masu karfi a Amurka suke yi don kokarin<br />
canzawa Musunci riga.<br />
Mun yarda cewa Musulunci ya watsu ta hanyar jihadi "fi<br />
sabilil lah", da hanyar Da'awa cikin kwanciyar hankali, kuma ko<br />
wata daula tana bukatar karfi wurin kare tushenta da abubuwan<br />
da ta mallaka. Dalilin haka abin da a ke kira yaki mai adalci<br />
"just war" shi ne cocin Turai ya kafu a kai kua ya yarda da shi,<br />
kuma da shi 'yan ba ruwan mu da addini na Turai suke yin abin<br />
da suke so a duniya, to na saboda me za a tsangwami<br />
Musulunci? Alhali kun sani kuma tarihi ya tabbatar cewa<br />
"Indonesia" da "philipis" da "Malasia" da wasu daga kasashen<br />
Afrika ba sojan da kafarsa ta taka wadannan kasashe, to ta yaya<br />
wadannan miliyoyin mutane suka shiga Musulunci? Tambayar<br />
da ya kamata mu yi a nan ita ce: me ya sa har yanzu Musulunci<br />
yake watsuwa a duniyi? Musamman a turai? Su ma takobin ne?<br />
Sam, tasirin da ya ke yi ne a zuciyar duk mau hankali.<br />
Amma amfani da hankali a cikin Musulunci kuwa, shimfidar da<br />
zamu yi anan ita ce: Hakika tarihi ya tabbatar da cewa Turawa<br />
su ne ba suka watsar da hankali a bayansu, wasu kuma suke<br />
wauta masa, wato imma a yi wannan, ko a aikata kishiyarsa, a<br />
dai-dai wannan lokaci kuwa, Musuluci adalci yake yi game da<br />
amfani da hankali, da amfani da shi warin yiwa dan adam<br />
hidimar da ta kamata, wai me ne ya sa wasu shuwabannin addini<br />
a turai suke sukan Musulunci ta bangaren hankali? Saboda kin<br />
gaskiya ne da boye nakasun da yake tare da su? Ko domin su<br />
taya 'yan baruwan mu da addi yaki da Musulunci?<br />
Lalle muna kira ga shuwagabanin addininsu, da su yi<br />
muraji'ar akidunsu musamman akidar Uluhiyya, a lokacin za su<br />
san tikka da warwarar da take cikin akidarsu, wanda rashin<br />
amfani da hankali ya jawo musu. Hatta boren da a ka yi musu<br />
gaban da suke yi da hankali da ilimi ya jawo musu, kuma shi ya<br />
sa kin addini ya mamaye kasashen su.<br />
Amma abin da ya watsu a turai na tuhumar Musulmi da<br />
Musulunci da abin da suka sawa suna ta'addanci, to, tuhuma ce<br />
ta zalunci, bata da asasi a tarihi balle a sarari, al'ummar Musulmi<br />
da a ka sani da rahama da kyautatawa. Lalle muna kiran turai da
٨<br />
su yi kokari su bar abin da suka gada na gaba da Musulunci tun<br />
lokacin da suka yaki Musulmi da sunan yakin salib (yakin<br />
kiristanci) wannan shi ne asalin ta'addanci, kuma duk wanda<br />
yake kiran mu 'yan ta'adda a yau, to shi ne babban dan ta'addan<br />
da ya kashe kuma yake kashe moliyoyin 'yan adam, yakin<br />
duniya na daya da na biyu Musulmi suna da hannu wurin tada<br />
su?<br />
Lalle masu tunani a Musulmi za su iya lura da canjin da ya faru<br />
daga wasu masu gaba da Musulunci daga yaki da Musulmi zuwa<br />
yaki da Musulunci, kuma daga kokarin canza Musulmi zuwa<br />
kokarin canza Musulunci. Muna fada musu cewa lalle<br />
Musulunci baya bukatar kwaskwarima kamar yadda suka yiwa<br />
addinin su, Musulunci an san shi addini ne kammalalle kuma<br />
har yanzu yana watsuwa ba tare da canza wani abu a cikinsa ba.<br />
Hakika zumudi ya debi wasu shuwagabanni turai wurin neman<br />
wasu kyara-kyare a Musulunci, addinin da ba su san kome a<br />
cikinsa ba, kawai abin da suka sani game da shi, shi ne lalle shi<br />
wani addini ne da ya sabawa kiristancinsu na zamani, wanda ya<br />
cakuda da lebralancin turai domin ya zama wani sabon addini,<br />
wanda dole ne duk wanda ya saba masa ya yi kokarin kyara<br />
tafiyarsa don ta yi dai-dai da wannan sabon addinin.<br />
Lalle mu mun sani cewa addininmu da babu wanda ya isa<br />
ya ce zai iya canza wani abu a cikinsa, ya isa ya zama maganin<br />
duk wata mushkilar da take damun turai, shi ya sa wasu suke<br />
kikarin rabuwa da Musulunci rabuwa ta karshe, kuma zamar<br />
Musulunci ba a canza kome a cikinsa ba ya na karyata abin da<br />
wasu suke zato cewa sune karshen tarihi.<br />
Lalle mu muna kin duk wani kokarin hana al'ummarmu<br />
damar ta gina tunaninta yadda take so, a lokaci daya kuma muna<br />
bayyana cewa lalle mun yarda da leka al'adun wasu da daukan<br />
mai amfani a ciki, kuma muna bayyana cewa lalle tunanin<br />
turawa wurin akidunsu da dokokinsu da al'adunsu ba karbabbe<br />
ba ne a duniyance, kuma ba mai tsarki ba ne. kuma duk wani<br />
kokarin sa shi ya zama haka, ba zai yi amfani ba. Lalle Musulmi<br />
sun sani cewa yakin da turai suke yida Musulunci, da sunan<br />
yakin tunani ba wani abu ba ne face tsoron cigaban Musulunci,<br />
wanda zai hanasu mamaye ko'ina.
٩<br />
Abin da kuke kira yakin tinani, abu ne da bamu yarda da<br />
shi ba, kuma ba za mu bar kare mutuncin addininmu ba, saboda<br />
mun lura cewa filin yakin tunani shi ne filin al'ummarmu, amma<br />
yakinin da muke da shi ya sanya bamu tsoron wani abu zai iya<br />
girgiza abin da muki yi imani da shi, kuma zamu iya bayyana ko<br />
gyara abin da ya batawa turai tunaninsu a cikin akidunsu, da<br />
suransu.<br />
YA MUKE FAHIMTAR TA'ADANCIN DA SUKE YIWA<br />
HURUMINMU?<br />
Daga abin da shuwagabanninsu suke fadi, ko wasunsu<br />
suke rubutawa zamu iya fahimtar cewa lalle yakin da suke yi da<br />
Musuluncin ba aikin Mutun daya ba ne, ko kuma ramuwar<br />
gayya saboda wani abu da a ka yi musu, wani shiri ne da a ka<br />
zauna aka shirya domin a takura musulmi a duniya, kuma shi ne<br />
ya fito fili a cikin maganar shugaban Amurka " J. W. Bush"<br />
yayin da ya ce: "wannan yaki da yake yi yakin addinin ne"<br />
wanda daga baya ake cewa yaki da ta'addanci, a Iraki da<br />
Afganistan da wasu wuraren da dama. Kuma shi ne maganar<br />
faraministan Italiya "sifo" ya yin da tuhunci Musulunci da<br />
tuhuma ta zalunci, kuma ya dauki Musulunci wai addini ne na ci<br />
baya, kuma ya manta aikin Musulunci a tarihi mai tsawo.<br />
"Adviser" Jamus ma ya fadi irin wannan magana, har yana<br />
cewa: "baza a bar Musulunci ya firgita ciganban turai ba"<br />
A nan tambaya zata zowa mutum cewa: shin mene suke<br />
nufi da wannan cin mutunci da ba ya karewa? Idan domin<br />
'yancin ra'ayi ne, to me ya sa ba bu hawa kan sauran addinai<br />
kama addinin mutanen Indiya da Yahudawa da Budanci da<br />
sauran su? Musulunci kawai a ke yaka, wannan sh ne ya ke<br />
karyata abin da suke fada koda yaushe. Shin ko abin da ya faru<br />
kwanannan shi ne dalilin wannan yaki? Lalle ba za mu yarda da<br />
wannan maganar ba; saboda yakin da suke yi da Musulunci yana<br />
nan tun kafin wannan abin da ya faru suka tuhumi wa su<br />
Musulmi da ta'addanci.<br />
Wasu masana lamuran yau da kullum daga Musulmi suna<br />
ganin abin da ke faruwa yanzu na yaki da Musulunci da<br />
ta'addanci a kan huruminsa dalilinsa shi ne: ganin turai
١٠<br />
Musulunci ya fara maida karfinsa da ya rasa kuma ya fara<br />
farkawa daga barcinsa, saboda ya cigaba da aikinsa na kyara dan<br />
adam da jiyar da shi dadi. Kuma abokin rige-rige wurin cigaba<br />
da tunani.<br />
Lalle muna ba maganar kungiyar yafiya a addini na kasar<br />
"Canada"mahimmanci yayin da su ka ce yawan Musulmi a<br />
duniya a shekarar 2003 biliyon 1,226 19 % na mutanen duniya a<br />
wancan lokacin, kuma suka tabbatar cewa addinin Musulunci<br />
shi ne addinin da masu shigansa suke karuwa, a lokacin da<br />
sauran addinan suke raguwa, kuma kungiyar ta kara da cewa<br />
nan da shekara ta 2023 Musulunci shi zai zama addinin farko a<br />
duniya, shin wannan magana ita ce ta sanya tsoron da ya ke<br />
cikin zukatanku ya dawo? Muna tambaya?<br />
Har ila yau muna ganin tikka da warwara game da sha'anin<br />
turai, kullum suna maganar 'yanci da dimukradiyya amma a<br />
lokaci daya suna hana Musulunci 'yancinsa a kasashensu,<br />
saboda kar Musulmi su dauki addininsu abin bi a cikin harkokin<br />
rayuwar yau da kullum. Kuma suna zuga wasu su cutar da su<br />
har a cikin gudajensu, da kuma kokarin yin musu mulkin<br />
mallaka.<br />
Lalle mun lura cewa gaban da wasu shuwagabanni da<br />
sauran mutanen turai suke yi da Musulunci ta gidajen sadarwa<br />
suna ganinsa dai-dai ne, kuma bakin shuwagabanninsu da<br />
gidajen sadarwarsu daya wurin gaba da Musulunci.<br />
Kuma wannan yakin da gidajen sadarwan suke yi ya haifar<br />
da wata matsala mai girma, ita ce hana wasu shiga addinin Allah<br />
Madaukakin Sarki. Kuma masana addinin kiristanci a cikinsu<br />
suna da hannu cikin wannan yaki, wurin boye hakikanin<br />
Musulunci, da kuma aibanta shi, da kokarin kore mutane daga<br />
gare shi, da kuma boye bisharar da a ka yi na zuwan Annabi<br />
Muhammad (S.A.W) a cikin Attaura da Linjila.<br />
Kuma akwai wani abu, shi ne yakan wasu rubuce-rubuce<br />
da wasu masu adalci a cikinsu suke yi, idan sun yiwa Musulunci<br />
adalci, sai ka ga a na kai musu farmaki da karfi, wanda zai ba ka<br />
tabbas cewa akwai wasu jama'a a turai maslaharsu ita ce su<br />
nunawa 'yan'uwansu aibun Musulunci da Musulmai.
١١<br />
A KARSHE:<br />
Lalle tattaunawa tsakanin al'ummomi yana da<br />
mahimmanci, musamman idan za a yi shi akan ka'ida saboda a<br />
samu zuwa hakika, kuma a samu tsayar da ta'addanci babu gaira<br />
babu dalili, kuma muna tabbatar musu da cewa fahimtar juna zai<br />
yiwu, idan za a lizimci adalci.<br />
Lalle cigaban turai a yau baya nuna cewa daga wurin su<br />
abin yake, a a, cikaban al'ummomi suka tara a wuri daya (daga<br />
ciki har akwai Musulmi) sai dai yanzu suna kokarin ninawa<br />
dunuya a su kadai ke da shi, kuma suna hana Musulmi duk wani<br />
abun da zai sa su su cigaba, sai su shagala da fadace-fadacen da<br />
su suke kunna su. (su kuma sai su yi gaba)<br />
Tuntuben da muke samu wurin cigaba da kere-kere saboba<br />
wasu dalilai, ya sha bamban da abin da muke kai a da, kuma<br />
wannan tuntuben ba ya nuna wai an barmu a baya, a wurin<br />
cigaba da halaye masu kyau, mun mallaki abu mai yawa na daga<br />
al'adu da halaye masu kyau, da mabubbugan shiriya da haske,<br />
kuma ba zai yuwu mu yi wasa da su ba, ko mu bar kiran mutane<br />
zuwa ga wannan hasken.<br />
Muna kiran ku da ku sake waiwaya baya game da finkarfin<br />
da kuke yiwa mutane cikin al'adunsu, kuma muna kara fadawa<br />
manyansu, su lizimci adalci game da Musulunci da al'adunsa<br />
masu girma, da kuma aikin da yakewa dan adam tun da har<br />
yanzu.<br />
Zai iya yiwuwa halin da muke samu kanmu a ciki yanzu<br />
mawuyacin hali ne, amma tushen akidarmu da shari'armu da<br />
halayenmu har yanzu masu kyau ne, kuma sun dace da duk wani<br />
zamani ko wani wuri. Idan muna ganin turai sun cigaba a zahiri,<br />
amma tushen cigaban na su ba shi da amfani ga dan adam kome<br />
zawon zamani, muna kara fada muku cewa duk da cewa akwai<br />
wasu aiboba a tare da mu a halin yanzun, amma duk da haka ba<br />
zai sa mu kasa ganin mahimmanci al'dunmu da addininmu ga<br />
dan adam, kuma muna kiranku da babban murya kuma manyan<br />
turai, da ku masu yakin Musulunci a madadin sauran mutane,<br />
muna son ku kiyaye wadannan abubuwa kamar haka:<br />
NA DAYA: Ku bar zaluntar mu, da yi mana shishshigi a<br />
lamurranmu, ko yi mana ta'addanci kan huruminmu, saboda
١٢<br />
wadannan abubuwa zasu cutar da ku ta bangaren kasuwancinku<br />
a kasashenmu, kuma hakan ba zai yiwu ba sai kun yiwa kanku<br />
adalci.<br />
NA BIYU: Muna kiran ku da ku taya mu fada da abin da 'yan<br />
jarida suke bazawa na batunci a kanmu, ko taba Alkur'aninmu,<br />
ko Manzonmu (S.A.W) amma idan sun cigaba da hakan, to<br />
muna zamu dauki mataki akan abin.<br />
NA UKU: Ku yi kokari wurin karantar sabubban da suka sa<br />
tsamin alaka tsakaninmu, maimakon kokarin mamaye mu da<br />
bangaren siyasa da kasuwanci da harkan soji, kuma ku tsaya ku<br />
fahinci sakon da a ka aiko Annabi Muhammad (S.A.W) kuma<br />
ku bude zukatanku ku fahinci Musuluncinmu cewa ya dace da<br />
duk duniya, kuma ku fahinci hakikanin addininmu da al'adunmu<br />
fafin ku yake mu, ko ku tare mutane wurin karban sa.<br />
NA HUDU: Lalle shuwagabannin turai su yi kokin gyra aibobin<br />
da suke cikin al'adunsu na yanzu kafin su ce zasu gyara na wasu:<br />
hakika turai suna bukatar gyara da gaske, wannan ya fi da<br />
wannan kokarin da suke yi wurin sai sun canza duniyar<br />
Musulmi. Lalle ne idan ba hakan suka yi ba, to suna dab da su<br />
fada wani rami mai zurfi wanda zasu kasa fitowa, idan dai sun<br />
ce zasu cigaba da zaluci, saboda duk wadannan aibobin zasu<br />
koma kansu ne su da masu taimaka musu su hallaka su. Lalle<br />
muna kira zuwa ga shuwagabanninsu su yi kokin gyara halin da<br />
kasashensu suke ciki, don su koma su bi hanyar Manzonnin<br />
Allah, kuma su gimama su dukkan su, cira da amincin Allah su<br />
tabbata a gare su, kuma su rinka taimako wadan da basu da laifi,<br />
kuma su hana zalunci da cutarwa, aduk duniya ba a turai ba<br />
kawai. Kuma muna sake kiran su da su gyra abin da ya shafi<br />
aure da iyali da kamun kai, kafin su ce zasu gyra mu, kuma su<br />
kare mutum daga ta'addancin kamfanoni da 'yan jari hujja, kuma<br />
su girmama al'adun mutane kafin su kalli ribar da zasu ci, kuma<br />
a yi kokari a dawo da kimar Malamai da karatu a duniya. Lalle<br />
wannan abu ne da lokaci ya yi da a fara aikata shi, saboda rashin<br />
addini yana kawo rushewar kome a duniya.<br />
NA BIYAR: Wajibi ne turai su nemi afwa game da wulakancin<br />
da suka yiwa Musulunci, haka kuma su nemi afwa game da duk<br />
wani laifi da suka yiwa Musulmi lokacin mulkin mallaka da
١٣<br />
kafin wannan lokacin da bayansa, kuma wajibi ne su san inda<br />
zasu yi amfani da karfi a duniyar da al'adu sun sha bamban.<br />
Amma sakonmu ga wanda ya dage sai ya yaki Musulunci<br />
shi ne, lalle bai bar watsuwa ba saboda yakin da a ke yi ba shi<br />
tun da, haka kuma ba zai bar yaduwa ba har sai Allah ya nade<br />
kasarSa da wadan da suke kanta, kuma lalle wannan al'umma<br />
zata iya dawowa da kaefinta bayan ta yi rauni, kamar yadda<br />
kowa ya sani a tarihance<br />
Mu kuma ba zamu takaita a kare huruninmu da addininmu<br />
kawai ba, zamu mai da hankali wurin tunawa masu gaba da dan<br />
adam asiri, kuma da sannu mutanen turai zasu gane cewa abin<br />
da masu gaba da Musulunci suke yi cutar da turai yake yi fiye<br />
da yadda yake cutar da Musulmi, kuma zai haranta musu fa'idan<br />
tuwa da mutum biliyon daya da kwata, kuma suna da karfi<br />
wurin yin ciniki a dunuya, kuma suma sun mallaki abubuwa<br />
masu waya da ake takama da su a duniya. Kuma sun daurawa<br />
kansu nauyin wanzar da adalci a duniya.<br />
Lalle bude ido game da abin da turai ke da shi warin<br />
cigaba baya nufin mutaru mu zama iri daya da su, mu bama son<br />
bin turai rididi, ko waninsu, duk da haka bamu hana anfawa da<br />
kere-kerensu ba, da amfanuwa da juna.<br />
Lalle muna kira zuwa ga shuwagabannisu da su karanci<br />
hakikanin Musulunci da Musulmi, dalilinmu a nan shi ne fadin<br />
Allah Madaukakin Sarki, kuma da shi zamu rife wannan sako:<br />
ﺎﺌﯿ ﺷ ﮫﺑ كﺮﺸﻧﻻو<br />
ﷲا ﻻإ ﺪﺒﻌﻧ ﻻأ ﻢﻜﻨﯿﺑو ﺎﻨﻨﯿﺑ ءاﻮﺳ ﺔﻤﻠﻛ ﻰﻟإ اﻮﻟﺎﻌﺗ بﺎﺘﻜﻟا ﻞھأ ﺎﯾ ﻞﻗ"<br />
لآ)"<br />
نﻮﻤﻠﺴ ﻣ ﺎ ﻧﺄﺑ وﺪﮭ ﺷا اﻮ ﻟﻮﻘﻓ اﻮ ﻟﻮﺗ نﺈ ﻓ ﷲا نود ﻦ ﻣ ﺎﺑﺎﺑرأ ﺎﻀﻌﺑ ﺎﻨﻀﻌﺑ ﺬﺨﺘﯾ ﻻو<br />
( ٦٤ ناﺮﻤﻋ<br />
Ma'ana: Ya ku mazuwa littafi! Ku taho zuwa wata kalma wadda<br />
zamu yi dai-dai da ku, kar mu bautawa kowa sai Allah, kuma ba<br />
za mu hada shi da wani abu ba,<br />
kuma sashinmu ba zai riki sashi iyayen gida ba Allah ba, to idan<br />
suka bada baya, to ku fadi lalle mu mun shaida lalle mu<br />
Musulmi ne. (Al Imran 64)