11.01.2013 Views

مﻮﻴﻟا ﻢﻜﻴﻠﻋ ﺐﻳﺮﺜﺗ ﻻ

مﻮﻴﻟا ﻢﻜﻴﻠﻋ ﺐﻳﺮﺜﺗ ﻻ

مﻮﻴﻟا ﻢﻜﻴﻠﻋ ﺐﻳﺮﺜﺗ ﻻ

SHOW MORE
SHOW LESS

You also want an ePaper? Increase the reach of your titles

YUMPU automatically turns print PDFs into web optimized ePapers that Google loves.

JAWABI WAJEN BIKIN AURE<br />

A yau, mun hadu a walimar auren Dr. Zahoor da amaryar sa Asma Rizvi. Ina taya<br />

ku murna da sauran jama'ar da suka hallara a wannan wuri. A koda yaushe<br />

muna fatan irin wannan haduwa wadda zata tattara abokai da 'yan uwa da kuma<br />

abokan aiki daga kasashe da kuma addinai dabam-daban, domin ba karamin jin<br />

dadi bane kasancewar mu a wannan wuri, musulunci ya tsara ko kuma ya maida<br />

irin wadannan shagulgula su kasance masu ma'anar gaske.<br />

Su dai Musulmi, mabiya tsari irin na Annabin Rahma Muhammad (sallallahu alaihi<br />

wa sallam), kan fadakar da sabin ma'aurata, da kuma wadanda suka yi auren tun<br />

tuni da ma masu son su yi aure nan gaba bisa hakkokin su ko kuma nauyin da ke<br />

rataye a wuyan su. A na yin wannan ne kuwa domin ita rayuwar aure tana da<br />

muhimmancin kwarai a wurin Allah SWT. Kai in muka yi dubi sosai cikin Al-<br />

Qur'ani Mai Girma zamu ga cewa Allah SWT ya yi bayanin rayuwar aure da fadi<br />

fiye da duk sauran nau'o'in ibada (bayan tauhidi). Nagartacciyar rayuwar iyali ita<br />

ke gina al'umma ta gari, wannan kuma shi zai samar da nagartacciyar rayuwa a<br />

cikin al'umma.<br />

Da farko muna godiya ga Allah SWT wanda shine ya halatta aure.<br />

Allah SWT ya fadi cewa :<br />

�ﺎﻔﻴﻌﺿ نﺎﺴﻧﻹا ﻖﻠﺧ و�<br />

Ma'ana: "Kuma an halitta mutum yana mai rauni" (An-Nisa: 28).<br />

Idan aka ce a rayuwa kowa ya tsaya shi kadai (babu aure) har abada abin da<br />

wuya ta bangarori da dama. Allah SWT bai kirkiri rayuwar aure kawai ba, amma<br />

ya ma kwadaitar damu yi aure da a kan kari, domin shine hanya nagartacciya<br />

tabbatacciyar da zamu iya kare rauni irin na dan Adam. Ta wannan hanya ne<br />

mutane biyu daban da suka fito daga wuri daban za su amince wa junan su ta<br />

hanyar soyayya da mutunta juna su zauna tare. Allah SWT da ya halatta yin aure<br />

bai bar mu kara zube ba, ya bayyana yadda za a cimma nasara a rayuwar aure<br />

kamar yadda ya fada a Suratur-Rum aya ta 21:<br />

ةدﻮﻣ ﻢﻜﻨﻴﺑ ﻞﻌﺟ و ﺎﻬﻴﻟإ اﻮﻨﻜﺴﺘﻟ ﺎﺟاوزأ ﻢﻜﺴﻔﻧأ ﻦﻣ ﻢﻜﻟ ﻖﻠﺧ نأ ﻪﺗﺎﻳﺁ ﻦﻣ و<br />

. نوﺮﻜﻔﺘﻳ مﻮﻘﻟ تﺎﻳﻵ ﻚﻟاذ ﻲﻓ نإ ﺔﻤﺣر و<br />

Ma'ana:<br />

"Yana daga ayoyin sa (Allah SWT): (shine yadda) ya halitta maku matan aure<br />

daga kan ku domin ku sami natsuwa daga gare su kuma ya sanya soyayya da<br />

rahama a tsakanin ku, hakika a cikin wannan akwai ayoyi ga (mutane) masu<br />

tunani"


A nan manufar yin aure shine samun kwanciyar hankali da jin dadi da darajta<br />

juna.<br />

Wannan zaman lafiya ba zai samu ba sai ta hanyar soyayya ta hakika tsakanin<br />

ma'aurata, daga kowa ne daya daga cikinsu zuwa dayan, ba wai daga bangare<br />

daya kawai ba. A wannan ayar da ta gabata, kalmomi guda biyu an yi amfani da<br />

su tare da juna domin bayyana wannan soyayya ta hakika a tsakanin ma'aurata.<br />

Ta farko ita ce 'mawaddah' dayar kuma itace 'Rahmah', duka suna nufin soyayya,<br />

malamai sun yin bayanin mawaddah ita ce soyayya dake wanzuwa a tsakanin<br />

ma'aurata lokacin da suke a halin samartakarsu ko a lokacin farko na aurensu,<br />

suna sha'awar junansu. Rahama ita ce so da jin-kai da mutunta juna da ke<br />

wanzuwa bayan da ma'aurata suka tsufa. Duk da cewa ma'auratan na iya samun<br />

aiwatar da abubuwan biyu lokaci guda a tsawon rayuwar aurensu.<br />

A yanzu, ina son zan yi bayanin hakkokin ma'aurata. Muna da hakkoki iri biyu,<br />

akwai hakkoki na mu'amala ta fuskar kasuwanci, wanda ake zaunawa a tsara<br />

ka'idoji wanda idan aka sami wata matsala ana iya zuwa kotu domin a waware<br />

matsalar, wanda yake da gaskiya a bashi wanda kuma yayi rashin-gaskiya ko cinamana<br />

a hukunta shi. Akwai kumda hakkoki a tsakanin iyaye da 'ya'yan su, miji a<br />

kan matar shi, mata a kan mijin ta, sa'annan hakkokin 'yan-uwa. Wadannan duka<br />

basu cika sai idan akwai soyayya, kauna, biyayya, tausayi da sanin-ya-kamata. A<br />

duk fadin duniya babu wani tsarin doka ko wani ma'auni da zai tantance mizanin<br />

da zai gwada yadda wani zai nuna soyayyarsa da kauna da sanin-ya kamatar sa.<br />

A mutum na iya yin wadannan abubuwa da aka zayyana a baya ta hanyar tsoron<br />

Allah da ranar karshe. Wannan ne ya sanya mason tsira Muhammad (sallallahu<br />

alaihi wa sallam) yake huduba yana cewa "ku ji tsoron Allah".<br />

Ku ji tsoron Allah a dukkkan al'amuran ku, wannan ita ma tunatarwa ce , tunda<br />

wadansu ayoyin Al'qur'ani mai girma suna fassara wasu ne. manzon Allah SAW<br />

yana kasanecewa yana bayanin aya ta farko a cikin Suratun- nisa'I:<br />

ﺎ�ﻬﺟوز ﺎﻬﻨﻣ ﻖﻠﺧ و ةﺪﺣاو ﺲﻔﻧ ﻦﻣ ﻢﻜﻘﻠﺧ يﺬﻟا ﻢﻜﺑر اﻮﻘﺘﻟا سﺎﻨﻟا ﺎﻬﻳأ ﺎﻳ<br />

نإ مﺎ�ﺣرﻷاو<br />

ﻪ�ﺑ نﻮﻟءﺎ�ﺴﺗ يﺬﻟا ﷲا اﻮﻘﺘﻟا و ءﺎﺴﻧ و اﺮﻴﺜآ <strong>ﻻ</strong>ﺎﺟر ﺎﻤﻬﻨﻣ ﺚﺑ و<br />

Ma'ana:<br />

�<br />

�<br />

ﺎﺒﻴﻗر <strong>ﻢﻜﻴﻠﻋ</strong> نﺎآ ﷲا<br />

Ya ku mutane ku bi uban-gijin ku da takawa, (wannan) da ya halitta ku daga rai<br />

guda (daya), kuma ya halicci matarsa (shi rayin) daga gare shi, kuma ya halicci<br />

maza da mata masu yawa daga gare su. Ku ji tsoron Allah SWT wanda kuke<br />

rokon juna da sunansa (ku kuma ji tsoron Allah cikin hakkin) zumunta<br />

tsakaninku). Allah SWT ya kasance Mai tsaro ne a kanku.


Me ya sa zamu ji tsoron Allah? Amsar wannan tambaya ita ce : shine ya halicce<br />

mu kuma rayuwar mu duka a hannun shi take. Allah ya fada a cikin Suratul-Insan<br />

aya ta 1 cewa :<br />

�<br />

ارﻮآﺬﻣ ﺎﺌﻴﺷ ﻦﻜﻳ ﻢﻟ ﺮهﺪﻟا ﻦﻣ ﻦﻴﺣ<br />

نﺎﺴﻧﻹا ﻰﻠﻋ ﻰﺗأ ﻞه<br />

Ma'ana :<br />

«Lallai ne wani tsawon lokaci ya kasancewa dan Adam (wadda a cikin<br />

shi) bai kasance wani abin ambato ba»<br />

Idan ya kasance mutum shekararsa ashirin da haihuwa, waye zai san shi shekara<br />

ashirin da biyar da suka wuce. Hatta iyayensa ma basu san shi ba, Allah SWT<br />

shine ya halicce shi.<br />

Allah SWT ba mahalicci ne ba kadai, duk wani abu da muka ci da kuma wanda<br />

muka samu shi ne ya bamu, anan duk wata biyyaya da girmamawa ga Allah ta ke<br />

SWT, ba shi da abokin tarayya .<br />

Da Allah ya ga dama, da ya halicce mu ta hanyoyi dabam-daban, amma sai ya<br />

halicce mu ta hanyar mutum daya (Adam) domin ya nuna mana ya kuma tunatar<br />

da mu cewa mu fa al'uma daya ne, a nan wadanda su ka kasance a wannan<br />

faffadar al'ummar ya kasance dole su nunawa junan su soyayya da kauna da<br />

mutunta juna. Anan musulunci yana koya mana 'yan uwantaka. Babu wani addini<br />

da ya nuna 'yan uwantaka da juna kamar addinin musulunci.<br />

A nan za mu yi bayanin matsayin ma'aurata da hakkokin da ke rataye a kan su ta<br />

hanyar Al-Kur'ani mai girma da hadisan Annabin rahma, Muhammad (sallallahu<br />

alaihi wa sallam).<br />

Allah SWT ya ce a cikin suratun-Nisa'I aya ta 34:<br />

�....<br />

Ma'ana : «Maza sune shuwagabanni akan mata»<br />

�<br />

ءﺎﺴﻨﻟا ﻰﻠﻋ نﻮﻣاﻮﻗ لﺎﺟﺮﻟا �<br />

Wannan ayar wani lokaci ana yi mata rashin fahimta saboda ana mantawa da<br />

wasu ayoyin da suka yi bayani akan aure. Misali anan ba a ce ba maza su zama<br />

masu tsauri, saboda an basu iko akan matan su, Allah SWT cewa yayi<br />

«ku zauna da su (matan ku) a cikin kyautatawa».<br />

Dole mu zauna da matan mu cikin kyautatawa da mutuntawa. Allah SWT ya fada<br />

a cikin Suratul Baqara aya ta 233 cewa:<br />

�روﺎﺸﺗو<br />

ﺎﻤﻬﻨﻣ ضاﺮﺗ ﻦﻋ�<br />

«… a kan yardatayya daga garesu da shawartar juna", kaga ke nan Allah<br />

yana umartarmu da tuntubar matanmu a harkokin gida da zamantakewar iyali.


Shawarwari a musulunci suna da matukar muhimmanci, don haka wajibi ne mu yi<br />

amfani da ita a sha'anin iyalin mu. Babu bambancin hakkoki a takanin na-miji da<br />

mace. Allah SWT ya fada a cikin a cikin suratul Baqara aya ta 228<br />

�ﻦﻬﻴﻠﻋ<br />

يﺬﻟا ﻞﺜﻣ ﻦﻬﻟ و�<br />

«(Mata) suna da hakki a kan ku irin wanda kuma kuke da shi akan su»<br />

Kowa yana da matsayinsa, na-miji shi ya kamata yayi ayyuka irin na maza, haka<br />

nan mace ita ya fi cancanta ta yi ayyuka irin na mace. Yaya ko za a ce wanda ya<br />

halicce mu bai san wadannan hakkoki ba, alhali kuwa shi ne ya shimfida su?<br />

Don haka muna ganin na-miji shi ne shugaba ga matarsa, kuma shi ne mai<br />

jibintar al'amuranta, amma ya rika yin shawara da ita kuma ya rika mutunta ta a<br />

ko da yaushe. Na miji na iya fadawa rikici in ya yi gurgun hukunci, domin abin na<br />

iya komowa kansa. Don haka za a kama shi da laifi a nan duniya da kuma ranar<br />

gobe kiyama.<br />

Na yi gargadi da jawo hankali ga mazaje, a yanzu kuma zamu ga mataye.<br />

Wacece mace ta gari? Allah SWT ya fada a suratun Nisa'I aya ta 34 cewa:<br />

�...<br />

ﷲا ﻆﻔﺣ ﺎﻤﺑ ﺐﻴﻐﻠﻟ تﺎﻈﻓﺎﺣ تﺎﺘﻧﺎﻗ تﺎﺤﻟﺎﺼﻟﺎﻓ�<br />

Ma'ana; Mata na-gari masu da'a ne (ga Allah da kuma mazajensu), masu tsare<br />

kan su ne a lokacin da mijin su baya nan (kuma suna tsare masu dukiyoyin su).<br />

A nan dukiya ana nufin kaddarorinsa da kuma 'ya'yansa. A nan tarbiyyar 'ya'ya<br />

tana da matukar muhimmaci kuma wanda yake da wahala. Allah yace zai<br />

taimakawa dukkan macen da ta sauke wannan nauyi matukar tayi kokari. Annabi<br />

Muhammad (sallallahu alaihi wa sallam) yayi bayani wannan aya cewa " mace tagari<br />

ita ce wacce idan mijin ta ya gan ta za ta faranta masa rai, idan ya yi mata<br />

umarnin sai ta yi masa biyayya idan kuma baya nana sai ta kare kanta da kuma<br />

dukiyoyinsa".<br />

Sha'anin rayuwa ba ya yiyuwa sai an sami gargada. To idan ya kasance an sami<br />

sabani (tsakanin mata da miji) sai Allah SWT ya ce :<br />

�ىﻮﻘﺘﻠﻟ<br />

بﺮﻗأ اﻮﻔﻌﺗ نأ و�<br />

Ma'ana : ><br />

Idan ka yafe ai ba asara kayi ba, sai ka ci nasara, saboda haka kada ku kasance<br />

masu wulakanci ga junan ku, kada ku kasance masu zargin juna, Annabi<br />

Muhammad (sallallahu alaihi wa sallam) ya fadawa sahabbansa cewa: "Kada ku<br />

zagi iyayen ku" sahabbai suka ce ta yaya zamu zagi iyayen mu ? sai manzon<br />

Allah (sallallahu alaihi wa sallam) yace idan ka zagi iyayen wani shima sai ya zagi<br />

naka.


Saboda gudun irin wannan fito-na-fito Al-Qur'ani mai girma ya nuna mana cewa<br />

mu yafe kuma kada mu manta da kyautatawa da kuma godewa juna. Allah SWT<br />

yace :<br />

�ﻢﻜﻨﻴﺑ<br />

ﻞﻀﻔﻟا اوﻮﺴﻨﺗ<strong>ﻻ</strong>و�<br />

Ma'ana :<br />

Kada ku manta da falala a tsakanin ku>><br />

Allah SWT ya wasafta mutunta juna tsakanin ma'aurata a cikin Suratul Baqarah<br />

ayah ta 187:<br />

�ﻦﻬﻟ<br />

سﺎﺒﻟ ﻢﺘﻧأو ﻢﻜﻟ سﺎﺒﻟ ﻦه�<br />

Ma'ana: "Su (matanku) tufafi ne a gare ku, kuma tufafi ne a gare su". Allah ya yi<br />

amfani da wani misali mai kyau don bayanin wannan dangantaka.<br />

To a nan zan tambaye ku.. meye amfanin tufafi ? yana kare mu daga zafin rana,<br />

sanyi, kura, da dai sauran su, a nan ma'aurata kariya ne ga junan su kuma<br />

garkuwa ne ga juna. Tufafi suna kare mana illa daga muhimman wurare a jikin<br />

mu, haka nan ma'aurata za su kare illoli da matsalolin juna ba wai kawai a tafi a<br />

fallasa wajen 'yan uwa da abokai ga matsalar abokin zama ba.<br />

Tufafi suna karawa mutum kyau da kawa ta jan hankali, haka nan ma ma'aurata<br />

ke karawa junan su kyau da kawa, su yi ado wanda ya amsa sunansa domin<br />

juna, amma ba a yi ado saboda zuwa wajen biki ko suna ba. Misali ba a son maza<br />

su yi shiga ta banza maras ma'ana a gidan su, haka nan kuma mata. Ana so<br />

kuma halayen kowa daga cikinsu su zama tamkar madubi ne na halayen<br />

danuwansa. Misali idan mace bata da halayya ta gari to fa tana gwada irin<br />

halayyar mijinta ne, haka nan kuma shi ma mijin.<br />

Abu na kusa da na karshe, su tufafi sune kusa da jiki fiye da komai, haka nan<br />

ma'aurata suna kusa da junan su fiye da kowa, sun san sirrin junan su. Don<br />

haka lallai su kare sirrin junan su, ba daidai bane mace ta kasance<br />

kusancinta da 'yan uwanta ya fi kusancinta da mijinta, ko kuma miji ya<br />

kasance kusancinsa da 'yan uwansa ya fi kusancinsa ta matarsa. Babu<br />

wata kalma a wani littafi a duk duniya banda Al-Qur'ani mai girma wanda yayi<br />

kammalallen bayani akan hakkokin ma'aurata kamar wannan ayar :<br />

Ma'ana :<br />

" Su (matan ku) tufafi ne a gare ku, kuma tufafi ne a gare su"<br />

�ﻦﻬﻟ<br />

سﺎﺒﻟ ﻢﺘﻧأ و ﻢﻜﻟ سﺎﺒﻟ ﻦه�


Ina addu'a ga Allah SWT ya shiryar damu mu gane mu yi amfani da abinda muka<br />

ji a rayuwar mu, ina yiwa ango da amarya fatan Alheri, kuma ina taya su murna<br />

da iyayen su da 'yan uwan su da abokan su.


Allah SWT ya ce a Suratul Hashri :<br />

GAISUWA A MUSULUNCI<br />

ﺰ�ﻳﺰﻌﻟا ﻦﻤﻴ�ﻬﻤﻟا ﻦﻣﺆ�ﻤﻟا مﻼ�ﺴﻟا سوﺪ�ﻘﻟا ﻚ�ﻠﻤﻟا ﻮ�ه <strong>ﻻ</strong>إ ﻪ�ﻟإ ﻵ يﺬ�ﻟا ﷲا ﻮه<br />

�نﻮآﺮﺸﻳ<br />

ﺎﻤﻋ ﷲا نﺎﺤﺒﺳ ﺮﺒﻜﺘﻤﻟا<br />

�<br />

رﺎﺒﺠﻟا<br />

Ma'ana :<br />

><br />

A wannan ayar, kalmar 'As-Salam' tana daya daga cikin sunayen Allah<br />

madaukaka (Asma'ullahil Husna), za mu yi kokari mu fahimci ma'anarta, dalilai<br />

da kuma amfanin kalmar salam.<br />

Kafin bayyanar musulunci, larabawa sun kasance suna gaishe da junan su da<br />

kalmar "Allah ya barka" sai musulunci ya kawo sabuwar gaisuwa: Assalamu<br />

Alaikum" , ma'ana: ina fata ka kasance cikin tsari daga dukkan wani bakin-ciki<br />

kon kunci, wahalhalu da kuma tsiya. Ibnul Arabi yace (Ahkamul Qur'an) "ita<br />

kalmar as salam tana daya daga siffofin Allah kuma tana nufin Allah shine mai<br />

tsaron ka .<br />

Wannan gaisuwa ta musulunci ta fin irin gaisuwar soyayya wadda wadansu<br />

kasashe ke amfani da ita saboda wadannan dalilai:-<br />

1) Ba wai kawai an ambaci soyayya bane kadai,a'a, an bayyana manufar<br />

soyayyar ne a yanayin addu'a, ana fatan ka tsaru daga bakin-ciki, wannan<br />

addu'ar bata rayuwar ba ce kadai kamar yadda larabawa ke fadi, a'a rayuwar<br />

wadata wadda take ita ce mafificiya.<br />

2) Kuma tana tunatar da mu cewa mu dogara ga Allah SWT babu wanda zai cutar<br />

da mu ko ya amfanar da mu sai Allah ya yarda. Haka nan wata irin ibada wadda<br />

take tunatar da musulmi Allah.<br />

3) Ka sani idan wani yayi maka addu'ar ka kasance cikin salama, yana<br />

tabbatarwa da yin alkawalin cewa ka tsira daga hannun shi da kuma harshen shi,<br />

kuma zai mutunta ka da daratta ka da mutunta ka.<br />

A cikin littafin Ahkamul qur'an, Ibnul Arabi ya ce " ka san ko menene 'salam'? mai<br />

maganar ya na sanarwar cewa ka tsira kwata-kwata daga duk wata cutarwa daga<br />

gare ni.<br />

A takaice, 'Salam' ita ce :-<br />

i) Tunawa da Allah.<br />

ii) Tunatarwa<br />

iii) bayyana soyayya a tsakanin musulmi<br />

iv) addu'a madaukakiya.


v) hakikan da sanarwar cewa ka tsira daga hannaye na da kuma harshe na.<br />

Hadisi yayi bayani gaba-daya:-<br />

"Musulmi na gari shine wanda baya cutar da wani musulmi da hannun shi ko da<br />

harshen shi".<br />

Idan muka fahimci wannan Hadisin kadai ya isa ya shiryar da al'ummar musulm.<br />

Shi ne ya sa Annabi Muhammadu (sallallahu alaihi wa sallam) yake jaddada<br />

muhimmancin yin sallama a tsakanin kuma ya kuma kira ta mafificiya a cikin<br />

ayyuka na gari da kuke yi.<br />

A karbo Hadisi daga Abu hurairah RA ya ce : Manzon Allah (sallallahu alaihi wa<br />

sallam) ya ce " Ba za ku shiga aljanna ba sai kun zamo muminai, ba kuma za ku<br />

zamo muminai ba har sai kun so junan ku, bari in fada maku wani abu wanda<br />

idan ku ka yi shi zai kara soyayya a tsakanin ku: ku yawaita yin sallama ga<br />

mutumin da ka sani da ma wanda ba ka sanin ba."<br />

Abdullahi bn Umar ya ce: wani mutum ya tambayi Manzon Allah (sallallahu alaihi<br />

wa sallam) wadanne ayyuka ne su ka fi a musulunci? Sai Manzon Allah (sallallahu<br />

alaihi wa sallam) ya ba amsa mashi da cewa : Ka ciyar da mutane abinci sannan<br />

ka yi sallama ga wanda ka sani da wanda ba ka sani ba."<br />

Abdullahi bn Mas'ud ya ce: Manzon Allah (sallallahu alaihi wa sallam) ya ce "<br />

Kalmar 'Salam' tana daya daga cikin sunayen Allah wanda ya saukar a duniya son<br />

haka mu yawaita yin sallama". Idan wani ya yiwa wani sallama darajar shi ta<br />

karu a wurin Allah, idan a taron jama'a babu wanda ya amsa mashi sallama, to<br />

wata halitta wadda ta fi su (wato mala'iku) za ta amsa mashi sallamar.<br />

Abu hurairah ya ce : Babban marowaci shine wanda yake yin rowa wajen yin<br />

sallama.<br />

A cikin Alqur'ani mai girma, suraun Nisa'I aya ta 86, Allah SWT ya ce :<br />

><br />

Ma'ana :<br />

><br />

A nan Allah SWT yace ku amsa sallama kamar yadda aka yi ko kuma da wasu<br />

kalmomi wadanda suka fi wannan. Manzon Allah (sallallahu alaihi wa sallam) ya<br />

nuna wannan kamar yadda ya zo a ibnu Jareer da Ibn abi Haatim cewa: wata<br />

rana Annabi (sallallahu alaihi wa sallam) yana zaune tare da sahabban shi sai<br />

wani mutum ya zo ya ce "Assalamu alaikum" sai Manzon Allah (sallallahu alaihi<br />

wa sallam) ya amsa mashi kamar haka : wa alaikumus salaam wa rahmatullahi",<br />

sai wani mutum na biyu ya zo ya ce " Assalmu alaikum wa rahmatullah" sai<br />

Manzon Allah (sallallahu alaihi wa sallam) ya amsa mashi kamar haka : wa


alaikumus salaam wa rahmatullahi wa barakatuhu", nan take sai wani mutum na<br />

uku ya zo ya ce : Assalamu alaikum wa rahmatullah wa barakatuh" sai Mnzon<br />

Allah (sallallahu alaihi wa sallam) ya amsa ma shi da cewa : "wa alaika". Mutumin<br />

na uku ya ce ya Manzon Allah da suka gaishe ka a takaiace ka amsa masu da<br />

kalmomi wadanda suka fi, ni kuma na gaishe ka da cikakkiyar gaisuwa na yi<br />

mamaki da ka amsa mani da takaitacciya ka ce ' wa alaika'! Manzon Allah<br />

(sallallahu alaihi wa sallam) ya amsa cewar : baka bar wani wuri da za a yi kari<br />

ba. Wannan ne ya say a maida maka sallama domin in cika ka'idar da Allah ya<br />

tsara a Alqur'ani.<br />

A takaice anan mayar da sallama a cikin matakan nan guda uku sunnah ce ko<br />

kuma muce hanya ce ta Annabi Muhammadu (sallallahu alaihi wa sallam). An<br />

kayyade yin sallama a wannan matakai guda uku domin ta zama takaitaccen sako<br />

bai I don bayani ba.<br />

A wannan aya Allah SWT yayi amfani da karkarfan karshe ba tare da bayyana<br />

maudhu'I ba.<br />

A nan Alqur'ani mai girma ya koya mana yadda ake amsa sallama, a fakaice yana<br />

umurtar mu da mu yi sallama ga junan mu, wannan yana nuna mana ya zamana<br />

halayya da al'adar mu, kuma yau da kullum muminai su rika gaishe da juna da<br />

sallama, kamar yadda aka ambata a baya wanda ya fara yin sallama shine wanda<br />

yake kusa da Allah SWT. Hassan Albsri ya ce yin sallama ba wajibi bane amma<br />

amsa ta wajibi ne.<br />

Ya zo a cikin Almuwatta na Al imam Malik wanda aka samo daga Tufail bin Ubayy<br />

bin Ka'b cewa Abdullah bn Umar ya kasance yana zuwa kasuwa domin yayi<br />

sallama ga mutane ba don ya sayo ko ya sayar da komai ba, domin ya fahimci<br />

amfanin fara yin sallama.<br />

A karshe, aya ta 86 a cikin suratun Nisa'I, Allah SWT ya ce " Allah ya na lissafe da<br />

komai"<br />

A nan kuma, fara yi da kuma amsa sallama duk an shigo da su do haka mu so<br />

mu fara yin sallama kuma mu amsa sallama domin mu kyautatawa Allah SWT<br />

kuma mu sanya soyayya a tsakanin mu.<br />

Manzon Allah (sallallahu alaihi wa sallam) ya fadakar da cewa;-<br />

- wanda yake akan abin hawa ya yiwa wanda yake a kasa sallama.<br />

- wanda yake tafiya ya yiwa wanda yake zaune.<br />

- mutane kadan su yiwa mutane wadanda suke da yawa sallama.<br />

- wanda zai tafi ya yiwa wanda su ke tsaye sallama.<br />

- idan za ka bar gida ko shiga gida ka yi sallama ko da babu kowa, domin<br />

mala'iku za su amsa.<br />

-idan kuna yawan haduwa ku yawaita yin sallama.


HALIN DA BA A AMSA SALLAMA<br />

- a lokacin da ka ke yin sallah, idan har ka amsa sallama to sallar ka ta abaci.<br />

- mai huduba, mutumin da ke karatun Alqur'ani, ko kiran sallah ko tada iqama,<br />

ko koyar da littafan musulunci.<br />

- ko kana zaune a dakin wanka.<br />

Allah SWT yayi bayanin falalar yin sallama a suratul An'aam aya ta 54.<br />

A nan Allah yana ilmantar da Annabi Muhammad (sallallahu alaihi wa sallam) a<br />

kan muhimmancin wadanda suke talakawa wadanda suke a koda yaushe tare da<br />

shi, koda yake masu arzikin daga cikin wadanda ba suyi imani ba sun so Manzon<br />

Allah ya kori wadannan matalauta domin masu arziki su kasance taer da shi.<br />

Allah SWT ya umarci Annabi (sallallahu alaihi wa sallam) yayi wa wadannan<br />

talakawa muminai Magana ya ce 'Assalamu alaikum'da zaran sun zo, wannan<br />

kuma tana nufin abu biyu: na farko ya isar da gaisuwar Allah a gare su, kuma<br />

wani abu na girmamawa da mutuntawa ga mutanen da suke talakawa kuma<br />

musulmai na gari, wannan zai kara karfafa zuciyar su da imanin su. Abu na biyu<br />

zai isar masu da labari mai dadi cewa da ikon Allah za su kasance cikin jin dadi,<br />

salama da kuma aminci ko da kuwa sun aikata wasu kusakura.<br />

Ya Allah SWT ka bamu ikon yin gaisuwa cikin tafarki na musulunci a halin<br />

rayuwar mu, wajen yin wannan ka sanya soyayya da hadin kai a tsakanin mu,<br />

Ameen.


TAQAWA<br />

Allah SWT ya ce a cikin suratu Aal Imran, aya ta 133:<br />

><br />

Ma'ana :<br />

><br />

a gaba sai Allah ya yayi bayani akan wadanda su ke a imani na gaskiya, sai yace<br />

:<br />

><br />

Ma'ana :<br />

>.<br />

Bari mu fahmci menene Taqwa.. Taqwa tana da matakai guda uku : idan mutum<br />

ya tsare kan shi daga kafirci da kuma hada Allah da wani a wurin bauta, wannan<br />

shine musulmin na gari, a nan duk wanda yayi imani mumini ne koda kuwa yana<br />

aikata zunubi. Wanda duk ya nisanta kanshi daga abinda Allah SWT da Manzon<br />

shi (sallallahu alaihi wa sallam) su ka yi hani, to wannan yana da kololuwar<br />

Taqawa. A karshe, idan mutum yana son Allah ya so shi a ko yaushe, wannan ma<br />

ya na da kololuwar Taqawa. Allah yayi bayani a cikin suratu Aal Imran, aya ta<br />

102 cewa:<br />

><br />

Ma'ana :<br />

><br />

Allah SWT ya yi bayanin alamomin musulmi na gari: sune su ke ciyarwa ta<br />

hanyar Allah, a misali idan suna da Naira dubu suna iya bayar da mafi kankanta<br />

(Naira daya), ciyarwa ta hanyar Allah shine tsarin rayuwar su,<br />

Allah zai cire su daga kangi saboda wannan kyaukyawan aiki. Har-ila-yau, mutum<br />

wanda ya ke son taimakon jama'a ba zai handame dukiyaer mutane ba, ya fi son<br />

ya yi wa mutane abu mai kyau. A'isha RA ta taba bayar da kwayar dabino daya<br />

sadaka tun da bara da komai.wasu mutanen kirki suna bada albasa daya sadaka.<br />

Annbi Muhammad (sallallahu alaihi wa sallam) ya ce " ka kare kanka daga wuta


koda kwaya daya ne, kada ka bar mabukaci ya tafi hannhn shi haka nan.. ka<br />

bashi ko da takon akuya ne idan shin kadai ya rage.<br />

An yi bayani a cikin At-tafseer Al-Kabeer na Al imam Ar raazi cewa wata rana<br />

Annabi Muhammadu (sallallahu alaihi wa sallam) yayi kira mutane su bada<br />

sadaka, sai wadan su suka kawo zinare da azurfa, wani ya kawo sanhon dabino<br />

ya ce bani da sauran wani abu , wani mutum ya ce wa Annabi (sallallahu alaihi<br />

wa sallam) ba ni da abin da zan bada sadaka! Yace na bada sadaka da imani na,<br />

idan har wani ya ci mani mutunci ko ya ba ta mani rai tko ba znn yi hushi ba". A<br />

nan mun gain ko da talakawa suna ciyarwa da dan abinda ke garesu son su<br />

taimakawa wasu a lokacin Annabi (sallallahu alaihi wa sallam).<br />

A wannan ayar ba a kayyade ciyarwa ba. Yin abu domin Allah ba ana nufin kadai<br />

yin amfani da dukiya ba, har ma da lokacin ka da basirar da Allah ya baka. Akwai<br />

wata hikima da aka ce muminai suna ciyarwa a huce (a lokacin da suke a<br />

yalwace), saboda yawancin mutane suna mantawa da Allah a lokacin da suke a<br />

cikin yalwa. Sun mance da Allah saboda suna damuwa da abubuwan da suka<br />

sanya a gaba.<br />

Wani baitin waka da aka yi da yaren 'Urdu' yana cewa:<br />

' Kada ka dauki mutum mai ilmi ne wanda yake mantawa da Allah idan yana cikin<br />

samu, baya jin tsoron Allah idan ran shi ya ba ci'.<br />

Allah SWT ya ce alama ta biyu ta muminai na gari ita ce suna kamewa daga bacin<br />

ran su. Na uku ba wai kawai suna kamewa daga bacin-ran su ba, har-wa-yau su<br />

na yafewa wanda ya bata masu rai har cikin zuciyar su, kuma suna kyautatawa<br />

mutane 'yan uwan su. A wajen bayanin wannan ayar Al Imam Al baihaqi RA ya<br />

kawo wani al'amari da ya afku cewa : wani lokaci Ali bn Ahussain RTA yana yin<br />

alwala wani bawan shi ya na zubo mashi ruwa a hannun shi da wani mazubi,<br />

wannan mazubin ruwa sai ya kubuce daga hannun bawan nan ya fada a kan Ali<br />

sai bawan ya fahinci ran shi ya baci a fuskar Ali, bawan nan yana da wayo sai ya<br />

rika karanta ayar nan a hankali- a- hankali ya karanta cewa muminai na gari<br />

sune masu boye hushin su, sai Ali ya hadiye bacin ran shi, da bawan ya karanta<br />

cewa sune masu yafewa idan an yi masu laifi sai Ali ya ce na yafe maka, da ya<br />

karanta cewa Allah ya na son maso kyautatawa sai Ali ya ce na 'yanta ka!.<br />

Yafewa wanda yayi maka wani laifi yana da sakamako babba a ranar tashin<br />

kiyama. Annabi (sallallahu alaihi wa sallam) ya ce Allah SWT zai yi kira ranar<br />

tashin kiyama : wanda duk ke da wani a warin Allah ya tashi tsaye, a wannan<br />

babu wanda zai mike sai masu yafewa wanda suka cuce su ko azabtar da su.<br />

Annabi Muhammad (sallallahu alaihi wa sallam) ya sake cewa " wanda duk ke son<br />

wata katafariyar fada a aljannar firdausi to yayi wadannan abubuwa:-


- Ya yafewa wanda ya azabtar da shi.<br />

- Yayi kyauta ga wanda bai taba baka komai ba.<br />

- Kada ya guji wanda da niyya ya yanke hulda da su.<br />

Ba wai ba ya cikin tsari a tunatar da musulmi su rika musayar kyauta a tsakanin<br />

su ba, ya kamata wannan ya kasance hali ne a gare su ba wai su takaice wata<br />

rana kamar yadda arna ke yi a bukin kirsimeti da wasu shagulgula ba.<br />

A nan Allah SWT yana nuna mana da kyau yadda za mu zauna da manyan<br />

makiyan mu- suratu Fussilat aya ta 34.<br />

><br />

Ma'ana :<br />

>.<br />

Wata rana wani mutum ya ci zarafin Abu Hanifa RA, sai Abu Hanifa bai ce da shi<br />

komai ba, sai ya je gida ya tattaro kyaututtuka ya baiwa wannan mutum ya gode<br />

mashi yadda ya yi mashi ya ce " kayi mani alfarma da ka dauki ayyukan ka masu<br />

kyau ka sanya cikin nawa sakamakon ta yadda ka ci mani fuska"<br />

Allah SWT har-wa-yau ya ce , suratu Al Imraan aya ra 135-136 ya kara bada<br />

haske a yadda muminai su ke :<br />

><br />

Ma'ana :<br />

>.<br />

Ka sani da cewa :<br />

Gafara Allah SWT ta zarce shiga aljanna a wannan ayar, yana a fili karara shiga<br />

aljanna yana cikin gafara da rahmar Allah SWT. Bai takaita ba a kan ayyukan mu<br />

na sha'awa, ka sani matsayin aljanna ya fi duniya da sammai idan aka hada baki<br />

daya. Kuma wata ma'anar wannan ayar shine girman aljanna ya fi sammai da<br />

ﷲا


kassai da duk abinda ke ciki. Muna iya mamakin aljanna yaya tsawonta yake tun<br />

a koda yaushe tsawao ya fi fadi. A karshe, wannan ayar tana nufin cewa aljanna<br />

an tanade ta ne saboda muminai na gari, kamar yadda wasu sannannun<br />

malaman musulunci suka fada cewa aljanna tana gaba da saman bakwai rayukan<br />

wadanda suka yi shahada tuni suna cikin dausayin aljanna.<br />

Allah SWT muna rokon ka ka bamu matsayi irin na muminai na gari, Ameen.


MUNAFUKAI<br />

A farkon Al qurni mai girma, Allah SWT ya rarraba wannan al'umma zuwa kashi<br />

uku, akwai mumunai, akwai kafirai, sa'annan akwai munafukai. Allah SWT yayi<br />

bayani takaitacce a kan mumunai, kafirai kuma yayi baynin su a aya daya,<br />

sa'annan yayi bayani mai tsawo akan munafukai saboda sune suka fi kowa hadari<br />

a cikin al'umma. Ya dace mu fahimci halayen su da kuma makomar su.<br />

Ya kamata a san cewa wannan karkasawa da aka yi wa al'uma an yi ta ne bisa<br />

gwargwadon imanin mutane da kuma aikin su ba tare da lura da launi su ba, ko<br />

kuma inda suka fito, ko yaren su, kasar su ko kuma yankin da suka fito ba.<br />

Bari mu dubi halayyar munafukai kamar yadda aka siffanta su a aya ta 8 da ta 9<br />

a cikin suratul Baqarah :<br />

><br />

Ma'ana :<br />

><br />

ka sani cewa duk da suna ikirarin sun yi imani da Allah da ranar lahira, to amma<br />

babu maganar imani da annabcin Annabi Muhammad (sallallahu alaihi wa<br />

sallam). Wannan shine aikin yahudawa a wancan lokaci. Don haka, duk wani<br />

imani ba tare da imani da manzancin Annabi Muhammad (sallallahu alaihi wa<br />

sallam) ba to ba karbabbe ne ba. Sun yi hasara, kuma ba su san aibnda suke yi<br />

ba.<br />

><br />

Ma'ana :<br />

><br />

A nan, karya ba karamin zunubi ce ba, tana iya maida mumini ya koma munafiki.<br />

Allah SWT ya bayyan karya tare da bautar gumaka a Alqur'ani mai girma:<br />

><br />

Ma'ana :<br />

<br />

Allah SWT yayi bayanin ababe guda uku da ke nuna munafukai; Baqarah, aya ta<br />

11 da 12:


Ma'ana:<br />

><br />

Na biyu, Allah SWT ya ce a aya ta 13 a suratul Baqarah;<br />

><br />

Ma'ana :<br />

><br />

A nan a bayyane yake cewa, jarrabawar imani na gaskiya shine kayi imani kamar<br />

yadda sahabban Manzon Allah (sallallahu alaihi wa sallam) suka yi. Allah SWT<br />

yana girmama sahabban Manzon Allah (sallallahu alaihi wa sallam) shine ya tsara<br />

matakan da za a jarraba imani na gaskiya. Har-wa-yau, Allah SWT ya karrama<br />

sahabbai a farkon ayar inda ya ce " munafukai suna kokarin su yaudari Allah da<br />

wadanda suka yi imani (wato sahabbai)"<br />

Allah SWT yayi bayanin mataki na uku dake nuna munafukai kamar haka:<br />

Baqarah, aya 14,15,16:<br />

><br />

Ma'ana:<br />

نوءﺰﻬﺘ��ﺴﻣ<br />


Ma'ana :<br />

><br />

Akwai abubuwa da dama da ya kamata ayi bayanin su a nan, mun gani cewa<br />

maza da mata wadanda suka yi imani an dauke su a matsayin daya a ladar da<br />

za su samu saboda aikin su. Akwai haske a gaban su saboda an basu sakamakon<br />

su a hannun dama. Al'ada ne ka sami fitila a gaban wanda ya ke a halin tafiya,<br />

wannan haske dake gaban su ya sakamakon aiyukan su na gari.<br />

Akwai Hadisai da dama daga bakin Manzon Allah (sallallahu alaihi wa sallam)<br />

wadanda suka yi bayani akan hakan.<br />

An karbo daga Anas RTA ya ce Manzon Allah (sallallahu alaihi wa sallam) yayi<br />

albishir ga wanda suke zuwa masallaci cikin duhu cewa za su sami wani irin haske<br />

a ranar tashin kiyama. (Ibn Maajah ne ya ruwaito shi)<br />

An karbo daga Ibn Umar cewa Manzon Allah (sallallahu alaihi wa sallam) ya ce "<br />

wadanda suke yin sallah a akan lokacin ta a koda yaushe za su sami sakamakon<br />

wani irin haske na shiriya a ranar tashin alkiyama, wadanda ba sa aikata hakan<br />

ba za su wannan haske ba, za su kasance tare da Qaruna, da Hamana da<br />

Fir'auna. ( Ahmad ya ruwaito shi a cikin Al Musnad)<br />

An karbo daga Abu Sa'id cewa Manzon Allah (sallallahu alaihi wa sallam) ya ce "<br />

duk wanda ya karanta Suratul Kahfi a ranar Juma'a zai sami haske na shiriya a<br />

ranar tashin kiyama wanda zai tashin tun daga kafar sa har zuwa Aljanna". (At<br />

tabarani ne ya ruwaito shi)<br />

An karbo daga Abu Hurairah RA cewa Manzon Allah (sallallahu alaihi wa sallam)<br />

ya ce " duk wanda ya karanta aya daya ta Al qur'ani za ta kasance mashi haske<br />

na shiriya a ranar tashin alkiyama (Al imam Ahmad ne ya ruwaito shi)<br />

An karbo daga Abu Hurairah RA cewa Manzon Allah (sallallahu alaihi wa sallam)<br />

ya ce " duk wanda ya rokar mani aminci da salama zai sami haske a kan Siradi a<br />

ranar lahira"<br />

Haka nan ma duk wani aiki mai kyau zai zama haske ga muminai. Sabanin halin<br />

da muminai suke a ciki a ranar lahira, Allah ya bayyana halin da munafukai za su<br />

kasance a ciki. Allah SWT ya ce (suratul Hadeed, aya ta 13,14,15.<br />


ﺬ�ﺧﺆﻳ <strong>ﻻ</strong> مﻮﻴﻟﺎ�ﻓ روﺮ�ﻐﻟا ﷲﺎ�ﺑ ﻢآﺮ�ﻏ و ﷲاﺮ�ﻣأ ءﺂ�ﺟ ﻰ�ﺘﺣ ﻲﻧﺎ�ﻣﻷا ﻢﻜﺗﺮﻏو ﻢﺘﺒﺗراو<br />

ﺮﻴﺼﻤﻟا ﺲﺌﺑ و ﻢآ<strong>ﻻ</strong>ﻮﻣ ﻲه رﺎﻨﻟا ﻢآ ىوﺄﻣ اوﺮﻔآ ﻦﻳﺬﻟا ﻦﻣ <strong>ﻻ</strong> و ﺔﻳﺪﻓ ﻢﻜﻨﻣ >><br />

Ma'ana :<br />

A ranar tashin kiyama munfukai maza d mata za su cewa mumunai ku jira mu<br />

domin mu yi amfani da hasken ku, sai su ce da su ku koma ku samo haske. Za yi<br />

bango tsakanin muminai da munafukai, a cikin wannan bango rahma ce ta Allah,<br />

a bayan shi kuma azaba ce. Munafukaii za su cewa muminai (da karfi) " shin ba<br />

mu kasance tare da ku (a duniya) ba? Sai muminai su ce " kwarai da gaske! Sai<br />

dai ku kun fitini kawunan ku, kun yi shakku, kun gurace-guracen rayuwa sun<br />

rude ku har sai da lamarin Allah ya zo, kuma mai rudarwa ya rude ku. Don haka<br />

a yau ba za a karbi fansa daga gare ku ba, kuma ba za a karba daga wanda suka<br />

kafircewa Allah ba, makomar ku ita ce wuta, ita ta fi dacewa da ku, makoma ta<br />

munana.>><br />

Kamar yadda Ibn Katheer yace dukkan muminai da minafukai za a basu haske a<br />

ranar tashin kiyama idan zasu tsallake siradi. Hasken munafukai za a bushe shi. A<br />

cikin wannan hali zai masu ba'a ne kamar yadda suke yin ba'a da bayin da suke<br />

yi ma shi biyayya. Allah SWT yace (suratul Baqarah aya ta 15)<br />

><br />

Ma'ana :<br />

Allah yana yi masu ba'a zai bar su a cikin batan su a dimauce >><br />

Ka sani cewa munafukai an ba su haske ne domin sun taba yin aiki na gari don su<br />

yi riya (don a gani)<br />

Muna iya yanke cewa aiki na kwarai yana iya kaiwa a kasance da dawwamamen<br />

haske. Munafukai kuma za a yi masu izgili a ranar tashin kiyama. Ibn Katheer ya<br />

ruwaito wani Hadisi mai tsawo inda aka ce mumunai za su sami hasken dai dai da<br />

ayyukan su, wasu zasu sami haske kamar tsauni, wasu kamar tsawon iccen<br />

goriba, wasu kuma kamar hasken kamar tsawon mutum.<br />

Allah SWT ya ce a cikin suratul Hadeed aya ta 17<br />

><br />

Ma'ana :<br />

><br />

A nan Allah SWT yana tunatar da nu cewa zai raya kasa idan ta mutu kum zai<br />

raya zukatan munafukai idan sun yi tuba na gaskiya, ina rokon Allah ya sa mu<br />

zama musulmi na kwarai ya kuma ba mu haske na shiriya na dun-dun-dun a<br />

ranar tashin kiyama.


BARZAKHU<br />

Barzkhu wani lokaci ne tsakanin mutuwa a duniya da ranar da za a tayar da<br />

mutane a ranar tashin alkiyama. Ba mu san ba abinda ke faruwa a wannan lokaci<br />

sai dai za mu iya sani daga wadansu ayoyi na alqur'ani mai girma da Hadisan<br />

Manzon Allah (sallallahu alaihi wa sallam), misali Allah SWT ya ce a cikin suratul<br />

An'am aya ta 93:<br />

><br />

Ma'ana:<br />


Ma'ana :<br />

><br />

A nan ya nuna cewa mutanen fir'auna an jefa su cikin wuta yayin da aka nutsar<br />

da su a a cikin ruwa, wannan ya nuna cewa akwai azabtarwa tun daga lokacin<br />

mutuwa. Yana da ban-sha'awa ka fahimci cewa an ambaci azabar wuta tare da<br />

nutsarwa a cikin ruwa. Al imam Ar raazi y ace " wannan hujja ce mai karfi akan<br />

cewa akwai azabar barzkhu da kuma 'kabari" yayi nuni cewa kalmar "fa" a cikin<br />

wannan ayar anyi amfani da ita ne don nuna cewa azabar wutar ta faru ne da<br />

gaggawa bayan nutsewa a rowan, kuma wannan azabar ba ana nufin ita ce<br />

azabar ranar tashin alkiyama ba.<br />

Allah SWT ya ce a suratu Gaafir (aya ta 45-46) :<br />

><br />

Ma'ana :<br />

><br />

Wannan ayar tana nuna mana cewa akwai azaba a kabari ga wandanda suka<br />

kafirce da kuma azabar da zata same bayan an yanke hukunci ranar tashin<br />

alkiyama.<br />

Abdullah dan Mas'ud yayi bayanin wannan ayar cewa rayukan mutanen fir'auna<br />

za a kawo su kamar bakaken tsuntsaye safiya da marece zuwa wuta ana fada<br />

masu "wannan shine karshen makomar ku"<br />

Allah SWT ya ce a suratul Takathur (aya ta 1,2,3,4):<br />


A karshe, Allah SWT ya fada a cikin Alqur'ani mai girma cewa: Duk wanda ya<br />

manta dani to zan sanya rayuwar shi cikin kunci kuma zamu tashe shi a makaho<br />

a ranar tashin kiyama "<br />

Ibn Mas'ud RA da Abu Sa'id Al khudri RA sun ce ma'anar sanya rayuwar shi cikin<br />

kunci na nufin azabar kabari. Haka kuma Abu Hurairah RA yace: Annabi<br />

Muhammad (sallallahu alaihi wa sallam) ya ce "abinda ake nufi da wannan shine<br />

Allah SWT zai aiko macizai casa'in da tara (99) a kabarin wanda ya kafirce,<br />

macijin zai dingi sarin shi har zuwa ranar tashin kiyama.<br />

Me zai faru ga ran Dan Adam idan ya mutu?<br />

An karbo daga Abu Hurairah cewa Annabi Muhammad (sallallahu alaihi wa<br />

sallam) ya ce " idan ran mumini ya rabu da gangan jikin shi, Mala'iku buyu za su<br />

dauke shi zuwa sama, sai Mala'ikun nan su ce " ran mumini ya zo daga duniya<br />

sai su ce "Allah yayi ma gafara da jikin da ka yi amfani da shi", sai a gabatar da<br />

wannan ran ga Allah SWT sai Allah SWT ya ce " ku sanya wannan ran a Sidratul<br />

muntaha sai ranar tashin kiyama". Idan kuma aka zare ran kafiri daga gangan<br />

jikin shi, sai Mala'iku su ce " mummunan rai ya zo daga duniya, sai Mala'iku su<br />

rika tsine mashi, wurin da yake kuma sai ya dume da wari, Allah SWT sai ya bada<br />

umurni a ajiye wannan ran a Sijjeen, Sijjeen wani wuri ne inda za a ajiye ran<br />

kafirai.<br />

Annabin rahama, Muhammad (sallallahu alaihi wa sallam) ya sanya rigar shi ya<br />

rufe hancin shi ya na bayyana warin ran kafirai.<br />

Akwai Hadisai da dama da suka nuna yadda zaman kabari ya ke.<br />

An samo daga Anas RA ya ce : Annabi Muhammad (sallallahu alaihi wa sallam)<br />

yace "idan aka sanya mutum a kabari bayan mutuwar shi, idan 'yan uwan shi da<br />

abokan shi sun bar makabartar zai rinka jin karar tafiyar su da sauran jama'a.<br />

Mala'iku biyu za su zowa mutum a kabarin shi, Mala'ikun sai su tayar da shi<br />

zaune sai su tambaye shi wadanan tambayoyi :-<br />

Me ka sani game da Muhammad (sallallahu alaihi wa sallam) ? Mumini sai ya<br />

amsa : Na tabbata shi bawan Allah ne kuma manzon Allah ne. Sai Mala'kun su ce<br />

mashi da baka yarda ba da makomar ka wutar jahannama ce, duba ka gani Allah<br />

SWT ya canza ta da Aljanna, duba kuma ka gani. Har-wa-yau, Mala'iku za su<br />

tambayi munafukai da kafirai : me kuka sani game da Muhammadu (sallallahu<br />

alaihi wa sallam)? Sai su amsa : ni ban san komai ba ina fadar abinda mutane<br />

suke fadi. Sai Mala'iku suce masu baka taba gwada yin imani da shi ba ko bin<br />

wanda suka yi imani dashi. Sai Mala'ika ya buge shi da sandar karfe, zai yi kara<br />

mai tsanani wanda duk wani abu mai rai zai ji shi banda aljanu da mutane. (<br />

Bukhari da Muslim ne suka ruwaito shi)


Asma'u diyar Abubakar tace : wata rana Annabi Muhammad (sallallahu alaihi wa<br />

sallam) ya yi huduba ga mutane yayi bayanin yadda azbar kabari take, da fadin<br />

haka sai muminai suka yi ta kuka, wurin duk ya rude da kuka. (Bukhari ne ya<br />

ruwaito shi)<br />

Ibn Abbas RA yace Annabi Muhammad (sallallahu alaihi wa sallam) ya yi addu'a<br />

kamar ayar Alqur'ani mai girma yace " Ya Allah ina neman tsarin ka daga azabar<br />

wuta, da kuma azabar kabari da jarrabar rayuwa da jarrabar mutuwa, da<br />

jarrabar Dajjal". (Muslim ne ya ruwaito shi)<br />

Annabi Muhammad (sallallahu alaihi wa sallam) yace " karanta Suratul Mulk akai-a-kai<br />

zai tsare mutum daga azabar kabari.(Tirmizi ne ya ruwaito shi)<br />

Ina rokon Allah ya kare ni da mai karatu da mai sauraron wannan takaitaccen<br />

bayani daga azabar wuta, kabari da kuma Dajjal, Ameen.


TASHIN KIYAMA<br />

Yana da wuya kafiri ya amince cewa Allah SWT zai tayar da shi bayan mutuwar<br />

shi a ranar tashi alkiyama. Suratul Waqi'ah (aya ta 47da 48) ta yi bayani :<br />

><br />

Ma'ana :<br />


daya. Tun da Allah SWT zai iya halittar mutune mabanbanta da junan su, me zai<br />

hana iya tayar da matattu ya maida rayayyu?<br />

A cikin suratun Nazi'aat (aya ta 27-28) Allah SWT ya kara fayyace hakan a<br />

fili:<br />

><br />

><br />

Allah SWT ya na yi mana bayani cewa yana da wuya ayi ginin sama ba tare da<br />

wani matokari ba. Da za mu yi kokarin gano wani kuskure ko matsala a yadda<br />

aka halicci sama, ba za mu iya ganowa ba, idanuwan mu har sun gaji ba tare da<br />

mun gano wata matsala ko kuskure ba. To idan har Allah SWT zai halicci sama da<br />

irin wannan tsarin da muke gani a kowane lokaci, menene abin wuya idan zai<br />

tayar da mutum bayan ya mutu?<br />

Allah SWT ya ce a cikin Suratur Rum (aya ta 50)<br />

><br />

:<br />

Dubi yadda alamomin rahmar Allah su ke, yadda yake rayar da kasa bayan<br />

mutuwar ta. Lallai wanda yayi haka zai tayar da matacce, lallai shi mai iko ne a<br />

kan komai>><br />

Wannan lamari an fayyace shi a bayyane a suratu Fussilat (aya ta 39):<br />

><br />

><br />

Wannan wata muhimmiyar hujja ce ta yau da kullum wadda samari da tsofaffi da<br />

masu arziki da talakawa, masu ilmin da jahilai ke gani. Ruwa yana sauka da iznin<br />

Allah SWT, sai fako ya farfado a hankali ya samar da tsirrai da za su tashi akan<br />

wannan fako. Wannan mashahurin al'amari mai ban mamaki yana nan har ma a<br />

kewaye da gidajen mu mutane na duba kurum ba tare da suna dubar abinda ke<br />

faruwa ba. Waye yake farfado da kasar nan? Mun manta waye yake bubbugo<br />

tsirran nan har suke fitowa daga cikin fakon.


Duk wanda ya dubi wadannan ayoyi na Allah SWT da idon basira, ba zai sami<br />

wata shakka ba a cikin zuciyar shi akan cewa Allah SWT zai tayar da mu a ranar<br />

sakamako bayan mun mutu mun koma turbaya da kuma kasusuwa.<br />

Akwai wadan su abubuwa guda biyu masu ban sha'awa da suka faru da aka<br />

bayyana su a cikin Suratul Baqarah domin shiriyar mu. Da farko mu duba aya ta<br />

259:<br />

><br />


MA'ANA DA MANUFAR GASKIYA DA RIKION AMANA A MUSULUNCI<br />

Allah SWT ya ce a Surat An Nisa'i (aya ta 58)<br />

><br />


Masu masu tsare amana (da aka basu) da kuma alkawullan su. Sune masu<br />

tsayuwa a kan shaida ta gaskiya. Sune masu dawwama akan yin Sallolin su.<br />

Wadannan sune wadanda za a karrama su a gidan aljanna.>><br />

A nan, cika alkawali dayai yake da yin Sallah ingantacciya.<br />

Annabi Muhammad (sallallahu alaihi wa sallam) har-ila-yau yace<br />

ﺔﻧﺎﻣأ ﺲﻟﺎﺠﻤﻟا<br />

" Haduwar mutane a wani wurin zama amana ne a tsakanin su" don haka duk<br />

abinda aka fadi a wurin tarukan mutane baya kamata a fade shi ga wasu na waje.<br />

Har-wa-yau, Annabi (sallallahu alaihi wa sallam) ya ce " Duk wanda aka nemi<br />

shawarar shi kamar an bashi rikon Amana ne, don haka lallai ne ya bayar da<br />

shawara ta gari, kada yana kan sani ya bayar da mummunar shawara, yin haka<br />

cin amana ne. haka kuma idan wani ya sanar da kai wanin sirrin shi kada ka<br />

sanar da kowa ba tare da izinin shi ba.<br />

Bari mu duba mu ga yadda sahabban Manzon Allah (sallallahu alaihi wa sallam)<br />

suka dauki wannan al'amari. Ka rike a kan ka cewa sahabban Manzon Allah<br />

(sallallahu alaihi wa sallam) mutane ne kamar mu kuma su na iya yin kuskure<br />

kamar kowa. A cikin Suratul Anfal, aya ta 27 Allah ya yi bayanin wani lamari, inda<br />

ya ce:<br />

><br />


daga wannan sansani ? sai Abu Lubabah ya sa yatsar shi a wuyan shi yana nuni<br />

da cewa za a sare ma su kawuna ne. wannan wani sirri ne tsakanin Manzon Allah<br />

da Abu Lubabah. Bayan da Abu Lubabah ya fahimci ya tafka kuskure sai ya ji ba<br />

dadi, duk hankalin shi ya tashi, sai ya je ya daure kan shi a jikin wata itaciya.<br />

Yana a cikin wannan hali har kwana bakwai, ya ce ba zai kwance kan shi ba sai<br />

an karbi tubar shi haka nan ya zauna ba ci ba sha. Sa'adda Annabi Muhammad<br />

(sallallahu alaihi wa sallam) ya sami wannan labari sai ya ce " da dai ya zo kaitsaye<br />

gare ni in roka mashi gafara, amma yanzu ya bar lamarin shi ga Allah ya<br />

jira har sai Allah ya karbi tubar shi. Bayan kwana bakwai aka yi wa Annbi<br />

(sallallahu alaihi wa sallam) wahayin cewa an karbi tubar Abu lubabah. Wasu<br />

dangin shi suka rugo su kwance shi, Abu Lubabah yace ya gwammace ya tsaya<br />

har sai Annabi Muhammad (sallallahu alaihi wa sallam) ya kwance shi da hannun<br />

Shi mai albarka, don ya nuna kwata-kwata an karbi tubar shi.<br />

Wannan ya nuna mana cin-amana ba karamin al'amari bane a wajen sahabban<br />

Manzon Allah (sallallahu alaihi wa sallam), suna daukar wannan tsatstsauran<br />

mataki ne don su nuna jimamin su. A yanzu haka, akwai wani ginshiki a<br />

masallacin Madina ya mayi ainihin itaciyar da Abu Lubabah ya daure kan shi a<br />

jikin ta. Mutane da yawa suna zuwa kusa da wanna ginshiki suna rokon Allah ya<br />

yafe masu zunubban su kamar yadda Abu Lubabah yayi,\.<br />

Kuma muna iya ganin cewa : Lokacin da Annabi (sallallahu alaihi wa sallam) ya<br />

mayarwa da Uthman bn Talha da makullan dakin Allah, a kudance ba wata daraja<br />

gare su ba, idan da za a sai da su, ba wani abu bane illa tsofaffin karafa, amma<br />

ba karamin matsayi ne ba a ce mutum ya kasance mai dawainiya da dakin Allah.<br />

Amana a nan ana nufin dora wata dawainiya. Muna iya yankewa da cewar duk<br />

wata gwamnati ko kungiya amana ce. Annabi Muhammad (sallallahu alaihi wa<br />

sallam) ya ce " idan wani shugaba ya dora wasu a wani mukami saboda 'yan<br />

uwantaka, ko abuta ko kuma wadanda aka dora basu cancanta ya rike wannan<br />

mukami ba, to tsinuwar Allah ta tabbata a kan wannan shugaba, sallar su kuma<br />

ba za a karba ba, a karshe kuma za a jefa su wutar Jahannama.<br />

Kamar yadda aka ruwaito a cikin littafin Bukhari, Annabi Muhammad (sallallahu<br />

alaihi wa sallam) ya ce<br />

><br />

" idan aka jingina abu ga wadanda ba su cancanta ba ku saurari tashin kiyama."<br />

Za mu iya karawa da cewar: babu abinda zai hana matsaloli a irin wannan<br />

gwamanti ko kungiya in har aka kauce daga dokokin Alkur'ani da Hadisin Manzon<br />

Allah (sallallahu alaihi wa sallam).<br />

Za mu kara lura da cewa amana babbban nauyi ne wanda lallai ne a sauke shi,<br />

idan a ka ci amana mumman sakamako zai afku, a misali, wani lokaci Abu Zarr


RA ya roki Manzon Allah (sallallahu alaihi wa sallam) ya ba shi wani mukami<br />

babba kamar yadda aka ruwaito a 'Muslim' , sai Manzon Allah (sallallahu alaihi wa<br />

sallam) ya ce :<br />

><br />

> ma'ana su<br />

wadannan sun tsira.<br />

Kamar a aya ta biyu inda Allah SWT ya ke cewa "Idan za ku yi hukunci tsakanin<br />

mutane,kuyi hukunci da adalci" wannan umarni ba a kan shuwagabanni kadai ya<br />

ke ba har ma a kan kowane mahaluki. A nan kowa dole ne a yi mashi adalci a<br />

Musulunci, babu wannan dan uwa ne ko aboki, Musulmi ko wanda ba Musulmi ba,<br />

dan kasa ko bako, kowa lallai ne a dauke shi abu daya bisa adalci.<br />

Yana da kyau mu lura, Allah SWT ya fara ambaton amana sa'annan ya umarce<br />

mu da mu yi adalci, ke nan ya nuna mana adalci baya tabbata sai an dauki wanda<br />

suka cancanta a dora su a kan hakkokin jama'a. A halin yanzu abinda aka rasa ke<br />

nan a wasu gwamnatoci da kungiyoyi har ma da masallatai da makarantun<br />

Islamiyyah. Matukar dai ba a yi abinda ya dace ba, to matsaloli ba za a iya<br />

magance su ba a gwamnatocin nan.<br />

Alqur'ani mai girma ya yi Allah-wadai da akidar nan ta bayar da mukami a<br />

ma'aikatun da hukomomin gwamanti a kan yawan jama'a ko jihohi ko kuma lardi.<br />

Alqur'ani ya ce wannan ba wata dama ba ce ta wani, wannan amana ce ga Allah,<br />

za a bada ta ne ga wanda kadai ya dace ya kuma cancanta. Alqur'ani mai girma<br />

ya fayyace a wata cewa: (qawiyyun ameen) ma'ana sai ya cancanta ko da yana<br />

da gaskiya da rikon addini, wadannan matakai sai sun gamsar. Kumaya bayyana<br />

karara kamar yadda ta kasance a kan annabi Musa a lokacin da ya sami wasu<br />

yara 'yan mata suna rike da shanun su kusa da rijiya. Annabi Musa ya lura<br />

mutane suna zuwa wurin rijiyar da shanun suna jawo ruwa su basu su sha su<br />

tafi,sukuma wadannan 'yan mata suna nan a rike da shanun su tsawon lokaci.<br />

Annabi Musa ya tambaye su " ko me ke faruwa?" sai 'yan matan nan suka amsa<br />

mashi "mu baban mu tsoho ne,kuma mu ba za mu iya jawo ruwa daga cikin rijiya<br />

ba, muna zuwa da shanun mu ne wurin rijiya idan kowa ya tafi sai shanun mu su<br />

sha abinda yayi saura. Annabi Musa AS ya jawo masu ruwa shanun su suka sha<br />

suka koshi, sai 'yan matan nan suka koma gida suka roki baban su da ya dauki<br />

Annabi Musa aiki, domin sun same shi ya cancanta, yana da karfi, gashi kuma da<br />

kyakykyawan hali. Wannan sune hanyoyin da za a dora amana.


A nan, ka'idoji da za a bi wajen bada mukaman gwamnati da hukomomi sune:-<br />

1. Allah SWT shi kadai ne shugaba duk wata gwamnati wakilai ne na Allah ta'ala.<br />

Duk wani iko yana kasa da na Allah ne shi kadai.<br />

2. Ayyukan gwamnati ba za a karkasa su a kan yawan mutane ko yankuna sai dai<br />

wadanda suka dace suka cancanta sune kadai za a rarrabawa mukamai.<br />

3. Tun da mutane wakilai ne na Allah SWTdole ne su bi dokokin Allah a bisa<br />

dukkan lamurra.<br />

4. Idan wani rashin jituwa ya afku, a yi adalci ba tare da nuna kabilanci ba ko<br />

yare ko launin fata ko akida ta addini.<br />

A karshe, mun sani a lokacin Hijirar Annabi (sallallahu alaihi wa sallam) daga<br />

Makka zuwa Madina ya bar Ali a kan gadon shi kuma ya umarce shi da ya mayar<br />

da duk wani abin amana ga masu. A wannan lokaci ne fa dukkan kabilu suka<br />

hada karfi da karfe suka zagaye gidan Annabi (sallallahu alaihi wa sallam) don su<br />

kashe shi kai-tsaye. Annabi Muhammad (sallallahu alaihi wa sallam) ya nuna<br />

kyakykyawan hali ya tabbatar duk an mayar da kayan amana ga masu su har da<br />

wandanda suka nuna mashi mummunar gaba an mayar masu ta kowane hali.<br />

Allah SWTmuna rokon ka ka bamu ikon rikon amana da alkawulla, ameen.


KADDARA DA RABO<br />

Yana da wuya mutane su yarda da cewa rayuwa da mutuwa duka suna hannun<br />

Allah SWT. Akwai tsayayyen lokaci wanda babu wanda ya isa ya canza shi ta<br />

kowace hanya. Allah SWT ya shiryar da mu a kan kaddara da rabo a cikin<br />

Alqur'ani mai girma, Suratul Baqarah, aya ta 246-247 :<br />

><br />


>.<br />

A nan, muna iya ganin cewa: Allah SWT ya tace wadanda suka yi imani na hakika<br />

da wadanda suke masu rauni ta hanyar kogi, kadan da suka yi imani ba wai sun<br />

tunatar da 'yan uwan su bane akan ikon Allah kadai, a'a, har-ila-u' sun nuna<br />

kaskantar da kana su ga Allah SWT ta hanyar yin addu'a a cikin lokaci, don haka,<br />

ba a yarda ba mutum ya yi alfahari da imanin shi ko wani kokarin shi. An


ayyana sakamakon biyayya da mika wuya da karfin halin da suka yi a aya ta<br />

251 ta suratul Baqarah:<br />

><br />

>.<br />

Yana da ban mamaki, mu gani an yi amfani da wannan kalma 'kadan' sau uku,<br />

da farko kadan ne suka mika wuya lokacin da aka wajabta masu yaki, kuma<br />

kadan ne basu sha ruwan kogi ba, a cikin kadan da suka rage wasu daga cikin su<br />

su ki yarda su yi yaki da Jalut da rundunar shi mai karfi. A karshe, yan kadan ne<br />

daga cikin masu cikakken imani a cikin kaddara da rabo suka lamarin(yakin).<br />

Allah SWT ya saka masu ba wai da nasara kadai ba, a'a, har ma da karfin mulki<br />

ya kuma sanar da su hanyoyi masu yawa na hikima. Allah SWT ya fada a cikin<br />

Alqur'ani mai girma: Al Baqarah aya ta 269<br />

><br />

><br />

Khalid bn Al Walid RA, sanannen sahabin Annabi (sallallahu alaihi wa sallam) ne,<br />

Khalid yayi yakoki da yawa wanda har ya kasance babu wani a cikin jikin shi<br />

wanda babu tabon rauni. Yana son ya mutu Shahidi. Daga karshe ya mutu a kan<br />

gadon shi a gidan shi. Kun gani, rayuwa da mutuwa duk a hannun Allah suke shi<br />

kadai.<br />

A nan, yana da kyau mu sami cikakken imani a kan kaddara da raboda umarnin<br />

Allah SWT- cin nasara zai kasance a gare ka. Ya Allah ka kara mana imani a kan<br />

kaddara da rabo, Amin.


ABUTA DA WANDA BA MUSULMI BA<br />

Allah SWT ya ce a cikin suratu Aal Imran, aya ta 28:<br />

><br />

<br />

>.<br />

Dangantaka ta uku ita ce nuna halayya ta gari ga wasu, ita kuma ana kiran ta<br />

(MUDAARAAT), ita ma an yarda a yi ta har ga kafirai ma. Alal misali lallai ne ka<br />

kyautatawa kafirai idan suka kawo maka ziyara. An yarda Musulmai su nuna<br />

halayya ta gari domin su ceci kan su daga sharrin kafirai. Wannan shine ake nufi<br />

a cikin Suratu Al Imran aya ta 28:<br />

Sai dai idan kun ji tsoron hadari ko cutarwa daga gare su""<br />

Dangantaka ta hudu shine ta fuskar kasuwanci, masana'antu ko aiki, wannan ana<br />

kiran shi 'MU'AMALAT' an bada dama ayi da kafirai har idan ba zai cutar da<br />

Musulmi ba, kuma an bada dama a nemi aiki a wajen wanda ba Musulmi ba ko<br />

kuma ka yi aiki a wata masana'antar shi. Har-wa-yau, an bada dama a yi<br />

kasuwanci da kafirai sai dai ba a yarda a sayaar masu da makamai ba idan suna<br />

yaki da Musulmi.<br />

Wannan kyakykyawar halayya Annabi Muhammad (sallallahu alaihi wa sallam) ya<br />

nuna ta. Misali lokacin da aka sami fari a Makka, ya taimake su duk kuwa da<br />

cewa sune suka kore shi daga gidan shi. Har-wa-yau, lokacin da ci Makka da yaki,<br />

mutanen Makka sun yi tsammanin Annabi (sallallahu alaihi wa sallam) zai kashe<br />

su ne ko ya mayar da su bayi ko ya wasashe dukiyoyin su da kadarorin su. Sun


damu matuka suna sauraren hukuncin da Annabi (sallallahu alaihi wa sallam) zai<br />

yanke a jawabin da zai yi mai dimbin tarih. Sai Annabi (sallallahu alaihi wa<br />

sallam) ya fara jawabin sa yana cewa da kafirai:<br />

<strong>مﻮﻴﻟا</strong> <strong>ﻢﻜﻴﻠﻋ</strong> <strong>ﺐﻳﺮﺜﺗ</strong> <strong>ﻻ</strong><br />

"Yau babu sauran zargi a gare ku a kan komai kuma babu wanda zai tsangwame<br />

ku". Babu wani a tarihin Dan Adam da zai iya nuna irin wannan kyakykyawan<br />

haliga abokan gaba. Sakamakon nuna wannan kyaukyawan hali ne mutanen<br />

Makka dubbai suka karbi Musulunci.<br />

Har-wa-yau, Annabi Muhammad (sallallahu alaihi wa sallam) ya bar wakilan<br />

kabilar Banu Thaqeef su zauna a masallacin shi duk da kasancewar su ba<br />

Musulmin ba, ya nuna karimci da mutuntawa.<br />

Khalifa Umar RA ya kasance yana ba kafirai tallafi daga baitil malin gwamnati.<br />

Muna riko da wadannan misalai a cikin ran mu. Sai mu sake duba wadansu<br />

ayoyin Alqur'ani mai girma mu ji abinda su ke cewa akan dangantakar muminai<br />

da kafirai. Allah SWT ya ce a cikin suratul Mumtahanah, aya ta 1:<br />

><br />

Ya ku wadanda kuka yi imani! Kada ku riki makiyi na kuma makiyin ku (kafirai) a<br />

matsayin masoya, kuna nuna kauna a gare su>><br />

A karshen wannan ayar, Allah SWT ya ce, Suratul Mumtahanah aya ta 1:<br />

ﻞ�ﺿ ﺪ�ﻘﻓ ﻢﻜﻨ�ﻣ ﻪ�ﻠﻌﻔﺑ ﻦ�ﻣ و ﻢﺘ�ﻴﻔﺧأ ﺂ�ﻣ و ﻢﺘ�ﻨﻠﻋأ ﺂ�ﻤﺑ ﻢﻠﻋأ ﺎﻧأ و ةدﻮﻤﻟﺎﺑ ﻢﻬﻨﻴﻟإ نوﺮﺴﺗ<br />

ﻞﻴﺒﺴﻟا ءاﻮﺳ>><br />

>.<br />

A cikin Suratul Ma'idah, aya ta 51, Allah SWT ya ce :<br />

><br />

><br />

Haka nan kuma Allah ya fada a cikin suratul Mujadala, aya ta 22:<br />

>



wanda ya cutar da wani kafirin amana da ke zaune a kasar Musulmi nine mai bi<br />

mashi hakki kuma zan yi nasara ".<br />

Har-wa-yau, Ali RA ya ruwaito Annabi (sallallahu alaihi wa sallam) yace " Allah<br />

SWT<br />

Ya yi hani a ci mutuncin wanda ba Musulmi ba dake zaune tare da Musulmi>><br />

Annabi Muhammad (sallallahu alaihi wa sallam) ya ce zan yi rook a madadin kafiri<br />

a ranar tashi alkiyama wadanda aka cuta ko kuma aka tauye masu wata dama,<br />

ko kuma aka takura su ko aka karbe masu wani abu ba tare da hakki ba.<br />

To dangantaka tsakanin Musulmi da kafirai dangantaka ce ta adalci, mutuntawa<br />

da kuma ka'idoji.<br />

Ian rokon Allah ya taimake mu mu zauna kamar yadda aka tsara a kur'ani da<br />

kyakykyawan misali daga Annabi Muhammad (sallallahu alaihi wa sallam) da<br />

sahabban shi.


HALAL DA HARAAM A MUSULUNCI<br />

A cikin Al qur'ani mai girma, Suratul Baqarah, aya ta 188, Allah SWT<br />

Ya ce :<br />

><br />

><br />

Dalilin saukar wannan ayar shine an same shi a cikin littafin 'Ruhul Ma'ani' kamar<br />

haka:<br />

Wasu sahabban Manzon Allah (sallallahu alaihi wa sallam) su biyu sun yi rigima<br />

dangane da wani fili sai suka kawo kara gaban Manzon Allah (sallallahu alaihi wa<br />

sallam). Wanda yake ikirarin cewa filin na shi ne, ba shi da shaida zai nuna na shi<br />

ne. Sai Annabi Muhammad (sallallahu alaihi wa sallam) ya tambayi dayan "ko ka<br />

iya rantsewa da Allah cewa wannan wuri na ka ne ? sai ya amsawa Annabi<br />

(sallallahu alaihi wa sallam), sai ya karanta<br />

aya ta 77 a cikin Suratu Aal Imran a matsayin tunatarwa.<br />

><br />

" Lallai wadanda ke bayar da alkawalin Allah da rantse-rantsen su, (a maimakon<br />

su) a basu wani dan abin duniya, lallai wadannan ba su da rabo a lahira kuma,<br />

Allah ba zai yi Magana da su ba ranar kiyama kuma kuma ba zai tsarkake su ba,<br />

kuma akwai azaba mai radadi a gare su>>.<br />

Wanda ya ke mallakar wannan fili a wannan lokaci ya saurari wannan ayar sai ya<br />

ki yarda yayi rantsuwa, sai ya ji tsoro ya na shakku, filin nan kuwa na shi ne<br />

kuma baya son ya kasance mai asara ranar tashin kiyama. Nan take Annabi<br />

(sallallahu alaihi wa sallam) ya mayar da fili ga mai abin.<br />

Ka sani wannan ayar an saukar da ita ne ta hana wasu tauye dukiyoyi ta<br />

mummunar hanya. Haka nan kuma gabatar da kara na karya da rantsuwa ta<br />

karya da bada shaida ta karya dukkan su haram ne. a farkon ayar an yi amfani<br />

da kalmar (bainakum), a nan yana da ban sha'awa yadda Allah SWT ke koya<br />

mana cewa kaci kayan wasu zai baiwa wasu kwarin gwiwa kai ma su ci kayan ka.<br />

Misali, wani ya hada madara da ruwa sai wani kuma ya sayar da rubabbun kaya<br />

marmari, sai wani kum aya sayar da rubabben dabino. Dukkan su suna cin<br />

dukiyar wani ba tare da son ran shi ba. A gaskiya, har ta kai yanayin da kowa<br />

yake cin dukiyar shi ba bisa ka'ida ba, kuma babu mahalukin da yayi nasara. Abu


na biyu yana koya mana idan ka sa wasu suka yi asarar dukiyar su, suna jin zafi<br />

kamar yadda kai ma kake jin zafi idan kayi asarar ta ka dukiyar. A nan, ka kiyaye<br />

dukiyar kowa tamkar taka wajen kula da ita.<br />

Um Salama RA ta ruwaito daga Manzon Allah (sallallahu alaihi wa sallam) yace "<br />

Ni mutum ne kamar ku, kuna kawo rigingimun ku zuwa gare ni, kuma watakila<br />

wani ya fi abokin rigimar shi iya bayani da dadin-baki, wannan na iya ja na in ba<br />

shi gaskiya. Ku sani cewa sanin hakikanin gaskiya hannun Allah SWT yake shi<br />

kadai, idan abu ba mallakar ku bane kada ku karba, saboda abinda nake ba ku a<br />

wajen wannan shari'ar ba kome bane illa gungumen wuta"<br />

A nan muna iya yanke hukunci cewa babu wata kotu, ko da kotun Manzon Allah<br />

(sallallahu alaihi wa sallam) ce ba za iya maida haram ya zama halal ba ko ta<br />

maida halal haram.<br />

A wata fadar kuma a cikin Surtul Baqarah, aya ta 168, Allah SWT yace :<br />

><br />

><br />

A wata ayar mai kama da wannan a cikin Suratun Nahl aya 51 Allah SWT ya ce :<br />

><br />

>.<br />

A ciki wadannan ayoyi guda biyu, an yi amfani kalmomi guda biyu, 'Halal' da<br />

kuma 'Dayyeb'. Halal ana nufin abinda aka yarda a yi ba ba tare da wani hani ko<br />

iyakancewa ba. Dayyeb kuma abinda ake nufin abin Halal kana son shi ko kana<br />

da sha'ar ka ci.<br />

A nan, muna iya hakikance cewa ayyuka na gari ba za su samu ba sai mun ci<br />

abinda yake Dayyeb. Annabi Muhammad (sallallahu alaihi wa sallam) yayi<br />

bayanin wannan ayar, ya jaddada cewa ba an saukar da wannan ayar bane ga<br />

annabawa kadai, har ma da mabiyan su. Manzon Allah (sallallahu alaihi wa<br />

sallam) yace addua'ar wanda yaci Haram ba karbabbiy ba ce. Ya kara da cewa<br />

mutane da dama suna bada kokari wajen bautar Allah kuma su mike hannayen<br />

suna cewa ya Allah! Ya Allah! Ka karbi addu'ar mu amma idan abin cin su Haram<br />

ne abin shan su Haram ne tufafin su Haram ne yaya za a yi a karbi addu'ar su?<br />

Muslim ne ya ruwaito shi.<br />

Akwai Hadisai da dama daga Manzon Allah (sallallahu alaihi wa sallam) wadanda<br />

suka fayyace tsakanin Halal da Haram.


Manzon Allah (sallallahu alaihi wa sallam) ya ce "wanda suka ci Halal suka bi<br />

tafarkin Annabi Muhammad (sallallahu alaihi wa sallam), sannan ba su zalunci<br />

kowa ba, za su shiga Aljanna" Sahabbai suka ce "ya Annabi (sallallahu alaihi wa<br />

sallam) wannan abu ai ya zama rowan dare ga mabiya a yanzu" Sai Manzon Allah<br />

(sallallahu alaihi wa sallam) ya ce "Akwai mutane da za su a nan gaba da wannan<br />

hanya".<br />

Abdullahi Bn Umar RA ya ce Manzon Allah (sallallahu alaihi wa sallam) yace "idan<br />

kana da halaye guda hudu sun ishe ka ka shiga Aljanna ko da baka sami komai<br />

ba a duniya 1) ka tsare alkawali.2) ka fadi gaskiya. 3) ka kyautatawa mutane. 4)<br />

ka ci abu na Halal.<br />

Wani lokaci Sa'ad Bn abi Waqqas RA ya roki Manzon Allah (sallallahu alaihi wa<br />

sallam) ya roka mashi Allah idan yayi addu'a ta zama karbabbiya, sai Manzon<br />

Allah (sallallahu alaihi wa sallam) ya ce mashi " ya kai Sa'ad, kaci abinda yake<br />

Halal da Dayyib ne Allah SWT zai karbi dukkan ddu'ar ka kuma ka zama wanda<br />

ake karbar addu'ar shi".<br />

Manzon Allah (sallallahu alaihi wa sallam) ya kara da cewa "Na rantse da Allah<br />

SWT wanda rayuwa ta take a gare shi, idan mutum ya ci mafi kankantar abu na<br />

Haram duk wani aikin shi ba za a karba ba har tsawon kwana arba'in. Idan jikin<br />

shi ya ginu da haram to babu abinda ya cacance shi sai wutar jahannam.<br />

Mu'az bn Jabal RA ya ce Manzon Allah (sallallahu alaihi wa sallam) ya ce " Idan<br />

aka tara mu ranar tashin kiyama, babu wanda zai bar wurin shi sai ya amsa<br />

wadannan tambayoyi guda biyar :<br />

1. Yaya ya gudanar da rayuwar shi.<br />

2. Yaya ya gudanar da kuruciyar shi.<br />

3. Yaya ya sami abinci shi.<br />

4. Yaya ya kashe abinda yake samu.<br />

5. Yaya ya tafiyar da ilmin da yake samu.<br />

An karbo daga Abdullahi Bn Mas'ud RA yace Manzon Allah (sallallahu alaihi wa<br />

sallam) yace " Na rantse da Allah wanda rayuwa ta take a hannun shi, wani ba<br />

zai zama cikakken Musulmi ba sai zuciyar shi da harshen shi sun kasance<br />

Musumi, kama makwabtan shi sun tsira daga duk sharrin shi. Idan mutum ya<br />

mallaki dukiya ta Haram idan ya bada sadaka ba za a karba ba, idan kuma ya<br />

batar da ita babu albarka a ciki, idan kuma ya barwa magadan shi ya bar masu<br />

abinda zai kai su zuwa wuta, Allah SWT baya kankare mummunan aiki da wani<br />

mummunan, Allah ya na kankare mummunan aiki da mai kyau ne.<br />

Abadullahi bn Umar yace Manzon Allah SAW ya yiwa wasu gungun masu hijira<br />

jawabi cewa: Ina neman tsarin Allah kuma ina fata abubuwa biyar ba za su<br />

kasance ba a tsakanin ku:


1. Idan munanan halaye suka yawaita a cikin mutane, ko kin hanuwa daga<br />

abinda Allah ya haramta, ko yin shiga mai bayyana tsiraici, Allah zai saukar masu<br />

da bala'I da cututtuka wanda kakannin su ma basu taba jin labarin su ba.<br />

2. Idan mutane suna tauye ma'auni (suna cin hakkin wadansu) kamar yadda<br />

mutanen Annabi Shu'aib su ka yi,to Allah zai saukar da fari da kunci rayuwa da<br />

wahalhalu da azzaluman shuwagabanni a gare su.<br />

3. Idan kuma basu bada Zakka za a dauke masu ruwan sama daga nan sai su<br />

fada talauci da bala'i.<br />

4.Idan suka kauce daga tafarkin Allah SWT da Manzon shi SAW makiya daga wani<br />

bangare za su zo su wasashe dukiyon su da karfi.<br />

5.Idan kuma jami'an gwamnati ko shuwagabanni ba su zartar da wani abu kamar<br />

yadda Allah SWT ya shirya a cikin Alqur'ani mai girma sai Allah ya saka gaba a<br />

tsakanin su sai su yi ta rigingimu a tsakanin su." (Muslim ne ya ruwaito shi)<br />

Ya Allah ka kare mu daga dukkan sabo. A bayyane yake cewa dukkan wasu<br />

abubuwa ba su kawo haduwar-kan Musulmi, hadin-kai zai samu ne kawai ta<br />

hanyoyi wadanda suke na Halal ne.<br />

Yana da ban-sha'awa aya ta 188 a cikin Suratul Baqarah (wadda ta gabata) ta zo<br />

ne bayan cikakkun dokoki da ka'idojin azumi ne a inda aka yi haramta cin wasu<br />

abubuwa na halala har zuwa wani kayydajjen lokaci. Don haka, yin manufar yin<br />

azumi ita ce domin ya sanya da'a da koyon kamun-kai wajen amfani da<br />

abubuwan da suke na halal ne. wannan koyarwa da kamun-kai da dangana yana<br />

da amfani kwarai. Ta hanyar wannan koyarwa mutum ya barranta kwata-kwata<br />

daga abubuwan da suke na haram ne. karin bayani, duk wanda zai yi buda baki<br />

yayi da abinda yake na halal ne. Idan abincin haram ne yayi buda-baki da shi<br />

Allah SWT baya karbar wannan azumi.<br />

Daga karshe, hanyoyi na halal da haram sune wanda Allah SWT ya bayyana. Duk<br />

wasu tarurruka na duniya da kulla yarjejeniya ba zai warware wannan matsala<br />

ba, tunda kowa kokarin shi shine ya kare kan shi. Haka kuma yarjejeniya da aka<br />

kulla da nufin matsawa wani ko ko wata kasa akwai son zuciya ne a ciki don haka<br />

babu wata hujja mai karfi a ciki. dokokin Allah su ne na gaskiya a ko wane lokaci.<br />

Kamar yadda aka fada a baya, Allah SWT ya fayyace halal da haram, ba a barsu<br />

a karkashin hukuncin wani annabi na wani lokaci ba. Tsarin Allah shine wanda ba<br />

kuskure a ciki shi.<br />

Ya Allahka bamu ikon mu tsaya a kan halal, ka kare mu daga fadawa cikin<br />

iyakokin na haram da kuma abubuwa masu rikitarwa.


SURATUL FATIHA<br />

Suratul Fatiha ita ce Sura ta farko a jerin Surorin Al qur'ani mai girma, tana da<br />

muhimmanci kwarai saboda dalilai masu yawa:<br />

1. Ita ce sura ta farko wadda a dunkule a ka saukarwa Manzon Allah SAW ita,<br />

shine ya sa ake kiran ta 'Fatihatul Kitab'<br />

2. Har-wa-yau, ana kiranta 'Ummul Kitab' kuma 'Ummul Qur'an'. Abu Hurairah,<br />

RA yace Manzon Allah SAW yace " na rantse da ubangiji wanda rayuw ta take a<br />

hannun shi, babu makamanciyar wannan surar a littafan da aka saukar, har ma a<br />

cikn Al qur'ani". Muslim da Tirmizhi ne suka ruwaito shi.<br />

3. Anas RA yace Manzon Allah SAW yace " A cikin duk surorin da ke cikin<br />

Alqur'ani Suratul Fatiha ita ce babba.<br />

4. Wanna sura har-wa-yau, ana kiran ta 'Sura ash ashifa'' (sura mai warkarwa)<br />

A yanzu za mu yi kokari mu fahimci ma'anar wannan sura da kadan-kadan.<br />

Al hamdu lillah na nufin dukkan wani irin yabo ya tabbata ga Allah SWT shi kadai.<br />

Ba yabo da godiya ga Allah SWT bane kawai, a'a, har ma akwai ma'anar kadaita<br />

Allah a cikin ta, don haka manufa ko dalilin yin yabo an gina shi ne a cikin ta.<br />

Wannan misali ne na farko na fasahar magana ta Alqur'ani.<br />

" Lallai dukkan yabo ya tabbata ga Allah, Mahaliccin kowa da komi"<br />

A nan, farkon ginshikin da aka kafa Musulunci shine "imani", an gina shi a kan<br />

wannan takaitacciyar kalma.<br />

Har-wa-yau, 'Alhamdu lillahi rabbil aalamiin' shi ma dalili ne na dukkan wani irin<br />

yabo yana ga Allah shi kadai. Ma'ana, Allah SWT shine Mahalicci, Majibincin mu,<br />

Mataimakin dukkan duniya wacce aka sani da wadda ba a sani ba, ta kowace<br />

hanya<br />

Bari mu ga yadda yayain bayanin halittar shi a cikin Al qur'ani mai girma. A<br />

misali, Allah SWT ya ce a cikin Alqur'ani, Suratat az Zaariyaat aya ta 47,48,49:<br />

><br />


wadannan ayoyi da Allah SWT ya yi bayanin su a wurare da yawa a cikin Alqur'ani<br />

mai girma shekaru aru-aru da suka wuce. Sai Allah SWT yace a cikin Suratul<br />

Waaqi'ah aya ta 68-73.<br />

><br />

" Shin ba ku ganin rowan da kuke sha ? shin kune kuke saukar da shi daga gizagizai<br />

ko kuma mune masu saukar da shi? Da mun so sai mu sanya shi ya zama<br />

mai zartsi (wanda bashi da amfani). To me ya sa kuma ba za ku godewa Allah<br />

ba?<br />

Shin ba ku ganin wutar da kuke kunnawa? Shin kune ku ka yi itatuwan ta (wanda<br />

a ke tada wuta da su) ko kuma mu ne masu yin su? Mu ne mu ka sanya ta<br />

(wutar) ta zama abin jin dadi ga masu yawo a cikin daji>>.<br />

Ka sani wannan ayar tana tunatar damu game da wutar lahira. A nan duniya,<br />

Allah SWT ya bamu ikon amfani da wuta domin jin dadin mu har ma mu yi girkegirken<br />

mu.<br />

Sai kuma Allah SWT ya yi Magana akan halittar Dan Adam a cikin Surat Al insan,<br />

aya ta 1,2,3, y ace:<br />

><br />

><br />

Shi mutum kamar wata mu'ujizar duniya yake. Da wasu bangarori suke iki da<br />

junan su a cikin kwanciyar hankali. Wannan babbar alama ce ta mahalicci. Shine<br />

ya sa Allah SWT ya ce a cikin Alqur'ani mai girma :<br />

><br />

>.<br />

Wannan ya bamu takaitaccen bayanin halittu na Allah SWT. Yanzu bari mu duba<br />

ma'anar 'Ar Rahman' da 'Ar Raheem'. Dukkan wadannan kalmomi am tsamo su<br />

ne daga tushe daya shine 'Ar Rahmah'.


'Ar Rahamaan' tana nufin: rahama tun daga farko har karshe, wannan kalma ce<br />

da bata da jam'i, kuma 'AlRahaman' za a iya amfani da ita ne ga Allah SWT kadai.<br />

'Ar Raheem' shine: cikakkiyar ko dawwamammiyar rahama. Wannan kalmar ana<br />

iya amfani da ita ga mutum ma. Misali Allah SWT siffanta Annabi SAW da cewa:<br />

ﻢﻴﺣر فوؤر<br />

Ma'ana :Mai matukar tausayi da kuma dawwamammiyar rahma ga wanda suka yi<br />

imani.<br />

Na ukku sai mu ce Allah SWT shine sarki a ranar hisabi.wannan yana bukatar<br />

sharhi na kashin kan shi. Aya ta gaba ita ce :<br />

ﻦﻴﻌﺘﺴﻧ كﺎﻳإ و ﺪﺒﻌﻧ كﺎﻳإ<br />

"Kai kadi muke bautawa kuma daga gare ka kadai mu ke neman taimako (a kan<br />

dukkan komi)."<br />

A nan, dukkan wani irin yabo ga Allah SWT wanda ya halicce mu kafin yanzu, a<br />

yanzu kuma yayi mana cikkakkiyar rahama, a nan gaba kuma shi kadai ne mai<br />

cikakken mulki a ranar sakamako. Idan haka ne don me ba za mu ce "shi kadai<br />

muke bautawa kuma shi kadai muke neman taimako a gare shi ba". Wannan ayar<br />

ana kiran ta zuciyar Suratul Fatiha. Yabo ne ga Allah SWT kuma addu'a ce ta<br />

neman taimakon Allah SWT.<br />

Abu na gaba sai mu fara da addu'a, muna rokon Allah ya shiryar damu a kan<br />

hanya madaidiciya. Kalmar "shiriya" tana bukatar bayani. Allah SWT ya na bada<br />

shiriyar shi ta hanyoyi guda uku. Allah SWT ya bada shiriya ga dukkan ababen<br />

halittar shi kamar yadda ya zo a bangarori da dama na Alqur'ani mai girma.<br />

Misali, Allah ya ce a Surat Al Isra' aya ta 44 :<br />

><br />

Sammai bakwai da kasa da duk abinda ke cikin su suna yin tasbhi gare shi (Allah<br />

SWT), babu wani abu face yana tasbihi da godiyar shi (Allah SWT) sai dai ku<br />

(mutane) ba ku fahimtar tasbihin su. Lallai shi ya kasance mai matukar hakuri ne<br />

kuma mai yawwan gafara>><br />

Dubi bakin iyakar mu. Lallai Allah SWT ya bada shiriya ga bishiyoyi, taurari, har<br />

ma duwatsu.<br />

Har-wa-yau, Allah SWT ya kara cewa a cikin Surat An Nuor, aya ta 41:<br />

Shin baku ganin duk abin da ke cikin sammai da kasa duk su na tasbihi ga Allah<br />

SWT, har ma da tsuntsaye su na masu shawagi da fuka-fukan su. Allah ya san<br />

addu'ar ko wanne daga cikin su da kuma tasbihin da yake yi wa Allah SWT. Lallai<br />

Allah Masani ne da abinda su ke aikatawa.


Har-wa-yau, Allah SWT ya ce a cikin Surat Al A'la, aya ta1-3:<br />

" Yi tasbihi da sunan Ubangijin ka, wannan da yayi halitta kuma ya daidaita<br />

halittar, wannan da ya tsara halittar shi kuma ya shiryar da su"<br />

a nan, komi yana da hanyar shiriyar da zai bi. Misali, kunne ba zai iya amfani ba<br />

wajen gani, haka kuma idanu wajen ji. Wannan ne ya sa Allah SWT ya ce a cikin<br />

Surat Maryam<br />

" Babu abinda ya ke cikin sammai ko kasa face bawa ne ga Allah "<br />

Abu na biyu, Allah SWT ya na bayar da shiriyar shi ta hanyar Manzannin Shi da<br />

littafan Shi.<br />

Na ukku : Allah SWT yana bada shiriyar Shi kai tsaye ga zababun bayin Shi.<br />

Daga cikin dukka alheran da Allah SWT yayi wa ababen halittar Shi abu mafi<br />

girma shine bada shiriya a gare su. Ba don wannan shiriyar ba to da an rasa<br />

dukkan halittu da kuma dukkan tsarin ya ruguje. Yanzu ke nan za mu iya<br />

tabbatar da cewa Allah SWT akwai wani nau'i na shirya da yayi ga dukkan komi.<br />

Me ya sa muke rokon Allah ya shiryar da mu akan hanya madaidaiciya? Haka<br />

kuma manzannin Shi hakika suna kan hanya madaidaiciya, me ya sanya<br />

wadannan Manzannin suke ta rokon Allah ya shiryar da su hanya madaidaiciya?<br />

Amsar wannan tambaya shine: Allah SWT zai iya kara shiriyar Shi a kan kowa,<br />

don haka babu wanda zai dauki kan shi a matsayin wanda ya wuce wannan<br />

larurar. A misali, Allah SWT ya cewa Annabi Muhammad SAW lokacin da yake<br />

bayanin fa'idojin cin Makka da yaki a cikin Suratul Fath:<br />

" Daya daga cikin fa'idojin shine a shiryar da ku hanya madaidaiciya"<br />

A hakika, dukkan Annabawa suna yin kokari daga wannan babban matakai zuwa<br />

ga babban mataki na shiriya daga Allah SWT<br />

ﻢﻬﻴﻠﻋ ﺖﻤﻌﻧأ ﻦﻳﺬﻟا طاﺮﺻ<br />

"Siratal lazina an'amta alaihim"<br />

Addu'a ce mai mai matukar ban-mamaki, tana cewa " ka nuna manar hanyar<br />

wadanda ka yi wa ni'ima"<br />

An yi cikakken bayanin wannan jimla a cikin Surat an Nisa' :<br />

" wanda duk ya bi umarnin Allah SWT Annabi Muhammad SAW to hakika<br />

wadannan suna tare da wadanda Allah SWT yayi wa ni'ima, daga cikin Annabawa,<br />

masu gaskiya, shahidai da kuma mutanen kirki"<br />

ka sani fa ba muna cewa " ka nuna mana hanya madaidaiciya ta Annabawa ko<br />

hanya madaidaiciya da aka yi bayanin ta a Alqur'ani. Alal- hakika, Allah SWT yana<br />

nuna mana cewa mu nemi ita wannan daidaitacciyar hanya a bisa shiryarwar<br />

alqur'ani mai girma a tawagar mutanen kirki wanda ake samun su kowane<br />

zamani.


Manzon Allah SAW ya taba cewa sahaban shi " Al'umma za ta karkasu kashi<br />

sabai'in, amma kashi daya ne zai kasance a kan hanya madaidaiciya" sahabbai<br />

suka tabaye shi "wadanne ne ?" sai Manzon Allahj SAW ya amsa " sune wadanda<br />

suka bi hanya ta da kuma hanyar saddhabban na". A nan, bin tafarki na mutanen<br />

kirki yana da amfani. Wani baiti da aka yi da yaren Urdu ya na cewa:<br />

" Ayyukan kwas suna bayar da sanin kalmomi ne kadai, amma malami mai<br />

koyarwa shi yake gyara matsayin mutum".<br />

Wadansu musulmi suna bin suna bin bayanan Alqur'ani wajen neman shiriya<br />

amma sai su manta da mutanen kirkin da ke kewaye da su, sun manta Allah<br />

SWT ya turo Manzon shi a matsayin malami mai koyarw. Hatta fasahohi na<br />

rayuwar duniya kamar ta ilmin likita koyarwa ta hanyar takardu kadai ba ta<br />

wadatarwa, tana bukatar malami.<br />

Wadan su musulman kuma suna bayar da hankalin su kadai a kan mutanen kirki<br />

na zamanin su wajen neman shiriya su kauda kai daga Al qur'ani mai girma. A<br />

nan sai matsala ta shiga tsakanin wadannan bangarori. A hakika, muna bukatar<br />

koyarwa ta Al qur'ani da tafarkin salihan mutane wadanda ke a cikin ko wane<br />

nau'I na mutane. Shine yasa Allah SWT ya ke nuni wajen wadannan mutane<br />

wajen neman hanya madaidaiciya wajen neman shiriya.<br />

A karshe, muna rokon Allah SWT kada ya sanya mu a kan hanyar wadand yayi<br />

fushi da su, hanyar wadanda karkace. Wannan ana nuni ne ga Yahudawa da<br />

kiristoci. An samo daga Abu Hurairah RA a cikin 'Muslim' cewa Manzon Allah SAW<br />

ya ce " Allah SWT ya ce na raba salla tsakani na da bawa na gida biyu, ina bashi<br />

duk abinda ya ke so.<br />

IDAN MUTUM YA CE SAI ALLAH YACE<br />

* Alhamdu lillahi rabbil alamin bawa na ya gode mani.<br />

* Ar Rahmanir rahim Bawa na ya yabe ni.<br />

* Maliki yaumid din Bawa na yayi bayanin karfi na<br />

* Iyyaka na'budu wa iyyaka nasta'in Wannan tsakanin bawa na ne<br />

da ni.<br />

Farkon wannan ayar yabo ne ga Allah SWT bangare na biyu kuma addu'a<br />

* Ihdinas siraatal mustaqim Bawa na zai sami duk abinda<br />

ya roka.<br />

A nan, Suratul Fatiha yabo ne ga Allah kuma addu'a ce madaukakiya zuwa ga<br />

hanya madaidaiciya. Ya Allah SWT ka gwada mana ka bamu ikon bin wannan<br />

hanya madaidaiciya har lokacin mutuwar mu. Amin.<br />

Muna godiya ga Allah SWT da ya koyar da mu yadda za mu yabe shi, yadda za<br />

mu roke shi da kuma abinda zamu roke Shi. Allah SWT ya koya mana yadda za<br />

mu yabe shi cewa : "Al hamdu lillahi Rabbil aalamin". Wannan shine zai kasance


gaisuwar 'yan aljanna kamar yadda a cikin Alqur'ani Allah SWT ya bamu alfarmar<br />

mu yi amfani da wannan kalmar a nan duniya. Lallai Allah SWT mai rahma ne ga<br />

bayin Shi masu biyayya. Babban abinda ya fi dacewa shine mu rufe wannan<br />

bayani da cewa ' Al hamdu lillahi Rabbil aalamin'.


ISRA'I DA MI'RAJI<br />

Allah SWT yace a suratul Isra'i :<br />

><br />

" Tsarki ya tabbata ga Wanda ya dauki bawan Shi da dare daga masallacin<br />

harami ya zuwa masallacin masallaci mafi nisa (Kudus)wanda muka yi albarka a<br />

gare shi, domin mu nuna mashi ayoyin mu, lallai shi Allah mai ji ne kuma mai<br />

gani ne"<br />

Wannan tafiya da Annaci SAW yayi ta kasu gida biyu. Na farko shine tafiya daga<br />

Makka zuwa Kudus, ana kiran ta 'isra'i'. bangare na biyu kuma shine daga<br />

masallacin Kudus zuwa sama, wanann kuma shine 'Mi'raji'. Ya kamata mu dubi<br />

dalilan da suka sanya yin wannan tafiya domin mu fahimci Isra'i da Mi'raji.<br />

Akwai abubuwan da suka faru shekara daya da rabi kafin tafiyar. Da farko kafirai<br />

sun kara matsa kaimi wajen takurawa da muzgunawar da suke yiwa musulmi. A<br />

wannan lokaci musulmi ba a basu damar su yi yaki ba a kowane irin hali suke.<br />

Allah SWT yayi umarni a cikin Suratul Baqarah aya ta 109:<br />

"Ku yafe ku kauda kai har sai umarnin Allah ya zo"<br />

kuma ya faru a lokacin da kawun Manzon Allah SAW, Abu Talib wani babban karo<br />

ne ga Annabi SAW daga kafirai, wannan shine ma ya sa kafirai suka kara<br />

tsandare. Kuma bayan rasuwar Abu Talib, matar Annabi SAW Khadija ta rasu, sai<br />

abubuwa suka cabewa Manzon Allah SAW. A cikin wannan yanayi sai Annabi SAW<br />

yayi shawarar komawa Ta'if ya ci gaba da yada musulunci. Ya tsammaci goyon<br />

baya daga shuwagabannin wannan gari, tunda dangi ne na mahaifiyar shi.<br />

Wadannan shuwagabanni su ka ko-in-kula da Annabi SAW lokacin da ya sauka a<br />

garin. Daga karshe ma si suka turo mashi yara suna jifar shi har suka ji mashi<br />

rauni kwarai sai da ta kai takalmin shi ya cika da jini da yake kwarara daga kan<br />

shi, sai ya fake a wani lambu a bayan garin. Mai lambun ya tausaya mashi ya<br />

korar mashi yaran. A nan sai Mala'ika ya zo mashi ya ce da shi " ya Muhammad<br />

hakika mutanen wannan gari azzalumai ne, idan kana so zamu birkice wannan<br />

gari mu lalata shi baki daya. Annabi SAW ya ce ni na zo ne domin rahma ga kowa<br />

ba domin azaba ba. Ina fata mutanen wannan gari nan gaba za su gane gaskiya.<br />

Saboda munanan abubuwa da suka faru a wannan shekara shine ya sa ake kiran<br />

ta " Shekarar bakin-ciki".<br />

lokacin da Annabi Muhammad SAW ya dawo Makka sai aka hana shi shiga, domin<br />

yanzu sun dauke shi ba mazaunin Makka ba, sai bayan da aka yi shawarwari<br />

sa'annan aka kyale shi ya shiga amma da sharadin ba zai sake yiwa kowa wa'azi<br />

ba a Makka, Annabi SAW yana wa'azi ne kadai a wajen wasu taruka ko wasu


ukukuwa a wajen Makka. Wannan ya nuna mawuyacin hali da matukar hakuri<br />

da karfin hali na Annabi SAW. Allah SWT ya bashi lada mai yawa saboda tsananin<br />

hakurin shi ya dauke shi zuwa wannan tafiya ta Isra'i da Mi'raji.<br />

Bari mu bayyana yadda Isra'i ya ke. Mala'ika Jibril ya zo masallacin Makka, ya<br />

umarci Annabi SAW da yayi alwalla da ruwan zam zam. Ya dauki Annabi SAW<br />

akan wani doki mai sauri, ana kiran shi Buraqa daga masallacin Makka zuwa<br />

masallacin kudus. Annabi SAW ya yi sallah raka'a biyu, sai Mala'ika Jibril ya bashi<br />

kofi biyu, daya na madara daya kuma na giya, sai Annabi SAW ya karbi na<br />

madara, sai Mala'ika yace "ka zabi abinda yake tabbatacce kuma mai kyau, ka<br />

sami shiriya ta gari , haka kuma al'ummar ka, da ka zabi giya da al'ummar ka<br />

sun karkace. Mun sani cewa giya ita ke kai al'umma ga tabarbarewa, kuma ana<br />

kiran ta<br />

Uwar zunubbai. Don haka, musulunci an gina shine akan tsafta/tsarki, gaskiya da<br />

kuma kyautatawa.<br />

Bayan nan sai Mi'raaj. Mala'ika Jibril ya dauki Annabi Muhammad SAW akan<br />

Buraqa suka yi sama, suka je sammai da-ban-da-ban. A can ne Annabi SAW ya<br />

sadu da sadu da Annabi Adam a sama ta farko, Annabi Yahaya da Annabi Isa a<br />

sama ta biyu, Annabi Yuosuf a sama ta uku, Annabi Anaq a sama ta hudu,<br />

Annabi Haaroun a sama ta biyar, Annabi Musa a sama ta shidda, Annabi<br />

Ibraheem a sama ta bakwai. Annabi Muhammad SAW ya yi sallama ga dukkan<br />

wadannan shuwagabanni namu.<br />

A wani wurin Annabi SAW ya ga Mala'ika Malik mai tsaron wuta. Annabi SAW ya<br />

roki Mala'ika Jibril ya bar shi ya ga yadda wuta take, Mala'ika Malik ya daga wuta<br />

Annabi Muhammad SAW ya wata irin wuta wadda za ta iya cinye komi. An<br />

nunawa Annabi Muhammad SAW misalin irin azabar da dake yiwa wadanda suka<br />

aikat zunubai.<br />

Ya ga wadansu mutane leben su kamar an rakumi kuma suna da dunkulen wuta<br />

a hannuwan su, ya gan su su na sanya wannan dunkulen wuta a bakin su, sai<br />

kuma dunkulen wutar ya fito daga duburar su. Mala'ika Jibril yayi bayanin cewa<br />

wadannan su ne maciya amana da a ka damka a hannun su.<br />

Ya gani SAW wadan su mutane masu katon ciki sa'annan mahaukatan rakumma<br />

masu jin kishi suna tattaka su, a ka yi wa Annabi Muhammad SAW bayanin cewa<br />

wadannan sune masu cin kudin riba (kudin ruwa)<br />

Ya ga wadan su mutane wadanda ke da abinci mai kyau da kuma abincin marar<br />

kyau gurbatacce a ajye kusa da su, amma suna cin abincin marar kyau<br />

maimakon wanda yake mai kyau din. Aka fada mashi cewa wadannan sune masu<br />

gujewa matan su na halal.


Sa'annan ya ga wasu mata wanda aka rataye su da nonon su, aka fada mashi<br />

cewa wadannan su ne suke cin amanar mazajen su.<br />

A wanann tafiya, Annabi Muhammad SAW ya zarce saman bakwai inda babu wani<br />

Mala'ika da ya taba zuwa. A nan ne Annabi Muhammad SAW ya ga ayoyin Allah a<br />

wannan wuri mai daraja. Allah yayi bayani a cikin Suratun Najm aya ta 17-18 :<br />

ىﺮﺒﻜﻟا ﻪﺑر تﺎﻳاء ﻦﻣ ﺁر ﺪﻘﻟ , ﻰﻐﻃ ﺎﻣ و ﺮﺼﺒﻟا غاز ﺎﻣ<br />

><br />

wannan ya nuna matsayin nutsuwa da kamun kai na Annabi SAW. Ya ga abinda<br />

ya kamata ya gani, har tsawon lokacin da ya ke son gani. Bai yi wani doki da<br />

kagara ba a lokacin da yana kallon kudurar Allah da kuma iradar Shi.<br />

Wajen wannan kusantaka da Allah an bashi abubuwa guda uku.<br />

An fadawa Annabi Muhammad SAW cewa duk wanda yayi kalmar shahada<br />

sahihiya zai shiga Aljanna.<br />

Annabi Muhammad SAW ya karbi ayoyi biyu na karshe na Suratul Baqrah.<br />

Da farko an bashi salloli guda hamsin a rana daya, aka rage su zuwa biyar<br />

rangwame na musamman da aka yiwa al-umar sa. Kuma za su sami ladar salla<br />

hamsin idan suka yi guda biyar. Allah SWT yana kyautatawa al'umar Annabi<br />

Muhammad SAW.<br />

Annabi Muhammad SAW yace :<br />

ﻦﻣﺆﻤﻟا جاﺮﻌﻣ ةﻼﺼﻟا<br />

" Sallah ita ce mi'rajin Mumini" ita ce dangantaka ta kusa tsakanin Ubangiji da<br />

bawan shi.<br />

Bayan da Annabi SAW ya karbi wannan sako sai ya sauko zuwa ga masallacin<br />

Kudus, sauran Annabawa suma suka zo, annabi Muhammad SAW ya jagorance su<br />

suka yi salla. Ya nuna cewa sakonnin manzanni Allah duk daya ne kuma ya nuna<br />

ya nuna fifikon Annabi Muhammad SAW a kan sauran manzanni.<br />

Daga nan sai mala'ika Jibril ya maido Annabi Muhammad SAW zuwa Makka a<br />

cikin dare daya. A lokacin da kafirai suka sami labarin tafiyar Annabi Muhammad<br />

SAW daga Makka zuwa Kudus zuwa sama ta bakwai duk a dare daya sai suka<br />

maida maganar abin dariya. Sai kafiran suka samin sayyidina Abubakr suka ce da<br />

shi " ka ji abinda abokin ka yake ikirari da shi na tafiya a cikin dare? Sai Abubakr<br />

RA ya tambaya " lallai manzon Allah shi ne ya fadi hakan?" sai kafiran suka ce<br />

lallai shi ya fadi, sai Abubakr ya ce lalllai ikirarin shi gaskiya ne. Tun daga nan<br />

Annabi Muhammad SAW yake kiran Abubakr 'As siddiq'.<br />

Aya ta farko a cikin Surat al Isra' tana karantar da mu abubuwa da yawa, misali,<br />

Allah SWT yana amfani da kalmar 'Abd' ko bawan Allah mai biyayya wajen


ambaton Manzon Allah SAW a maimakon ya kira shi da duk wani suna. Wannan<br />

yana nuna duk da ya kai matukar kusanci da Allah SWT amma yana nan a<br />

matsayin bawa mai biyayya, ba wai tsara ne na Allah ba ko ta wane bangare. A<br />

nan ana nuna maka kada mu hada Allah da kowa a wurin bauta kamar yadda<br />

wasu mabiya littafai ke yi.<br />

Har-wa-yau, wannan tafiya an yi ta ne da amfani da gangan jiki da kuma zuciyar<br />

Manzon Allah SAW saboda an yi anfani da wannan kalma ' Al abd'. A wannan<br />

ayar, kalmar 'Al abd' ta kunshi gangan jiki da kuma rai ba wai daya daga cikin su<br />

ba. Kuma ayar ta nuna mana mu so masallacin Kudus wanda Allah ya albarkaci<br />

dukkan kasar da ke kewaye da shi.<br />

Dadin-dadawa, kalmar 'Lailan' da ta zo a cikin ayar ta na nufin bangaren dare.<br />

Allah mai ji ne kuma mai gani ne, ya ji addu'ar Annabi SAW kuma ya ga hakurin<br />

shi sai ya saka mashi da wannan tafiyar mai girma ta Isra'i da Mi'raaji wadda<br />

take nufin cewa daga karshe shine zai ci nasara.<br />

I na rokon Allah SWT ya bamu ikon fahimtar ainihin manufar Isra'i da Mi'raaji,<br />

Ameen.


YAKIN BADAR<br />

Ba a umarci musulmi ba da su yi yaki tsawon zaman su shekara goma sha uku a<br />

Makka ko da kuwa ana muzguna masu ko an fitar da su daga gidajen su. Bayan<br />

hijrar Manzon Allah SAW daga Makka zuwa Madina ya shirya dangantaka da<br />

wadanda ba musulmi ba a matsayin yarjejeniya kuma ya kafa daular Musulunci.<br />

A tarihin addinin Musulunci, yakin badar shine na farko wanda kafirai sun ninka<br />

musulmi yawa har sau uku. Rundunar musulmi ta kunshi mutum 313, rakumma<br />

70, dawaki 2 da takubba 8. Annabi Muhammad SAW sun hau rakumi daya da shi<br />

da Abu Lubabah RA da Ali, kamar yadda su ma sauran su ka yi. Su kuma kafirai<br />

sun kunshi sojoji 1000 da makaman su, rakumi 700, dawaki 100.<br />

Za mu yi bayanin abubuwan da suka faru kafin lokacin yakin da lokacin yakin da<br />

kuma bayan yakin domin mu sami koyami daga wannan yakin.<br />

Kafin yakin, Annabi Muhammad SAW ya damu matuka, ya roki Allah SWT cewa<br />

idan aka cinye wadannan musulmin da yaki to da kyar za a samin sauran<br />

musulmi wanda za su daukaka kalmar Allah SWT. Wannan lamari an yi bayanin<br />

shi a cikin Surat Al anfal, aya ta 9-10:<br />

ﷲا ﻪ�ﻠﻌﺟ ﺎ�ﻣو , ﻦﻴﻓدﺮ�ﻣ ﺔ�ﻜﺋﻼﻤﻟا ﻦﻣ ﻒﻟﺄﺑ ﻢآﺪﻤﻣ ﻲﻧأ ﻢﻜﻟ بﺎﺠﺘﺳﺎﻓ ﻢﻜﺑر نﻮﺜﻴﻐﺘﺴﺗ ذإ<br />

ﻢﻴﻜﺣ ﺰﻳﺰﻋ ﷲا نإ , ﷲا ﺪﻨﻋ ﻦﻣ <strong>ﻻ</strong>إ ﺮﺼﻨﻟا ﺎﻣو ﻢﻜﺑﻮﻠﻗ ﻪﺑ ﻢﻜﺑﻮﻠﻗ ﻦﺌﻤﻄﺘﻟو ىﺮﺸﺑ <strong>ﻻ</strong>إ<br />

(ka tuna) lokacin da kuke neman taimakon Ubangijin ku, sai ya amsa maku da<br />

cewa "Zan agaza maku da mala'iku dubu wanda za su ci gaba da zuwa wasu<br />

bayan wasu har sai an kammala yakin, Allah SWT yana yin haka ne don ya baku<br />

kyakykyawan albshir kuma zuciyar ku ta sami nutsuwa da zuwan wadannan<br />

mala'iku. Nasara ba daga kowa take ba face daga Allah shi kadai. Lallai Allah<br />

mabuwayi ne kuma mai matukar hikima".<br />

Allah SWT yana bada sanarwa zai kawo gudun-mawar mala'iku ne domin ya ba<br />

muminai bayyanannar hujja domin zuciyar su ta wadatu. Allah SWT yana cewa<br />

kada ku yi tsammanin wannan taimako daga mala'iku yake. Hakika nasara daga<br />

Allah take shi kadai, kuma shine ya turo da wadannan mala'iku.<br />

An umarci mala'iku su yi abubuwa da yawa. Allah SWT ya fada a cikin Suratul<br />

Anfaal, aya ta 12:<br />

اوﺮ�ﻔآ ﻦﻳﺬ�ﻟا بﻮ�ﻠﻗ ﻲﻓ ﻲﻘﻟﺄﺳ اﻮﻨﻣاء ﻦﻳﺬﻟااﻮﺘﺒﺜﻓ ﻢﻜﻌﻣ ﻲﻧأ ﺔﻜﺋﻼﻤﻟا ﻰﻟإ ﻚﺑر ﻲﺣﻮﻳ ذإ<br />

نﺎﻨﺑ ﻞآ ﻢﻬﻨﻣ اﻮﺑﺮﺿاو قﺎﻨﻋﻷا قﻮﻓ اﻮﺑﺮﺿﺎﻓ ﺐﻋﺮﻟا<br />

(ka tuna) lokacin da uban gijin ka yayi wahayi ga mala'iku cewa ina tare da ku,<br />

don haka kuj tabbatar da wadanda suka yi imani. Da sannu zan jefa tsoro a cikin<br />

zukan kafirai. Ku sare kawunan da yatsun kafirai".


Mun ji daga wannan ayar mala'iku ba wai sun karfafi zuciya da kuma duga-dugan<br />

musulmi ba, har ma sun shiga yakin . Abu Dawoud hanafi da Suhail bn Haneef<br />

sun ce " mun kasance muna nuna kafiraia da takubban mu sai su fadi kasa tun<br />

kafin takubban mu su isa gare su. Hakika wadannan mala'iku su ke wannan aiki.<br />

Aya ta 50 a ciki Suratul Anfal ta kara bayyana yadda abin ya faru :<br />

باﺬ�ﻋ اﻮﻗوذ و ﻢهرﺎﺑدأ و ﻢﻬهﻮﺟو نﻮﺑﺮﻀﻳ ﺔﻜﺋﻼﻤﻟا اوﺮﻔآ ﻦﻳﺬﻟا ﻰﻓﻮﺘﻳ ذإ ىﺮﺗ ﻮﻟو<br />

ﻖﻳﺮﺤﻟا<br />

Da za ka ga yadda mala'iku ke daukar ran kafirai, suna dukan fuskokin su da<br />

bayan su (su na cewa) ku dandani azabar wuta"<br />

Wanan ayar tana nuan mana idan mala'iku za su dauki ran kafiri daga jikin shi<br />

suna azabtar da shi ta hanayr bugon shi a fuska da kuma bayan shi da sandar<br />

karfe mai zafi. Allah SWA ya kara da cewa a cikin Suratul Anfal, aya ta 51:<br />

"wannan (azabar) an yi maku ita ne saboda ayyukan da kuka yi wa kan ku,<br />

kuma lallai Allah ba mai zaluttar bayin shi ne ba"<br />

Har-wa-yau, a aya ta 14 Suratul Anfal, Allah SWT yace ku dandani azabe yanzu,<br />

akwai azaba babba a ranar tashin al kiyama. Mun hakikance cewa 'sakraatul<br />

maut' ko kuma lokacin mutuwa lokaci ne mai tsanani ga kafirai, ana azabtar da<br />

su saboda sun ki Allah SWT da manzon Shi. Duk wanda ya ki Allah da manzon<br />

Shi to Allah mai tsananin azaba ne.<br />

Akwai wadansu abubuwan mamaki da suka faru kafin yakin. Misali Annabi<br />

Muhammad SAW ya yi mafarki kafin yakin, kamar yadda aka yi bayani a Suratul<br />

Anfal, ay ta 43:<br />

ﷲا ﻦ�ﻜﻟو ﺮ�ﻣﻷا ﻲ�ﻓ ﻢﺘﻋزﺎﻨﺘﻟ و ﻢﺘﻠﺸﻔﻟ اﺮﻴﺜآ ﻢﻬآارأ ﻮﻟو ﻼﻴﻠﻗ ﻚﻣﺎﻨﻣ ﻲﻓ ﷲا ﻢﻬﻜﻳﺮﻳ ذإ<br />

روﺪﺼﻟا تاﺬﺑ ﻢﻴﻠﻋ ﻪﻧإ ﻢﻠﺳ<br />

Allah ya nuna maka abokan gaba kadan a mafarkin ka, da ya nuna maka yawan<br />

su da kun tsorata kuma da kun yi jayayya a tsakanin ku dangane da lamarin, sai<br />

Allah SWT ya kare ku daga samun rashin jituwa. Allah ya san abubuwan da suke<br />

a zukatan ku"<br />

Koda yake abokan gaba suna da yawa, Allah SWT ya nunawa Annabi su a<br />

mafarkin shi. Da Allah ya nuna mashi makiyan da yawa Annabi Muhammad<br />

SAWda ya shawarci sahabban shi da kuma ya jawao mummunan sabani gare su.<br />

Rashi jituwa ba ya da kyau a koda yaushe, kuma sabani a filin daga ba karamin<br />

bala'I ba ne, Allah sai ya kare musulmi daga wannan bala'in cikin hikima.<br />

Har-wa-yau, wani abin mamaki ya kara faruwa a lokacin yakin kamar yadda Allah<br />

SWT ya bayyana a Surat Al Anfal, aya ta 44:


نﺎ��آ اﺮ��ﻣأ ﷲا ﻲ��ﻀﻘﻴﻟ ﻢﻬﻴ��ﻋأ ﻲ��ﻓ ﻢ��ﻜﻠﻠﻘﻳ و ﻼﻴ��ﻠﻗ ﻢﻜﻨ��ﻴﻋأ ﻲ��ﻓ<br />

رﻮﻣﻷا ﻊﺟﺮﺗ ﷲا ﻰﻟإ و<strong>ﻻ</strong>ﻮﻌﻔﻣ<br />

ﻢﺘ��ﻴﻘﺘﻟا ذإ ﻮ��ﻤﻜﻳﺮﻳ ذإو<br />

" A lokacin yakin, mummunai sun ga abokan gaba kadan, haka nan abokan gabar<br />

sun ga mummunai kadan, saboda Allah ya yanke abinda zai afku, dukkan<br />

al'amura za a maida su ne ga Allah>><br />

muminai sun ga abin mamaki nan a filin daga, sun ga abokan gaba kadan sai<br />

suka sami kwarin-gwiwa. Hikimar da ta sa kafirai suka ga muminai kadan shi ne<br />

don kafiran su matso kusa a azabtar da su a filin daga.<br />

Wani abin sha'awa ya faru a lokacin yakin: Shaidan ya zo a siffar Suraqah bn<br />

Malik shugaban kabilar Banu bakr shigo cikin kafirai, ya yaudari kafirai ya nuna<br />

yana tare da su ya rika zuga su yana cewa " Duk duniya babu mai iya murkushe<br />

ku, ni ma mai taimakon ku ne. yayin da shaidan ya ga banagarorin biyu sun<br />

fuskanci juna sai ya tsere ya na cewa " Ni babu ruwa na da ku, lallai ni ina ganin<br />

abinda ba ku gani (mala'iku), ni mai tsoron Allah ne, lallai Allah mai tsananin<br />

azaba ne wannan an yi bayanin shi a Suratul anfal.<br />

Musulmi sun ci wannan yaki sai Allah SWT ya ce da su a cikin Suratul Anfal<br />

ﻪ�ﻨﻣ نﻮ�ﻨﻣﺆﻤﻟا ﻲ�ﻠﺒﻴﻟو ﻰﻣر ﷲا ﻦﻜﻟو ﺖﻴﻣر ذإ ﺖﻴﻣر ﺎﻣو , ﻢﻬﻠﺘﻗ ﷲا ﻦﻜﻟو ﻢهﻮﻠﺘﻘﺗ ﻢﻠﻓ<br />

ﻢﻴﻠﻋ ﻊﻴﻤﺳ ﷲا نإ<br />

ﺎﻨﺴﺣ ءﻼﺑ<br />

" Ku musulmi ba kune ku ka kashe su ba, Allah ne ya kashe su. Kuma kai<br />

(Muhammad SAW) a lokacin da ka jefe su ba kai ne ka same su ba, Allah ne ya<br />

same su. Lallai Allah mai ji ne kuma mai gani ne"<br />

Allah yana cewa Annabi Muhammad SAW da sahabban sa, kada su yi alfahari don<br />

sun ci nasara a yakin. Nasara tana zuwa ne daga Allah kadai. Allah yana tuna<br />

mana yayin da Annabi Muhammad SAW ya dauki kasa da duwatsu a hannun shi<br />

ya watsawa abokan gaba sai ta koma guguwa. Wannan guguwa ta shiga cikin<br />

idanun abokan gaba kuma ta sanya dole suka tsere, kamar yadda kasar nan da<br />

ya jimka ta canza zuwa guguwa da ikon Allah, haka nan ma cin nasarar ya zo ne<br />

da ikon Allah SWT.<br />

Kusa da karshen yakin, sai musulmi suka kasa kan su uku, kashi daya su ka bi<br />

kafarai da suka tsere don kada su dawo, kashi na biyu kuma suka debi<br />

kayayyakin da aka zubar a filin daga, wadannan musulmi da suke talakawa ne<br />

sun yi matukar farin ciki da wannan kayayyakin abokan gaba da suke mawadata,<br />

kashi na uku kuma suka tsaya tare da Annabi Muhammad SAW domin kada wasu<br />

kafirai suyi sumame su far mashi. To akwai matsala babba da ta faru a wajen<br />

yadda za a raba ganimar. Wannan kashin da syuka tattara kayan suna ikirarin na<br />

su ne, domin su ne suka tattara. Kashi na farko su ka ce sai dai a raba da su,


domin sune suka kawo damar da aka tattara kayan. Kashi na uku suma suke ce<br />

ai suna da kaso domin sune suka yi aiki mafi muhimmanci na kare Annabi<br />

Muhammad SAW.<br />

Kamar yadda aka samo daga Ubbadah Bn As Saamit ya ce " an sami matukar<br />

rashin jituwa a tsakanin su har ta kai sun fara aibanta juna. A lokacin babu wani<br />

umarni ta yadda za a raba wanan ganima. Al'ummai da suka shude ba a basu<br />

damar su yi amfani da ganima ba, sai dai su tara su a wuri daya, idan wata wuta<br />

ta zo ta kona su to alama ce ta cewa an karbi wannan jihadi na su.<br />

Allah SWT ya saukar da cikakken bayani ga Annabi Muhammad SAW akan yadda<br />

za a kasafta wannan ganima a cikin Suratul Anfal. Sa'adda sahabban manzon<br />

Allah SAW suka sami labarin wannan shiriya sai dukkan sabanin da suka samu ya<br />

gushe. Sai dukkan ganimar aka raba ta ga dukkan wadanda suka halarcin yakin<br />

kamar yadda Allah SWT ya tsara. Wannan rahama ce daga Allah SWT ga al'umar<br />

Annabi Muhammad SAW da ya basu alfarma da kuma matsayin yin amfani da<br />

dukiyar ganima. Kuma ya koya mana yadda sahabban Annabi Muhammad SAW<br />

suke a hade suna gaggawar bin umarnin Allah SWT.<br />

Kamar yadda wasu masana tarihi da ba musulmi ba su ka fadi, yakin Badar shine<br />

yaki mafi muhimmanci a tarihin dan Adam baki daya, wannan kuma shine ya<br />

samar da dawwamammen tasiri ga tarihin dan Adam.<br />

Mun bi abubuwan mamaki da suka faru a yakin Badar ta yadda taimakon Allah ya<br />

zowa musulmi da suka mika wuya.<br />

Wani mawakin Urdu ya ce " Idan da za ku kawo yanayi irin na Badar da mala'iku<br />

sun sake saukowa sahu-sahu sun kawo maku taimako.<br />

Ina rokon Allah SWT ya taimake mu mu bi tafarkin Annabi Muhammad SAW da<br />

sahabban shi, Ya kuma bamu nasara kamar yadda ya basu a yakin Badar, Amin.<br />

MU'UJIZOZI TARA NA ANNABI MUSA AS<br />

Mutane a zamanin annabi Musa AS ba tare da wata tababa ba suke amincewa da<br />

al'amura na tsafi. Allah SWT ya ba annabi Musa mu'ujizozi guda tara domin ya<br />

gamsar da mutanen shi akan samuwar Allah SWT da kuma cikar ikon Shi. Biyu<br />

daga cikin wadannan mu'ujizozi sanannu ne, sauran bakwai din kuwa ana<br />

mancewa da su.<br />

Kafin mu shiga mu fara bayani a kan wannan al'murra, za mu banbance tsakanin<br />

mu'ujiza da tsafi.<br />

Mu'ujiza wata irin baiwa ce ta musamman wanda wani mahaluki ba zai iya yin ta<br />

ba. Allah SWT yana bad wannan damar ta hannun zababun manzannin Shi.<br />

Sauran alamomin mu'ujiza sune :


Mutumen dake nuna mu'ujiza a koda yaushe mutane ne masu halaye masu<br />

kyawu, kuma ba su nuna mu'ujiza domin su yi wasa da mutane.<br />

Annabawa suna gwada mu'ujiza wadda Allah SWT ya basu, umarni nuna<br />

mu'ujiza yana ga Allah SWT Shin kadai.<br />

Mu'ujiza tana gwadawa karara cewa akwai wani mai iko da ya sanya wannan<br />

abubuwa suke faruwa.<br />

Zababbun manzannin basu ikirarin cewa wannan mu'ujiza saboda wata baiwar<br />

suce ta musamman. Sun yi imani cewa Allah SWT ya yarda wannan ta kasance<br />

domin ya gwada cewa Allah na nan da ikon Shi.<br />

Ba yaudara bace da ake yiwa yan kallo wadda za su gani a matsayin wani abu da<br />

ya wuce tunanin su.<br />

Mu'ujiza kowa ma yana iya kallon ta ba wani sashe ba na yan kallo kadai kamar<br />

yadda tsafi yake.<br />

Annabawa basu gwada alfahari da wannan baiwa da Allah ya basu.<br />

Annabawa basu rokon a basu lada ko kudi ko kuma su yi wani suna.<br />

A bangare guda, tsafi siddabaru ne wanda wasu mutane da ke da mummunan<br />

hali suke aikatawa. Rayuwar su duka bata da kyawu. Su kuwa annabawa ko da<br />

makiyan su sun amince cewa su mutanen kirki ne.<br />

Tsafi wani siddabaru ne a fili wanda ke iya kuskurewa nan-da-nan. A dayan<br />

hannu, mu'ujiza wani al'amari ne na Allah. A misali, Allah SWT ya ce da Annabi<br />

Muhammad SAW<br />

ﻰﻣر ﻦﻜﻤﻟو ﺖﻴﻣر ذإ ﺖﻴﻣر ﺎﻣو<br />

" Ba kai ka yi jifa (da jimkin kasa) ba a yakin Badar, Allah ne yayi (jifar), suratul<br />

anfal 17.<br />

Wannan jimkin kasa a hannu ya koma gagarumar guguwa da umarnin Allah,<br />

wannan ya rikitar da abokan gaba. Wannan guguwa ita ta kawo murkushewar<br />

kafirai daga musulmi yan kadan.<br />

Tsafi mafi yawa ana yin shine domin kudi ko suna.<br />

Ana yin tsafi domin a kawo matsala a tsakanin mutane har ma tsakanin miji da<br />

mata. Yana kawo burgewa, amma idan aka sami akasi yana zamewa hadarin<br />

gaske.<br />

Yanzu zamu koma a kan karamomin annabi Musa AS. Duk lokacin da annabi<br />

Musa AS ya fiddo hannu daga cikin mayafin shi sai ka gan fari kal, kuma ba tare<br />

da wata cuta ba.<br />

Fir'auna, shugaba na wannan lokacin sai ya tattara matsafa na kasar shi, ya<br />

shirya wata gasa tsakanin su da annabi Musa AS. Matsafan su ka tambayi annabi<br />

Musa AS mu zamu fara gwada tsafin mu ko kuma kai za ka fara gwada naka, sai<br />

annabi Musa AS yace " ku fara"


Matsafan nan suka jefa igiya a kasa sai ta zamewa yan kallo macizai. Sai annabi<br />

Musa AS ya jefa sandar shi a kasa. Ba wai sandar ta koma maciji bane kawai, a'a,<br />

har ma sai da ta cinye igiyoyin matsafan nan wanda wannan shi ya kawo faduwar<br />

fir'auna.<br />

Gamsuwa da wannan karamomi guda biyu ya sa wasu da suka dade a cikin kafirci<br />

suka musulunta.<br />

Fir'auna ya cewa wadannan wanda suka musulunta:<br />

نﻮﺒﻠﻘﻨﻣ ﺎﻨﺑر ﻰﻟإ ﺎﻧإ ﺁﻮﻟﺎﻗ , ﻦﻴﻌﻤﺟأ ﻢﻜﻨﺒﻠﺻﻷ ﻢﺛو فﻼﺧ ﻦﻣ ﻢﻜﻠﺟرأ و ﻢﻜﻳﺪﻳأ ﻦﻌﻄﻗﻷ<br />

" Zan sassare maku hannuwa da kafafu da-ban-da-ban, sai musulman suka ce "<br />

Ba damuwa! Ai daman za mu mutu mu koma ga Allah"<br />

Sai wadannan sababbin shiga musulunci suka yi kyakykyawar addu'a. suratul<br />

A'raaf, aya ta 126:<br />

ﻦﻴﻤﻠﺴﻣ ﺎﻨﻓﻮﺗ و اﺮﺒﺻ ﺎﻨﻴﻠﻋ غﺮﻓأ ﺂﻨﺑر<br />

" Ya Allah ka kara mana hakuri, kuma ka dauki ran mu muna musulmi"<br />

annabi Musa AS ya kwashe shekara ashirin yana wa'azi ga kafirai na Masar.<br />

Kafirai sun karya alkawarin su daya bayan daya, suka ci gaba da muzgunawa da<br />

azabtar da wanda suka yi Imani. Allah SWT ya aiko da ayoyi wadanda za su<br />

farkar da Fir'auna da mutanen shi, wadannan ayoyi an yi bayanin su a takaice a<br />

nan kasa:<br />

mutanen Fir'auna sun fuskanci fari na tsawon shekaru babu kayan lambu.<br />

Fir'auna da mutanen shi suka yiwa annabi Musa AS alkawali :idan Ubangijin shi<br />

ya ye masu wannan wahala za su bi tafarkin Allah SWT. Annabi Musa AS yayi<br />

addu'a wannan fari da rashin kayan lambu ya gushe, amma kafirai suka karya<br />

alkawarin su suka ce sai ta wuce wani dan lokaci.<br />

Allah SWT ya aikio masu da ambaliyar ruwa domin ya ladabtar da su. Kafirai suka<br />

yi alkawarin cewa da zarar ya tsaya za su karbi musulunci. annabi Musa AS ya yi<br />

addu'a Allah ya tsaida ruwan. Wannan ruwa mai yaaewa sai ya kasance an sami<br />

amfani mai kyau. Ganin wannan amfanin gona yayi kyau kwarai sai kafirai suka ji<br />

hankalin su ya kwanta, don haka, ba su canza komai ba a kan alkawarin da su ka<br />

yiwa annabi Musa AS.<br />

Allah SWT ya aiko da fara ta zo ta cinye abincin da yake a tsaye. A haka amfanin<br />

gonar da ya sanya kafirai murna, yanzu a kan idon su ya bace. Har-wa-yau, su ka<br />

rokon annabi Musa AS ya roka masu Allah ya raba su da wannan bala'i. suka ce<br />

wa annabi Musa AS " Wannan karon dai ba za mu karya alkawarin mu ba. annabi<br />

Musa AS ya yi roko ga Allah, sai ba a sake ganin fara ba, amfani ya farfardo. D di<br />

mutanen nan suka suka ga suna da abinci dankare da gidajen su, har-wa-yau, sai<br />

suka manta da alkawalin su.


A lokacin na gaba si Allah ya aiko masu da kwari suna cinye abincin da aka boye,<br />

kuma suka sake zuwa wajen annabi Musa AS da dai alkawalin da suka saba.<br />

annabi Musa AS ya yi hakuri ya sake yin addu'a aka cire masu ladabtarwar da aka<br />

yi masu. Sai suka ji ai suna da abinci mai yawa da zasu dafa su ci su more<br />

rayuwa, ba su bukatar Allah SWT sam.<br />

Allah SWT ya azabtar da su ta hanyar aiko da kwaddi a wannan kasar. Kwaduna a<br />

ko ina, a gidaje, a tukunyar abinci, a dakin ajiyar abinci, da kuma cikin ruwan da<br />

za su sha. Kafirai su ka yi kuka babu mataimaki. Sai suka rokin annabi Musa AS<br />

yayi addu'a sun yi alkawalin za su musulunta da zaran sun fita daga cikin wannan<br />

matsala. Annabi Musa AS mai zuicya mai tausayi yayi addu'a Allah ya cire<br />

kwadunan. Har-wa-yau, kafirai suka sake karya alkawalin su, sai ma suka kara<br />

bijirewa, sai suka ce lalli Musa shahararren matsafi ne".<br />

Allah SWT ya sake turo masu wani bala'in na jini. Idan suka dauko ruwa daga<br />

rijiya sai ya koma jini. Duk wani abincin su ya cika da jini. Idan suka yi kokarin<br />

yin girkin abinci sai sai ya koma jini. Abin mamaki, mabiya annabi Musa AS su an<br />

kebe su daga wannan, yana faruwa ne kadai a gidajen kafira. Bugo da kari, idan<br />

kafiri ya roko ruwa daga gidan mumini, sai ya koma jini da zaran za su yi amfani<br />

dashi.<br />

Sai mutanen Fir'auna su ka hanzarto zuwa wajen annabi Musa AS da suka karya<br />

bayan da aka raba su da akubar, shine yasa Allah ya ce :<br />

"su masu girman kai ne kuma manyan masu laifin ne a ko wane lokaci"<br />

Yanzu kafirai suka hadu da wata irin annoba ta agana. A kiyasi, mutane 70,000<br />

ne suka mutu. Kuma suka sake rokon annabi Musa AS yayi masu addu'a. babu<br />

makawa, wannan lokaci za su bi tafarkin Allah SWT idan aka kauda masu wanna<br />

bakin-ciki.<br />

Ba wai sun karya sun karya alkawalin su ba ne kadai, har-wa-yau, suna zargin<br />

wannan bala'i nasu ya faru ne a dalilin kasancewar annabi Musa a cikin su, sai<br />

suka fidda annabi Musa AS da mutanen shi daga gidajen su, suka bisu don su<br />

kashe su. Lokacin da musulmi suka je bakin teku, Allah SWT ya raba teku domin<br />

su, suka wuce salim-alim. Fir'auna da mutanen shi cikin fushi suka bisu sai ruwa<br />

ya cinye su.<br />

Sun yi bayani cewa farin da aka ayi da kuma karanci kayan lambu sai da ya<br />

kwashe shekara bakwai. Sauran horon sun dauki sati guda guda, kuam sun sami<br />

sati uku a tsakanin su. Duk wannan tunatarwa ba ta taimake su ba su fito daga<br />

cikin duhun kin yin imani.<br />

Wannan an yi bayanin shi a cikin Suratul A'raaf, aya ra 130-133.


ﻢﻬﺗءﺂ��ﺟد اذﺈ��ﻓ , نﻮ��ﻌﺟﺮﻳ ﻢ��ﻬﻠﻌﻟ تاﺮ��ﻤﺜﻟا ﻦ��ﻣ ﺺ��ﻘﻧ و ﻦﻴﻨ��ﺴﻟﺎﺑ نﻮ��ﻋﺮﻓ لﺁ ﺂﻧﺬ��ﺧأ ﺪ��ﻘﻟو<br />

ﻢهﺮﺋﺎ�ﻃ ﺎ�ﻤﻧإ ﻵأ , ﻪ�ﻌﻣ ﻦ�ﻣو ﻰ�ﺳﻮﻤﺑ اوﺮ�ﻴﻄﻳ ﺔﺒﻴ�ﺼﻣ ﻢﻬﺒ�ﺼﺗ نإو ﻩﺬ�ه ﺎﻨﻟاﻮﻟﺎﻗ ﺔﻨﺴﺤﻟا<br />

ﺎ�ﻤﻓ ﺎ�ﻬﺑ ﺎﻧﺮﺤ�ﺴﺘﻟ ﺔ�ﻳاء ﻦ�ﻣ ﻪ�ﺑ ﺎ�ﻨﺗﺄﺗ ﺎ�ﻤﻬﻣ اﻮﻟﺎ�ﻗ و نﻮ�ﻤﻠﻌﻳ <strong>ﻻ</strong> ﻢهﺮﺜآأ ﻦﻜﻟو ﷲا ﺪﻨﻋ<br />

تﻼ��ﺼﻔﻣ تﺎ��ﻳاء مﺪ��ﻟاو ﻞ��ﻤﻘﻟا و داﺮ��ﺠﻟاو نﺎ��ﻓﻮﻄﻟا<br />

ﻢﻬﻴ��ﻠﻋ ﺎﻨﻠ��ﺳرﺄﻓ , ﻦﻴﻨﻣﺆ��ﻤﺑ ﻚ��ﻟ ﻦ��ﺤﻧ<br />

ﻦﻴﻣﺮﺠﻣ ﺎﻣﻮﻗ اﻮﻧﺎآو ضرﻷا ﻲﻓ اوﺮﺒﻜﺘﺳﺎﻓ>><br />

Hakika, azabtar da mutanen Fir'auna ta hanyar shekarun fari da karancin 'ya'yan<br />

itatuwa da fatan za su dawo ga Allah"<br />

Amma idan wani abu mai kyau ya zo masu sai su ce "wannan shine namu", idan<br />

wani abin sharri ya same su sai su danganta shi da Musa da da mutanen shi. Ka<br />

sani! Sharrin da ya ke bibiyar su daga wurin Allah yake, amma da yawa daga<br />

cikin su ba su san haka ba"<br />

Suka ce (wa annabi Musa AS) duk wani wata aya da zaka zo mana da ita don ka<br />

tsafe mu da ita to mu fa ba za mu yi imani da kai ba"<br />

Sai muka aiko masu da ambaliyar ruwa da fara, da kwarkwata da kwaduna da<br />

jini, a matsayin ayoyi, amma sai su ka kasance masu girman kai suka kasance<br />

'yan ta'adda "<br />

A kan wannan, muna iya yanke hukunci / samun fa'idoji daga wannan bayani. :<br />

* Mutane nan-da-nan suke mantawa da Allah SWT idan suna cikin wadata duk da<br />

cewa ya kamata kwanciyar hankali ta kasance karin godiya ga Allah SWT. Abin<br />

takaici, mafi yawan mu abin ba haka yake ba. Misali, duk da yadda aka bamu<br />

kayan more rayuwa da jin dadi, amma kadan ne daga cikin mu suke zuwa<br />

masallaci a koda yaushe.<br />

* Allah yana son ya gwada shiriya har ga masu aikata zunubai ko da yaushe.<br />

* Allah SWT ya na ya yafe zunubai a ko da yaushe.<br />

* Annabawa suna da wani irin hakuri da sanin ya-kamata, shine ya sa Allah SWT<br />

ya zabe su.<br />

Wadanda suka sami shiriya sai su dauka cewa sun yi sa'a kuma su godewa Allah<br />

SWT.<br />

Muma akwai wata mu'ujiza a tare da mu wadda bata karewa- shine Al qur'ani mai<br />

girma. Sai mu bi shiriyar Al qur'ani ko mun sami nasara a rayuwar mu da kuma<br />

gobe kiyama.<br />

Ina rokon Allah ya kara rahma a gare mu.


RANAR HISABI<br />

Sa'adda annabi muhammad SAW ya fara wa'azin addinin musulunci a Makka,<br />

sakon shi ya kunshi abubuwa uku kamar haka:<br />

1. Babu wani abin bautawa sai Allah SWT shi kadai. Kada ka hada Allah da<br />

komai ta ko wace hanya. Mutanen Makka ba su damu da su bautawa Allah shi<br />

kadai ba, sun fi so su hada shi da wani. A saboda haka ba su iya su yi wa manzon<br />

Allah SAW gardama da tsanani ba wajen kare ra'ayin su.<br />

2. Annabi Muhammad SAW ya ce " Ni manzon Allah ne ". mutanen Makka basa<br />

so su yarda da haka amma babu dama suce ba gaskiya ya ke fada ba, tunda<br />

mutanen sun san shi da cewa shi "Ameen" ne, wato amintacce. Don haka<br />

mutanen Makka ba su iya musunta wannan sabon aike<br />

3. Annabi Muhammad SAW yace akwai wata rana da za ta zo, kuma mutane za<br />

a saka ma su da abinda suka aikata. Za a basu lada ko kuma a yi masu azaba<br />

gwargwadon ayyukan su a ranar hisabi. Wannan shine ya ba mutanen Makka<br />

dama su karyata wannan sabon aike. Mutanen Makka suka ce da annabi<br />

Muhammad SAW, suratul Waqi'ah aya ta 47-48 :<br />

نﻮﻟوﻷا ﺎﻧءﺎﺑﺁ وأ , نﻮﺛﻮﻌﺒﻤﻟ ﺎﻧإء ﺎﻣﺎﻈﻋ و ﺎﺑاﺮﺗ<br />

نﺎآ اذإء نﻮﻟﻮﻘﻳ اﻮﻧﺎآ و<br />

(kafirai) suna cewa "shin yanzu idan mun zama kasa da kasusuwa za a tayar da<br />

mu, har ma da kakannin mu suma (za a tada su)?.<br />

Mutanen Makka ba wai suna wannan magana ba ne kawai, har ma su na kiran<br />

annabi muhammad SAW mahaukaci. Allah SWT ya basu amsa a suratul Waqi'ah,<br />

aya ta 49-56:<br />

ﻢ���ﻜﻧإ ﻢ���ﺛ مﻮ���ﻤﻠﻌﻣ مﻮ���ﻳ تﺎ���ﻘﻴﻣ ﻰ���ﻟإ نﻮ���ﻋﻮﻤﺠﻤﻟ<br />

ﻦﻳﺮ���ﺧﻵا و ﻦﻴ���ﻟوﻷا نإ ﻞ���ﻗ<br />

نﻮ�ﻄﺒﻟا ﺎ�ﻬﻨﻣ نﻮﺌﻟﺎ�ﻤﻓ مﻮ�ﻗز ﻦﻣ ﺮﺠﺷ ﻦﻣ نﻮﻠآﻵ نﻮﺑﺬﻜﻤﻟا نﻮﻟﺎﻀﻟاﺎﻬﻳأ<br />

ﻦﻳﺪﻟا مﻮﻳ ﻢﻬﻟﺰﻧ اﺬه ﻢﻴﻬﻟا بﺮﺷ نﻮﺑرﺎﺸﻓ ﻢﻴﻤﺤﻟا<br />

ﻦﻣ ﻪﻴﻠﻋ نﻮﺑرﺎﺸﻓ >><br />


ta 'Zakkuum'. Za ku cika ciki da ita. Za ku sha tafasashshen ruwa. Irin shan<br />

rakumma. Wannan shine masaukin su a ranar sakamako>>.<br />

Kalmar 'Nuzul' na nufin abinda za a sauke su da shi da zarar sun iso. Kuma<br />

kalmar 'Nuzulu hum' tana nufin farkon abinda za a yi masu. Abinda zai biyo baya<br />

ya fi tsanani.<br />

Mutanen Makka kuma sun ce, Suratul Mulk, aya ta 25:<br />

ﻦﻴﻗدﺎﺻ ﻢﺘﻨآ نإ ﺪﻋﻮﻟا اﺬه ﻰﺘﻣ نﻮﻟﻮﻘﻳو<br />

Kuma suna cewa yaushe ne wannan rana (da ake yi mana alkawali) za ta zo?<br />

Idan abinda kake fadi gaskiya ne?.<br />

Allah SWT ya basu amsa a aya ta 26:<br />

ﻦﻴﺒﻣ ﺮﻳﺬﻧ ﺎﻧأ ﺂﻤﻧإ و ﷲا ﺪﻨﻋ ﻢﻠﻌﻟا ﺎﻤﻧإ لﺎﻗ<br />

(ya Muhammad)! Ka ce da su " ilmin wannan rana ya kadaita ne a wurin Allah. Ni<br />

kawai mai gargadi ne">>.<br />

Mutanen Makka suna tambayar ranar hisabi da wasa ko da yaushe. A cikin<br />

Suratun Naba'i, aya ta 4-5 Allah SWT ya ce :<br />

نﻮﻤﻠﻌﺗ فﻮﺳ ﻼآ ﻢﺛ<br />

نﻮﻤﻠﻌﺗ فﻮﺳ ﻼآ<br />

><br />

A na nufin cewa za ku sani game da ita a lokacin mutuwa da ake kira 'sakratul<br />

maut' a Barzakhu, (wanda lokaci ne tsakanin mutuwa da ranar hisabi) kuma<br />

lallai za ku san ta idan kuka fuskanci ranar a lokacin hisabi.>><br />

A wani lokaci Allah SWT yana bada takaitacciyar amsa domin mu gane ba wani<br />

abu bane mai wuya wajen Allah SWT ya kawo wannan ranar hisabi. Surat an<br />

Naba', aya ta 6-16 tana cewa :<br />

و , ﺎﺗﺎﺒ�ﺳ ﻢﻜﻣﻮ�ﻧ ﺎ�ﻨﻠﻌﺟ و , ﺎ�ﺟاوزأ ﻢآﺎﻨﻘﻠﺧ و , ادﺎﺗوأ لﺎﺒﺠﻟا و , ادﺎﻬﻣ ضرﻷا ﻞﻌﺠﻧ ﻢﻟا<br />

ﻦ��ﻣ ﺎ��ﻨﻟﺰﻧأ و , اداﺪ��ﺷ ﺎﻌﺒ��ﺳ ﻢﻜﻗﻮ��ﻓ ﺎ��ﻨﻴﻨﺑو , ﺎ��ﺷﺎﻌﻣ رﺎ��ﻬﻟا ﺎ��ﻨﻠﻌﺟ و , ﺎ��ﺳﺎﺒﻟ ﻞ��ﻴﻠﻟا ﺎ��ﻨﻠﻌﺟ<br />

ﺎﻓﺎﻔﻟأ تﺎﻨﺟو , ﺎﺗﺎﺒﻧ و ﺎﺒﺣ ﻪﺑ جﺮﺨﻨﻟ , ﺎﺟدﺎﺠﺛ ءﺂﻣ تاﺮﺼﻌﻤﻟا,<br />

>.<br />

A nan, Allah SWT yace idan zai yi duk wadanna abubuwa da ya bayyana,mai zai<br />

hana ya iya kawo ranar hisabi? A misali, ya samar mana da barci wanda zamu<br />

sami cikakken hutu, ko da wani yana son ya kauce mashi (yin barcin) sai ya zo a


cikin rahamar Allah SWT. Bayan wannan barcin, mutum zai tashi cikin karazan da<br />

karfi. Idan Allah SWT zai ba mutum wannan haka nan daga wannan al'uma zuwa<br />

wata al'umar, me zai hana ya iya kawo ranar hisabi? Duk wannan misalai suna<br />

bukatar irin wannan bayanin. Za mu takaita domin mu yi bayanin wasu abubuwa<br />

na ranar hisabi.<br />

Annabi muhammad SAW ya kawo mana albishir da kuma gargadin azabar ranar<br />

hisabi ga wadanda basu bi shiriyar Allah SWT ba. Musulmi sun amince da ranar<br />

hisabi ko da ba su ganta ba. Allah SWT cikin rahmar shi ya yi bayanin irin<br />

abubuwan da za su wakana a ranar hisabi saboda fahimtar mu da shiryuwar mu.<br />

Da farko, bari mu ji yadda aljanna take. Allah SWT a cikin Surat Al Tur, aya ta<br />

17-20 ya ce :<br />

اﻮ�ﻠآ , ﻢﻴ�ﺤﺠﻟا باﺬﻋ ﻢﻬﺑر ﻢهﺎﻗوو , ﻢﻬﺑر ﻢهﺎﺗﺁ ﺂﻤﺑ ﻦﻴﻬآﺎﻓ ﻢﻴﻌﻧ و تﺎﻨﺟ ﻲﻓ ﻦﻴﻘﺘﻤﻟا نإ<br />

ﻦﻴﻋ رﻮﺤﺑ ﻢهﺎﻨﺟوزو ﺔﻓﻮﻔﺼﻣ رﺮﺳ ﻰﻠﻋ ﻲﻨﺌﻜﺘﻣ , نﻮﻠﻤﻌﺗ ﻢﺘﻨآ ﺎﻤﺑ ﺎﺌﻴﻨه اﻮﺑﺮﺷاو<br />

Hakika masu tsoron Allah za su kasance a cikin lambu (Al janna) suna masu farin<br />

ciki da abinda Ubangijin su ya basu, kuma Ubangijin su ya tsare daga azabar<br />

wuta. (za a ce dasu) ku ci, ku sha, ko koshi saboda abinda kuka kasance kuna<br />

aikatawa. Suna masu kishingida a kan gadaje na daraja wanda aka shirya su.<br />

Kuma mun aura masu 'yan mata masu kyawun idanu>><br />

Har-wa-yau, a cikin suratul Haaqqah yana cewa :<br />

><br />

><br />

Allah SWT ya sake bayani a kan mutanen da ke zaune a gidan aljanna a cikin<br />

Suratu Yasin, aya ta 55-58 :<br />

><br />


abinda suka bukata. Za a gaishe su da kalmar 'Salam' daga Ubangiji mai jinkai.>><br />

kamar yadda wannan aya ta nuna, idan mutanen gidan aljanna suka sami<br />

kowane irin karimci daga wurin Allah SWT, Allah zai tambaye su " Ya ku bayi na<br />

masu biyayya me kuma kuke so ?" 'Yan aljanna sai su ce " Ya Allah mun gode<br />

maka, mun sami komi" Allah SWT sai ya ce dasu "Bari in baku wani abu wanda<br />

duk ya fi karimcin da kuka samu". A wannan lokaci sai a girmama su cikin jin<br />

dadi su ga Allah SWT kuma Allah SWT sai ya gaishe su da 'salam'.<br />

Har-wa-yau, Allah SWT ya yi bayanin abubuwan da za su faru a ranar hisabi da<br />

azabar da za a yi wa wadanda suka fandare. Misali, a cikin Surat al Mulk, aya ta<br />

6-10 Allah SWT ya ce:<br />

ﺮﻴﺼﻤﻟا ﺲﺌﺑ و ﻢﻨﻬﺟ باﺬﻋ ﻢﻬﺑﺮﺑ اوﺮﻔآ ﻦﻳﺬﻠﻟ و,<br />


MATSAYI DA HAKKOKIN NA-MIJI DA MACE A MUSULUNCI<br />

Allah SWT ya ce a cikin surat An Nisa'i aya t a32:<br />

" kada ku yi gurin samun abinda Allah SWT ya fifita sashen ku a akan sashe da<br />

shi. Maza suna da ladar abinda suka yi, (haka nan ma) mata suna da ladar<br />

abinda suka yi. Allah masani da dukkan komi".<br />

Wajibi ne fahimtar wannan ayar don sanin ka'idoji da hakkokin mazaje da mataye<br />

a musulunci. Dalilin da suka sanya aka saukar da wannan ayar yana da bansha'awa.<br />

Ummu Salama RA matar annabi Muhammad SAW ta tambayi annabi<br />

SAW " tunda mata suna samun rabin abinda maza suke samu a gado, ke nan za a<br />

bamu rabin ladar ayyukan mu na gari idan aka kwatanta da maza?" ba wai tana<br />

so ta kawo rudani a kan abinda ake ba maza bane, a'a, ta yi tambayar ne saboda<br />

ta sami ilmi. Wadansu mata ma cewa su ke dama a ce su maza ne da sun shiga<br />

jihadi domin su sami lada a wurin Allah SWT.<br />

Duk amsoshin wadannan tambayoyi suna kumshe ne a cikin wannan aya. Allah<br />

SWT yana cewa da Ummu Salama da daukacin musulmi, kada su kwaikwayi wasu<br />

da Alla SWT ya daukaka su a kan su. Bari mu kara kawo misali. Allah SWT ya<br />

halicci wasu gajeru, wasu dogaye, wasu kuma masu kyawun gaske. Idan Allah<br />

SWT ya sa wani mutum abin sha'awa ba zai iya kame kan shi ba, sai ma ya kara<br />

samun damar tafka sabo. Amma sai Allah ya kare shi daga yin sabo ta kin maida<br />

shi mai kyau. Wadansu mutane kuma talakawa ne, wadansu kuwa samun duniyar<br />

su kadan ne. Allah ya sani idan ya maida su masu arziki ko wani matsayi na<br />

duniya wanda ya fi nasu, da ba za su yi adalci ba. Haka nan Allah SWT ya zabi<br />

wani fili domin ayi masallaci a cikin garin. Wannan fili ya fi duk sauran wani fili da<br />

yake a cikin garin daraja. Mana yin sallah (tahiyyatyl masjid) duk lokacin da<br />

muka shiga masallacin don mu nuna girmamawar muga wannan sama da duk<br />

sauran wuraren da ke cikin garin. Za mu yi mamakin yadda Allah SWT ya zabi<br />

birnin Makka a cikin hamada aka gina dakin Allah, wanda shine wuri mafi daraja a<br />

nan duniya. A nan muna iya cewa Allah SWT shine masani, akwai hikima wajen<br />

sanya wani abu ya dara wani wanda ya zarce fahimtar mu. Fifiko tsakanin wani<br />

da wani ba wani abu bane na son kai kuma abu ne da ya wuce iyawar mu. Allah<br />

SWT yana bada baiwar sa ne ga wanda ya so. Kuma Allah SWT ya fifita wasu<br />

manzanni a kan wasu ta hanyoyi da dama. Allah SWT yace a cikin Surat Al<br />

Baqarah, aya ta 253:<br />

"Mun fifita wasu manzannin akan wasu".<br />

Da wannan takaitaccen bayani, a bayyane yake cewa duk abinda Allah SWT ya<br />

bamu sai mu yi farin cikin da shi. Idan mace aka bata matsayi irin na na-miji ba


za ta iya cika wannan matsayi ba kamar yadda ya kamata. Allah SWT ya amsawa<br />

Umm Salama RTA da sauran mata babu rabin lada ga mata idan aka kwatanta da<br />

maza. Maza da mata za a basu lada dai-dai a bisa ayyukan su masu kyau. Ayoyi<br />

da dama a cikin Al qur'ani mai girma sun yi bayanin hakan. Misali, Allah SWT<br />

yace a Surat Gaafir ko Mu'min, aya ta 40:<br />

" Duk wanda ya aikata aiki na-gari na-miji ne ko mace, wadannan sune za su<br />

shiga aljanna ana azurta su a cikin ta ba tare da lissafi ba"<br />

Fitattun mata kamar Umm Ammarah Al ansariyya da Asma' Bint Umais, da sun<br />

nuna damuwar su ga annabi Muhammad SAW kamar yadda ya zo a cikin 'Tirmizi',<br />

sun ce yaya mafi yawan lokaci Allah SWT ya na maganar maza kai tsaye, muna<br />

tunanin anya mata ma suna da irin wadannan alkawulla. Sai Allah SWT ya saukar<br />

da a cikin Surat Al Ahzaab, aya ta 35:<br />

"hakika musulmai maza da musulmai mata, masu imani maza da masu imani<br />

mata, maza da mata masu tawali'u, maza da mata masu gaskiya, maza da mata<br />

masu hakuri, maza da mata masu yin sadaka, maza da mata masu yin azumi,<br />

maza da mata masu kare al'aurar su (daga zina), maza da mata masu ambaton<br />

Allah, Allah yayi masu tanadin gafara da lada mai girma".<br />

A nan, mata suna da dama daya da lada kamar maza a musulunci. Mutane suna<br />

aikata laifuffuka da zunubbai a lokacin da basu bi wannan shiriyar ta Allah ba.<br />

Wadansu suna yin sata domin suma su yi arziki, wasu ma sai su kashe wasu<br />

domin su mallake dukiyar su. Shiriyar Allah ta tafiyar da irin wannan tunani na<br />

Hassada da hali na ta'addanci. Da mutane suna farin ciki da kuma wadatuwa da<br />

abinda Allah ya basu da basu aikata ta'addanci ba. Muna sane cewa wasu<br />

mutanen masu arziki ne sosai, wadansu kuma suna da tarin ilmi da gaske kuma<br />

sun yi fice. An yarje mana mu roki Allah ya bamu wannan ta hanyar rahmar Shi.<br />

Zai bamu idan yana da kyau a gare mu, tunda Ya san komi.<br />

Idan muka fahimci ayar da ta gabata, da cikin sauki zamu ji dadin sanin hakkokin<br />

dake a kan maza da kuma mata a musulnci. Kamar yadda ya zo a cikin Surat An<br />

Nisa', ya ta 34:<br />

" Maza sune masu karewa da kuma jibintar mata, saboda Allah ya fifita dayan<br />

sashen akan dayan, saboda (su maza) suna ciyarwa daga dukiyoyin su (domin su<br />

dauki dawainiyar matan). Saboda haka, mace ta gari itace mai biyayya ga Allah<br />

da kuma mijin ta, kuma tana tsarewa idan mijin ta baya nan abinda Allah ya<br />

umarce ta ta tsare, (misali, mutuncin su da kuma dukiyoyin mijin su)".<br />

A nan ba ana nufin ba maza su kasance masu kama-karya akan mata.<br />

Za mu kawo wadansu ayoyi a alqur'ani mai girma domin mu gane ma'anar ta.<br />

Allah SWT yace a aya ta 19 a surat An Nisa':<br />

" Ku zauna da su a cikin kyautatawa"


Haka kuma a Surat Al Baqarah, aya ta 228, Allah SWT yace :<br />

"Mata suna da hakki a kan maza kamar yadda su ma maza suke da hakkin a kan<br />

mata.<br />

A aya ta 233 a Surat Al baqarah, Allah SWT ya ce:<br />

"Ku shawarci matan ku a kan abubuwan da suka jibinci rayuwar gidan ku"<br />

Tuntuba abu ne mai matukar muhimmancia rayuwar musulmi.<br />

A bisa ga haka, mazaje ba wai kawai za su shawarci matan su bane, su ma zauna<br />

da su a mutunce kuma su ba su damar su. Bayan sun yi wannan abu mai<br />

muhimmanci sai su rinka yanke shawara daya. Hakika, maza sune su ke daukar<br />

babban nauyi, idan su ka yi son-kai ko suka yi abinda bai dace ba to zai dawo<br />

masu a rayuwar su ta gobe kiyama. A wata fadar kuma su maza sune masu<br />

hakkoki da Karin jibintar al'amura. Idan aka maida mace kamar na-miji, ba za tai<br />

ya jibintar wadansu al'amura masu wahala ba. A nan mata ba za su so su<br />

kasance kamar maza ba, haka nan kuma maza. Kowa Allah ya bashi matsayin da<br />

ya dace da shi. Na-miji zai gudanar da hakkokin shi ta hanyar da ta fi dacewa<br />

haka nan ma mace za ta gudanar da na ta.<br />

Bari mu fahinci hikimar baiwa mace rabin abinda na-miji ke samu a gado. Dun<br />

abinda mace ta samu na ta ne, tana da damar ajiye shi don karon kan ta, ba ma<br />

za ta kashe ko kwabo domin gudanar da wani sha'ani na gidan ta ba. Idan ita<br />

daya ce (ba ta da aure) mahaifin ta zai dauki nauyin rayuwar ta, idan kuma<br />

matar aure ce mijin ta ne zai jibinci al'amuran ta kome arzikin ta. Idan kuma<br />

bazawara ce tana da 'ya'ya ko kuma a'a sai ta koma wajen mahaifin ta ya dauki<br />

dawainiyar ta idan ya zama tilas. A koda yaushe dai, akwai namiji da zai taimake<br />

ta. Idan kuma namiji ya karbi ninkin abinda mace ta samu ba zai ajiye domin kan<br />

shi ba, dole ya kasha shi saboda iyalan shi, matar shi ko 'ya'yan shi da kuma<br />

sauran dangi. Akan haka muna iya cewa mace tafi namiji cin moriyar gadon duk<br />

da cewa ta samu rabin gadon ne idan aka kwatanta na namiji. Wannan shine<br />

fifikon da mata suka samu a musulunci.<br />

Yana da muhimmanci mu duba yadda rayuwar mata ta kasance kafin zuwan<br />

musulunci. Laarabawa sun kasance suna binne 'ya'yan su mata da ran su, kuma<br />

ana daure gashin mace a jikin rakumi a sanya rakumin ya ruga. Wannan shine<br />

rayuwar larabawa a wancan lokacin. Mata a wannan zamanin ba a barin su su<br />

sami wani abin kirkia gado. Musulunci ba wai kawai ya baiwa mata dama daya<br />

ne, a'a, ya ma ba su damar mallaka da kuma cin gado.<br />

Za mu kuma duba alamomin mace ta gari. Allah SWT ya ce a cikin Al qur'ani a<br />

cikin Surat An Nisa', aya ta 34:


"Mace ta gari itace mai biyayya ga Allah da kuma mijin ta, kuma tana tsarewa<br />

idan mijin ta baya nan abinda Allah ya umarce ta ta tsare, (misali, mutuncin su<br />

da kuma dukiyoyin mijin ta)".<br />

Annabi Muhammad SAW ya ce mace ta gari ita ce wadda idan miinta ya gan ta<br />

sai hankalin shi ya kwanta, idan ya umar ce ta sai ta yi mashi biyayya, kuma tana<br />

tsare kan ta da kuma dukiyar sa idan baya nan.<br />

A nan, mace ta gari dole ne ta bi dokokin dokokin Allah, kuma su yarda a zuciyar<br />

su da dokokin da ya sanya ma su na yin biyayya ga mazan su a matsayin<br />

shuwagabannin su a kan komi. Kuma an umarce su da su tsare kan su daga<br />

shaidan wanda karara makiyin mu ne, kuma su kare dukiyoyi. Bai kamata su kai<br />

wata ziyara sai da izinin mijin su. Har-wa-yau, dole ne su tsare muhimman<br />

kadarorin mijin su kamar 'ya'ya. A kuma wata fadar dole ne su ilmantar da<br />

tarbiyyantar da 'ya'yan ta fuskar musuluncin su, cusa masu kyakykyawan hali.<br />

Wadannan abubuwa suna da nauyi kwarai. Allah yayi alkawali a wannan ayar<br />

cewa zai taimake su ya tallafa masu domin su sauke wannan matukar sun yi<br />

gaskiya wajen neman yin hakan.<br />

Musulunci ya tsara yadda za ladabtar da mata a cikin Surat An Nisa', aya ta 34,<br />

Allah SWT ya ce :<br />

"wadannan matan da kuke tsoron bijirewar su, sai ku yi masu nasiha sannan ku<br />

kaurace masu a wajen kwanciya, daga karshe ku buge su. Amma idan sun dawo<br />

da biyayya, kada ku nuna masu fushin ku. Lallai Allah shine madaukaki mai<br />

girma".<br />

A nan, muna ganin hanyoyin da za a bi a gyara al'amurra a kowane mataki. Da<br />

farko za a bi hanyar shawarwari na cikin gida sannan kuma sai shawrwari daga<br />

waje. A bin takaici, musulmi a fadin duniya sun kauda kai daga wadannan<br />

muhimman matakai, sun bari sai da matsaloli su ka taru sun wuce a yi maganin<br />

su. Musulmi su na jin tsoron ace suna da matsala ta wajen sanin halayyar<br />

mutane, don haka sai suke gujewa neman shawarwari. Gaskiya ne kowane irin<br />

mutum yana bukatar shawarar wani a rayuwar shi. Ina rokon mu da mubi<br />

wadannan hanyoyi da aka tsara da kyau da kuma sanin ya-kamata a duk lokacin<br />

da wata matsala ta taso.<br />

Abu na biyu, ku kaurace masu daga gadaje. Wannan ba yana nufin a matsawa<br />

mace ta bar gida ba, haka nan kuma, mace kada kawai don karn kan ta tafi gida<br />

saboda wannan sabani. Kamar yadda wasu malamai su ka ce : kada su raba<br />

dakin kwanciya, an unmarce su kawai su kauracewa juna a akan gado. Hikimar<br />

yin haka shine: yin hakan abu ne da ke da wuyar daurewa. Wannan mawuyacin<br />

hali yana iya canja masu ra'ayi su koma yadda suke.


Abu na uku ; an anincewa na-miji ya bugi matar shi domin ya ladabtar da ita. Ba<br />

wai ana nufin ya ware damtse ya naushe ta a ido ko a fuska ko a wasu bangarori<br />

na jikin ta ba. Kamar yadda wasu suka ce : ka dan buge ta da buroshin gugar<br />

hakori ko kuma wani abu ba mai nauyi ba ka ladabtar da ita.<br />

Annabi Muhammad SAW yace " Namiji na kirki ba zai ladabtar da matar shi ba da<br />

duka"<br />

Muna iya sani cewa babu wani annabi da yake bugon matar shi, har da annabi Lut<br />

AS.<br />

Annabi Muhammad SAW ya ce wanda suke kyautatawa matan su za su kasance<br />

kusa da ni a cikin aljanna.<br />

Allah ya bamu shawara " Idan suka dawo suna bin umarnin ku kar ku yi<br />

maganganu gatsai-gatsai gare su, wannan zai tunatar da su rashi jituwa ta baya.<br />

Na miji an sake bashi umarni daga Allah SWT kada ya manta Allah SWT shine<br />

babba kuma madaukaki. Shine ya maida shi shugaba a kan matar shi kuma<br />

namiji zai kasance mai kididdiga a kan ayyukan ayyukan shi gare shi. Saboda<br />

haka, dole ya yi mata adalci a kan wadannan matakai.<br />

Allah SWT ya sake cewa a cikin surat An Nisa', aya ta 35:<br />

Idan kuna jin tsoron sabani a tsakanin su (miji da mata) ku sanya masu sulhu a<br />

tsakanin su, daya daga dangin shi daya kuma daga dangin ta, idan suna nufin<br />

gyara Allah zai daidaita tsakanin su ma'auratan. Hakika Allah ya kasance masani,<br />

ya san komi da komi".<br />

A nan, idan sabani ya abku tsakanin miji da matar shi kuma ba a warware shi ba,<br />

sai mu sanya masu sulhu a tsakanin daya daga kowane bangare. A nan Allah yayi<br />

kyakykyawan alkawali. Allah ya ce idan dukkan su suka kawo shiriya a tsakanin<br />

su Allah zai tabbatar da haka tunda abinda ke a zuciyar kowa. Malamai su ka ce<br />

"wannan Magana tana tana nufin miji da matar har ma da masu shiga tsakani na<br />

dukkan bangarorin. A nan idan dukkan su hudun suna neman gyara a kan<br />

wanann ma'ala to Allah yayi alkawalin zai kawo ta, tunda shi masani ne game da<br />

niyyar mu.<br />

Musulunci kuma ya bada dama bai daya ga namiji da kuma mace kuma ya tsara<br />

wasu hanyoyi da za a bi idan sabani ya abku. Kwata-kwata ba daidai bane kace<br />

mata su kasance gaba –gaba a kan gida. Maza da mata kowanne an shata mashi<br />

matsayin shi wanda ko wanne zai iya. Mata sun iya cin gado kuma su ajiye<br />

abinda su ka samu har abada.<br />

Sahabban Annabi Muhammad SAW suna tsammanin mata an basu dama da yawa<br />

kuma an daga matsayin su na kafin zuwan Musulunci. Suna ganin wadansu da<br />

aka basu a janye. A nan suka yi ta tambayar Annabi Muhammad SAW akai-akai


dangane da wahayi a kan damar da aka ba mata. Allah yace a cikin Surat An<br />

Nisa' aya ta 127:<br />

" sun tambaye ka game da ka'idojin sharia dangane da mata. Allah ya umarce ka<br />

a akan dagane da su da abinda aka karanta maku a cikin littafi dangane da<br />

marayun 'yan mata wanda baku ba bangare daga gado wanda kuke son ku aura,<br />

kuma dangane da yaran da aka zalunta kuma ku tsaya tsayin daka akan yin<br />

adalci ga marayu. Duk abinda kuka yi mai kyau Allah har abada yana sane da shi.<br />

A wata fadar, dama daya da daukakar darajar mata tana nan daram har abada a<br />

addinin Musulunci.<br />

Ina rokon Allah ya sa mu bi wannan umarni ta fuskar iyalin mu domin mu<br />

daukaka matsayin al'umar Musulmi, Amin.<br />

ZATO, SA-IDO DA GULMA<br />

Allah SWT ya ce a cikin suratul Hujuraat aya ta 12:<br />

" Ya ku wanda kuka yi imani ku daina zargi (zato) domin zargi laifin ne , kada ku<br />

rinka sa-ido, kada ku yi gulma a tsakanin ku, dayan ku yana son ya ci naman dan<br />

uwan shi da ya mutu? Ba za ku so ba , to ku ji tsoron Allah. Hakika Allah shine<br />

mai karbar tuba mai jin-kai".<br />

A nan, Allah SWT yana koya mana mutunta juna da kuma zamantakewa a<br />

ayyukan mu na yau da kullum. Za mu bisu daya bayan daya mu fara da zargi.<br />

Akwai zargi mai kyau da zargi marar kyau. Imam Abubakr Jassas ya kasa zargi<br />

gida hudu, kamar yadda yayi bayani a littafin shi ' Ahakamul qur'an'<br />

Wadannan matakai guda hudu sune : haram, wajib, mustahab, da mubah.<br />

Zargin da ba a yarda da shi ba shine mutum ya dinga cewa a ranshi " Allah zai<br />

azabtar da shi, Allah zai yi mashi akuba, yanke tsammani aka n rahama da jin<br />

kan Allah SWT. Manzon Allah SAW yace:<br />

"Ka sanya kyakykyawan fata wurin Uban gijin ka har ranar mutuwar ka"


A Hadisi Kudusi kuma, Allah SWT yace " ina yi wa bawa na a yadda ya sanya<br />

tsammani a gare ni. Misali zato wanda yake wajibi shine baka san al kibla ba,<br />

kuma babu wanda zai nuna maka a nan an baka dama ka yi amfani da abinda<br />

kake zaton daidai ne.<br />

Misali, zato na mustahabbi shine ka sa kyakykyawan tsammani ga kowane<br />

Musulmi. A nan an amince ka yi taka tsan tsan wajen huldayya ta yau da kullum<br />

ba tare da daukar wani barawo ko dan ta'adda haka nan kawai ba.<br />

Misali zato da aka amince shine idan kana kokanton baka cika raka'a uku ko hudu<br />

a salla an amince a amince ka yi amfani da abinda kake zato dai dai ne a zuciyar<br />

ka. Sauran zato haramun ne a musulunci.<br />

A yanzu bari mu duba sa-ido, ba a yarda ba kayi bincike kuma ka fallasa asirin<br />

wasu ko kuma ka ji idan wani idan yana boyewa ko kuma yana fakewa yana barci<br />

kamar sa-ido ne ga wadansu. Amma idan akwai kyaukyawa zato, wadansu zasu<br />

cutar da wani Musulm, wannan bincike ne ko sanya ido an yarda.<br />

Zamu kuma bada misalign gulma. Manzo SAW yace " Gulma itace yin zancen<br />

wani wanda idan yaji ba zai ji dadi ba.<br />

A nan ba a yarda ba ka yi zancen wani a bayan idon shi, ko da kuwa abinda ka ce<br />

din gaskiya ne. idan kuma ba gaskiya ba ne, ya zamana babban zunubi wanda<br />

ake kira Buhtan (zargin karya).<br />

Yana da kyau mu sani idan ka sami kuskuran wasu ko yin maganganu gatsegatse<br />

ko kuma muzanta wani a na kiran shi ' Lamz', a cikin Al qur'ani mai girma,<br />

Allah SWT yace a cikin Surat Al Hujraat, aya ta 11:<br />

" kar ku muzanta junan ku".<br />

A na nufin idan ka sami kuskure a wajen wasu suma zasu juyo su sami kuskure<br />

a kan ka.<br />

Abin sha'awa ga wannan ayar shine samun wasu da laifi kamar samun laifin ne<br />

ga kan ka. kamar yadda Allah yace<br />

ﻢﻜﺴﻔﻧأ اﻮﻠﺘﻘﺗ <strong>ﻻ</strong>و<br />

" kada ku kashe junan ku".<br />

Idan ka kashe wasu, kai ma za su yi kokari su kashe ka. Allah SWT ya ce a cikin<br />

Alqur'ani mai girma, Surat al Humazah 1:<br />

ةﺰﻤﻟ ةﺰﻤه ﻞﻜﻟ ﻞﻳو<br />

" Bone ya tabbata ga mai aune, mai zune (mai rada) "<br />

Bahadar Shah Zafar yace " Idan ban san kai na ba sai in dinga ganin kuskure a<br />

wajen wasu, idan kuma na duba kai na, ban ga mutumi wanda ya fi ni muni ba".


A aya ta 12 ta Surat al Huraat, Allah SWT ya bayyana karara bata sunan wani<br />

Musulmi bayan idon shi kamar cin naman dan uwan ka ne da ya mutu, wanda<br />

kowa ba ya kauna.<br />

Wannan shine mummunan zunubi ka sani idan mutum yana nan zai kare kan shi<br />

ko da yake ba kowa yake da kwarin gwiwar da zai kare kan shi ba a wannan hali,<br />

idan kuma aka bata mashi suna a bayan idon shi batancin yayi tsanani na<br />

dundundun ne. Allah SWT ya yi bayanin wannan zunde a wani yanayi da ko wane<br />

Musulmi zai kyamaci wannan mummunan laifi.<br />

Zunde ba ana yin shi da harshe bane kawai, ana yi kuma da ido, hannu da sauran<br />

kyafuce-kyaufuce, misali kwaikwayon wani gurgu domin bakanta shi. Manzon<br />

Allah SAW yace " zunde yin zina laifi", kuma an sami Karin bayani daga Manzon<br />

Allah kamar yadda Abu Sa'id da Jabir suka ce, a Timizi " Allah SWT yana<br />

gafartawa wanda yayi zina idan ya tuba, kuma Allah SWT ba zai yafewa wanda<br />

yayi gulma ba da dan uwan shi har sai wanda a ka yi da shi ya yafe mashi". A<br />

wani lokaci Manzon Allah SAW ya nuna wadansu kabarurruka guda biyu yace da<br />

sahabban Sa " Dukkan wadannan mutanen ana yi masu azaba a cikin kabari,<br />

daya daga cikin su yana gulma da mutane, dayan kuma baya kiyayewa yana<br />

fantsama fitsari a jikin shi da tufafin shi. Shine ya sa wani lokaci Manzon Allah<br />

SAW yace wa matar shi A'isha RA " Kibi a hankali da abinda kike kira da karamin<br />

zunubi", suna iya kawo mummunar azaba a kabari. A lokacin Mi'raji Annabi SAW<br />

ya ga wasu mutane wanda farautan su na jan karfe ne suna kartar fuskokin su da<br />

kirjin su, Manzon Allah SAW ya tambayi Mala'ika Jibrilu labarin su, Mala'ika Jibrilu<br />

ya amsa mashi " Ana azabtar da su domin suan cin naman mutane a rayuwar su,<br />

sun kasance suna gulma da bata sunayen mutane.<br />

An karbo daga Abu Huraira cewa Manzon Allah SAW yace " Kashe musulmi haka<br />

nan ko kwace dukiyar wasu ko bata sunan wani dan uwa Musullmi an haramta shi<br />

kwata kwata a Musulunci". (Muslim ne ya ruwaito).<br />

Har wa yau, an karbo daga Abu huraira cewa Manzon Allah SAW yace " wanda<br />

bai bar yin karya ba, Allah bai damu da kin cin abincin shi ba da sauran su a<br />

lokacin azumi.<br />

Imam Ghazali ya rubuta a cikin Ihya'u ulumid din cewa wani mutum ya kasance<br />

yana gulma da Hassan basri sai Hassan Basri ya aiko mashi da dabino kyauta, da<br />

ya sami labarin wannan zunde, Hasan basri kuma ya aika mashi da wannan<br />

sakon " Yin gulma da kake yi da ni, kana dauko ayyukan ka na alheri zuwa gare<br />

ni, sai wannan dabino bai cancanci abin kirkin da kake yi mani ba, ina fata zaka<br />

amshi wannan muhimmiyar kyauta.<br />

Ka sani fa yin gulma da yaro ko mahaukaci ko kafiri da yake zaune a kasar<br />

Musulmi ba a yarda da shi ba.


Abubuwa wadanda ba a dauke su ba a zunde ba :-<br />

1. Ka yi koke a kan azzalumin shugaba domin wanda yake da hakki ya ladabtar<br />

da azzalumin shugaba.<br />

2. Ka yi koke ga uba ko miji akan dan shi ko matar shi, wanda shine zai iya gyara<br />

masu rayuwar su.<br />

3. ka yi bayani cikakke ta yadda za a sami fatawa.<br />

4. ka yi bayani ka ceto Musulmi kada a cutar da shi ta fuskar addini.<br />

5. a yi bayani ta yadda za a sami kwararriyar tuntuba.<br />

6. ka yi bayanin manya-manyan zunubbai ga mutum da ya ke aikata wannan<br />

zunubbai a fili karara, kuma kayi alfahari da yin hakan.<br />

Ka sani fa manufa a nan bisa wannan abubuwan da aka bayyana a sama shine<br />

anbaton da aka yi an yi shi ne domin wani mashahurin abu da ake nufi ba domin<br />

a dankwafe ko bata sunan wasu ba da niya ko kuma haka nan kawai.<br />

Har way au, sauraren gulma dai dai yake da yin gulma da wani. Mafi kyau shine<br />

ka bar wajen da ake yi.<br />

Cin naman wani tuyewa ne ga damar Allah SWT da damar mutane. Domin haka<br />

dole da farko, ka nemi gafara ga wanda kayi wa, tunda Allah ba zai gafarta maka<br />

ba sai wanda ka yi da shi ya gafarta mak. Idan wanda aka yiwa ya mutu ko kuma<br />

ba a san inda yake ba, to a nan sai a biya diyya.<br />

An karbo daga Anas cewa Manzon Allah SAW yace " Diyyar cin naman wani shine<br />

ka roki Allah gafara cewa " Ya Allah ka yafe mani zunubai na da nashi".<br />

Ina rokon Allah SWT ya kare mu daga aikata mummunan zato da sa-ido da gulma<br />

(zunde), Amin.


BABBA DA KARAMIN ZUNUBI<br />

Allah SWT ya ce a cikin Surat An Nisa', aya ta 31:<br />

" Idan kuka bar babban zunubi wanda aka hane ku da aikatawa zamu barranta ku<br />

daga kananan zunubai, mu sanya ku a kykykyawan mushiga, watau aljanna".<br />

A bayyane yake daga wannan aya akwai zunubi iri biyu, karami da babba, kuma<br />

a yake alkawalin Allah SWT, idan mutum ya guji aikata manyan zunubai, zai yafe<br />

mashi kananan zunubai . muna sane wajibi ne mu aikata Fardh (abubuwan da<br />

suka wajabta a kan mu) kamar Salla, Zakka da azumi kamar yadda ya dace,<br />

kuma muna masu kauracewa babban zunubi. Barin ayyukan nan da aka wajabta<br />

to shima babban zunubi ne. A nan idan mutum ya aikata manyan zunubbai Allah<br />

SWT zai yafe mashi kananan zunuban shi.<br />

Menene zunubi?<br />

Duk abinda aka aikata sabanin yadda Allah ya ce ko umarnin Allah wannan shine<br />

zunubi, a nan babu karamin zunubi ko babban zunubi, saboda haka, idan ana<br />

yawaita kananan zunubai ba tare da wata damuwa ba zi zamana babban zunubi.<br />

Wani malami yayi bayanin matsalar kananan zunubai da babban zunubi a<br />

wadannan misalai. Yace ka kaddara harbin mu'ujizar kunama da babbar kunama,<br />

kuma ka kaddara konewa daga mu'ujizar wuta da konewa daga konewa daga<br />

giwar wuta. Dukkan su suna da zafi amma illar da babbar za ta yi ya fi matsala.<br />

Kuma dukkan zunuban nan suna da illa amma babban zunubi yafi ta'adi akan<br />

karamin zunubi. Muhammad Bn Ka'ab Karazi ya ce " Mafi kyawun bautar Allah<br />

mutum ya bar dukkan zunubbai ". Allah SWT baya karbar Sallar mutum da<br />

kullum sauran ibadu matukar wannan mutum baya barin aikata zunubbai. Haka<br />

nan kuma Fudhail Bn Ayyadh ya ce " idan mutum ya kasance yana daukar zunubi<br />

karami wadannnan zunubai za su kasance manya a idon Allah SWT".<br />

Annabi Muhammad SAW yace " idan mummuni ya aikata zunubi sai ya kasance<br />

wani bakin digo a zuciyar shi, idan ya tuba sai wannan bakin digo ya bace, idan<br />

kuma bai tuba ba sai wanann digon yayi ta girma har ya mamaye zuciyar. Allah<br />

SWT ya bayyana a cikin Alqur'ani mai girma a cikin Surat Al Mutaffifin, aya ta 14<br />

:<br />

A aha! Ba haka ba abinda su ka kasance suna aikatawa yayi tsatsa a zukatan su".<br />

Idan zuciyar ta kasance cike da tsatsa babu wata shiriya ko fadakarwa da zata<br />

ratsa zuciyar irin wadannan mutane, don haka, ba za su ba za su amfana da<br />

tunatarwa ta Alqur'ani ba. Alqur'ani ya karfafa wannan magana da dama cewa shi


Alqur'ani fadakarwa ne ga masu tsoron Allah da wankakkiyar zuciya wadda zata<br />

karbi shiriya.<br />

Bari mu fassara zunubi a haske da shiryarwa ta Alqur'ani da Sunna. Kamar yadda<br />

wadansu malamai duk wani zunubi wanda ALqu'rani ya fadi hukuncin wanda ya<br />

aikata shi ko tsinuwar Allah da aka fadi, ko gargadin wutar Jahannama wadannan<br />

an dauke su manyan zunubbai. Kamar yadda aka yi bayani a baya duk wani<br />

karamin zunubi da aka aikata ba tare da nuna wata damuwa ba, a bayyane<br />

karara yana iya kasancewa babban zunubi. Wani ya fadawa Ibn Abbas cewa<br />

manyan zunubai guda bakwi ne. sai Iban Abbas ya amsa mashi da cewa ba<br />

bakwai bane gara ma dari bakwai ne. Imam Ibn Hajjar Meccy RA yayi bayani a<br />

tsare jerin manyan bayanai da cikakken bayani a cikin littafin sa KITABUZ<br />

ZAWAJIR ya lissafa dari hudu da sittin da takwas manyan zunubbai. Tare da<br />

kebance wurin kin biyayya da umarnin Allah SWT.<br />

Yaya za a yafe karamin zunnubi ? misali yafe karamin zunubi an yi bayanin shi a<br />

Hadisi : Idan mutum ya yi alwalla, ya wanke bangarori na jikin shi, zunubin da<br />

aka aikata a bangaren jikin an wanke shi, kamar yadda busashshen ganye zai<br />

fado daga kan bushiya idan iskya kada. Misali idan muka kurkure baki zunubin da<br />

muka aikata da harshen mu an wanke shi, idan muka wanke kafafun mu, zunubin<br />

da muka aikata da taimakon kafar mu an wanke shi. Idan mutum ya tafi zuwa<br />

masallaci bayan yayi alwalla bayan yayi alwalla duk takin da yayi ya zama diyyar<br />

kananan zunubban shi. Shi babban zunubi ba a wanke shi ta hanyar alwalla ko<br />

kuma yin salla kadai, wanke babban zunubi yana faruwa ne ta hanyar tuba na<br />

gaskiya. Tuba ya kunshi abubuwa guda uku. Da farko mutum sai ya mutunta ya<br />

kuma tabbatar da aikata zunubin. Na biyu sai ya hakikance cewa ba zai sake<br />

aikata wannan laifi ba. Na uku sai yayi nadama sannan ya roki gafara. A nan,<br />

idan yana yin salla kuma yana azumi kana kuma ya sa kan shi a cikin babban<br />

zunubi, to Allah SWT ba zai yafe mashi manyan zunubai da kanana. Annabi<br />

Muhammad SWA ya fadi manya-manyan zunubbai da dama a kan wani yanayi da<br />

lokaci. Saboda haka, malamai sun yi ittifaqi ba a sanya wani kiyasi a kan dukkan<br />

manyan zunubbai. Annabi Muhammad yace " Bari in sanar da ku manyan<br />

laifuffuka guda uku: hada Allah da wani, kin biyayya ga mahaifa da kuma shaidar<br />

zur. Bukhari da Muslim ne suka ruwaito.<br />

Wani ya tambayi Annabi Muhammad SAW game da manyan zunubbai, ya amsa<br />

mashi da " Kada ka hada Allah SWT da wani". Sai ya sake tambayar shi " sai<br />

wane?", Annabi Muhammad SAW ya ce " kada ka kashe dan ka domin gudun<br />

dawainiyar ciyar da yaron da abinci". Sai ya sake tambayar shi " wane zunubi<br />

babba ne gaba? Sai Annabi Muhammad SAW ya ce " ka yi zina da matar<br />

makwabcin ka. Kamar yadda ka sani, zina babban zunubi ce, makwabcin ka yana


da hakki ka kare iyalin shi. Saboda haka, zina da matar makwbcin ka laifi guda<br />

biyu ne. (Bukhari da Muslim)<br />

Annabi Muhammad SAW ya ce " Zunubi ne babba mutum ya zagi mahaifin shi",<br />

Sahabbai suka ce " yaya za a yi mutum ya zagi mahaifan shi"? Annabi<br />

Muhammad SAW yace " Idan ka zagi iyayen wani to shima zai zagi naka iyayen.<br />

Saboda haka, zagin iyayen wani tamkar kana zagin naka iyayen ne.<br />

Annabi Muhammad SAW yace " hada Allah SWT da wani, kashe wani haka nan,<br />

cin dukiyar maraya, cin riba, gudu daga fagen fama, ka zargi mace mummuna,<br />

kin biyayya ga mahaifa, da kin girmama dakin Allah SWT dukkan wadannan<br />

zunubai ne manya.<br />

Annabi Muhammad SAW ya ce idan wani ya zargi wani ba da hakkin shi domin<br />

kawai ya muzguna mashi ko kuma ya yanke kauna daga rahmar Allah SWT ko kin<br />

bin shari'ar rabon gado, wannan suma zunubbai ne manya. Kamar yadda aka<br />

samu daga wani Hadisin hada salla guda biyu ba tare da abinda addin ya shimfida<br />

ba, wannan ma babban zunubi ne. Ya zama dole mutum ya rika yin sallah a kan<br />

lokacin ta.<br />

Wani lokaci, Annabi Muhammad SAW yace " Wannan mutum ya halaka! Har sau<br />

uku. Abu Zarr ya tambaya wanene wannan ? Annabi Muhammad SAW ya amsa :<br />

Mutum mai alfahari wanda zai saki tufafin shi su rika jan kasa, mutum da zai<br />

ciyar domin Allah SWT sannan ya rika fadawa mutane abinda ya yi, mutumen da<br />

ya ke tsoho sannan yana yin zina, mutumen da ya ke rike da babban mukami<br />

sannan yake cin amana, mutumen da yake alfahari domin Allah ya bashi 'ya'ya,<br />

ko wanda yake biyayya ga wani Imam domin samun duniya. (Muslim)<br />

Annabi Muhammad SAW yace " wadannan mutane ba su shiga aljana : wanda<br />

yake sha giya, da wanda baya biyayya ga mahaifan shi, da wanda ya kauracewa<br />

dangin shi ba tare da dalili ba, wanda yake tunatar da mutane abin da yayi na<br />

kyautatawa. Da wanda yake bokanci da wanda ba ya kokarin ya hana iyalan shi<br />

aikata wadansu abubuwa marasa kyau."<br />

Annabi Muhammad SAW yace mutumin da yake cin naman dan uwan shi ba zai<br />

shiga aljanna ba.<br />

Sahihaan.<br />

Ina rokon Allah SWT ya yafe mana zunubban mu manya da kanana, ya sany mu<br />

bi tafarkin Alqur'ani da Hadisi,Amin.


IKIRARIN MABIYA LITATTAFAI<br />

Babban abin alheri da Allah SWT ya yiwa Yan Adam shine sanya su akan hanyar<br />

shiriya. Matukar babu shiriya mutane za su dimauce su fada halaka ta hanyoyi da<br />

dama. Yahudawa da kiristoci Allah SWT ya basu baiwa ta samun shiriya ta<br />

gaskiya, amma mafi yawa daga cikin su sun yi fatali da wanna muhimmiyar dama<br />

da suka samu. Bari mu ga yadda suka nuna halayya da wannan shiriyar da<br />

Allah SWT, Surat Al Baqarah, aya 135:<br />

" sun ce ka zama bayahude ko kirista ko sami hanya madaidaiciya ! kace da su "<br />

mu mun bi addinin Ibraheem AS madaidaici kuma ba ya tare da wanda suka hada<br />

bautar Allah da wanin sa".<br />

A nan, mun gani yahudawa da kiristoci suna ikirarin su mabiyan. Annabi ibrahim<br />

AS amma ikirarin karya ne tunda Annabi Ibrahim AS bai taba hada Allah SWT da<br />

wani ba.<br />

Aya ta 40, a Suratul Baqarah Allah SWT ya ce :<br />

" Ko kace ku da Ibraheem, Isma'il, da Ishaq, Ya'qub da Al asbad su yahudawa ko<br />

kirista. Kace kun fi sani ne ko kuma Allah mafi cancanta ya sani (cewa dukkan su


Musulmai ne), to wanne ne ba akan dai dai ba ga wanda ya biyo samun tabbaci<br />

daga Allah ? ko Allah bai san abinda san abinda suke yi ba?"<br />

Allah SWT ya bayyana wannan tabbaci wanda ma'abuta littafi su ka sami, wanda<br />

a bayyane suka sami shaida, ba gara a aya ta 146 v yace :<br />

" Wadanda suka baiwa littafai (yahudawa da kiristoci) sun gane shi (Muhammad<br />

SAW) kamar yadda suke gane dan su, amma wasu bangare daga cikin su sun<br />

boye gaskiya duk da sun san ta (shima alamomin Muhammad SAW wanda aka<br />

rubuta a cikin littafin su).<br />

Karara masu ilmi daga cikin malaman su sun boye gaskiya da gangan saboda son<br />

samun duniya, duk da haka da yawa daga cikin ikirarin su mai rauni ne. A misali,<br />

ma'abuta littafai sun ce ; Suratul Baqarah, aya 111;<br />

" (sun ce) Babu wanda zai shiga aljanna sai dai wanda ya ke bayahude<br />

ko nasara, wannan abinda suke so ke nan. Kace da su (ya Muhammad)<br />

ku kawo hujjojin idan kun kasance kuna da gaskiya."<br />

Har wa yau, sun sake ikirarin, Suratul Baqarah, aya ta 150:<br />

" Su yahudawa suka ce: wuta (watau lahira a ranar tashin kiyama) ba za ta taba<br />

su ba sai na wasu 'yan kwanaki! Kace da su (ya Muahmmad) kun yi alkawali ne<br />

da Allah wanda (kuma) Allah ba zai taba alkawalin su ba? Ko kun fadi wani abu<br />

game da Allah wanda ku baku sani ba."<br />

Ikirarin ma'abuta littafi bai iya rike ruwa, kuma zai sanya wani ya fada kogin<br />

tunanin gaskiya ko dibar wannan Magana, shine Allah SWT ya ce a cikin Suratu<br />

Aal Imran, aya ta 65:<br />

" ya ku ma'abuta littafi (yahudawa da kiristoci) me yasa kuke yin jayayya akan<br />

Ibrahim bayan At Taura da Linjila ba a saukar da su ba sai bayan shi? Ko ba ku<br />

da hankali ne ?"<br />

ِAllah SWT ya sake cewa a suratu Al Imran , aya ta 68 :<br />

" Hakika , akin mutane wanda yafi can canta suyi ikirarin Ibrahim sune mutanen<br />

suka bishi, da Annabin sa Muhammadu SAW da wadanda suke yi imani, Allah<br />

shine mai kariya da taimakon mummunai."<br />

Wannan kinaya ta wadan nan mutane ma abuta littatafai ya kai awani<br />

mastayi sai Allah ya sake cewa a suratul Al Imran aya ta 72 " Wadansu bangare<br />

na cikin mutane ma'abuta littafi sun ce ku yarda dasa saifya wanda aka saukowa<br />

mummunai (musulmi) ku yi watsi da karshen rana domin su juya baya"<br />

A wata aya ta 78, Surat Aal Imran:<br />

"hakika a cikin su akwai wadanda suka bata littafi idan (idan suna karantawa)<br />

domin ka yi tsammanin daga littafin su ya ke amma b adaga littafin ya ke ba, sai


su ce wannnan daga Allah SWT ne, amma ba daga Allah ya ke ba. Sun yi wa<br />

Allah karya duk da sun sani."<br />

Allah SWT ya bawa Annabi Muhammad SAW hakuri saboda ya na kokari da<br />

gaskiya, a sanya ma'abuta littafi akan hanya madaidaiciya.<br />

Allah SWT yace a cikin Baqarah, aya ta 75-77 :<br />

" Kana tsammanin za su bada gaskiya da addinin ka duk da wasu daga cikin su<br />

(yahudawa) suna sauraron kalmomin Allah, suna sane suke jirkita ta bayan sun<br />

fahimce ta. Idan (yahudawa) suka iske wadanda suka bada gaskiya sai suce " Mu<br />

mun yi imani", idan kuma suka hadu da junan su sai su ce " Mu (yahudawa) yaya<br />

za mu sanar da su ne abinda Allah ya saukar mana (yahudawa) game da<br />

Alamomi da ingancin Annabi SAW wanda aka rubuta a (At Tauarh), da musulmi<br />

sun yi jayayya da ita dangane da ita a gaban Allah, (yahudawa) suka ce baku<br />

sani ba? "<br />

Yanzu yahudawa suna sane da cewa Allah SWT ya san abinda suka boye da<br />

abinda suke bayyanawa.<br />

Shine Allah SWT yace a aya ta 79:<br />

" Tir da wanda suke rubuta littafi da hannun su, sai suce wannan daga Allah ne, a<br />

saye shi da arha! Tir da su da abinda suka rubuta da hannun su, tir da su da<br />

abinda suka karu da shi"<br />

Daga karshe Allah SWT ya gayyace su zuwa ga hanya madaidaiciya a aya ta 64<br />

Surat Al Imran:<br />

" ka ce yaku ma'abuta littafi (yahudawa da kiristoci) ku zo mu yi magana tsakani<br />

na da ku, kada mu bautawa kowa sai Allah, kada mu hada Allah da wani, kada<br />

mu dauki kowa uban giji sai Allah."<br />

Ya na da ban sha'awa ma'buta littafi ba su kasance daya ba, kamar yadda Allah<br />

ya ce a aya ta 75 a cikin surat Aal Imran:<br />

" A cikin ma'abuta littafi (yahudawa da kiristoci) akwai wanda idan a ka bashi<br />

amanar Qintar a shirye ya ke ya mayar, kuma a cikin su akwai wanda idan aka<br />

bashi kwabo na azurfa ba zai biya ba sai an yi fama, saboda sun ce babu laifi<br />

gare mu idan mun ci amana, kuma idan muka ci kayan jahilai, amma suna fadar<br />

karya da Allah bayan sun sani"<br />

a aya ta 113-114, Al Qur'ani ya furta cewa ba dukkan su daya suke ba, wadansu<br />

daga cikin su sun kasance a hanya ta daidai, suna karanta ayoyin Allaha a cikin<br />

dare kuma suna yin Salla, sun yi imani da Allah da ranar karshe, suna umarni da<br />

kyakykyawan aiki da bin tafarki.wadannan suna daga cikin mutanen kirki".<br />

Ina rokon Allah ya nunawa ma'abuta littafi hanyar shiriya ta gaskiya, wadda ita<br />

ce tun farko aka saukar masu da ita, wadda kuma ba ta da banbanci da Alqur'ani.


WATAN SHA'ABAN<br />

Musulmi suna shagulgula a wani dare a cikin watan sha'aban, a wurare da ban<br />

da ban a fadin duniya, ana kiran wannan dare 'SHAB-BARAH' ko kuma<br />

'LAYLLATUL BARA' dare ne muhimmi. Akwai wadansu sanannun al'adu da imani<br />

ga Musulmi dangane da wannan dare wanda bashi da wani mahalli ko gurbi a<br />

Musulunci. Misalai sune kamar haka:-<br />

1. wadansu Musulmi sun yi imani cewa rayukan wadanda suka mutu suna dawo<br />

masu a wannan rana. Suna daddafa abinci masu dadi rarrabawa mutane. Kwata<br />

kwata wannan ba Musulunci bane. Duk Musulmi na kwarai ba zai bautawa wanda<br />

ya mutu ba sai dai yayi mashi addu'a.<br />

2. A wani camfin kuma, wadansu Musulmi sun ce shawarar a halitta rai da<br />

mutuwa, Allah SWT ya yanke shawarar yin haka ne a sha biyar ga watan


Sha'abaan (15 th Sha'abaan). Gaskiya ne Allah SWT ya yanke shawarar yin rai da<br />

mutuwa, amma fa ya yi hakan ne tun ma kafin a yi halittar mu.<br />

3. Wani shaci-fadin zance kuma shine wai akwai wata itaciya wadda aka rubuta<br />

sunayen kowane mahaluki a bisa ganyayyakin ta. A wanann dare na ake girgiza<br />

ta ganyaye za su fado, su gwada wadanda za su mutu.<br />

4. Wata al'ada kuma maras kyau wadda ake yi a wannan dare shine: mutane<br />

suna yin wasan wuta. Allah kadai ya san bisa ko wane dalilin suke yin ta. Amma<br />

wannan yana kasancewa saboda cudanya da wadansu al'adu na addinan Hindu da<br />

kuma Budah. Mun kasance a cikin wannan al'ada shekaru da shekar, kuma mun ji<br />

dadin aikata wannan mummumar al'ada, kuma bamu damuwa muje wajen<br />

masana daga ciki mu mu gano gaskiyar al'amarin.<br />

Manzon Allah SAW yace " zan bar maku abu guda biyu a baya na sune Alqur'ani<br />

da Hadisi, matukar kuka rike su ba za ku karkace ba. To a nan tambaya ta hakika<br />

: menene matsayin Alqur'ni da Sunna a kan wannan dare na Sha'aban ?<br />

Babu inda aka gwada wannan rana ko a kafa hujja a kan ta a cikin Alqur'ani mai<br />

girma sai dai kadan daga cikin masu Tafsirai sun an'anbace a cikin aya ta 3-4 a<br />

cikin Surat Ad Dukhaan Allah SWT ya ce :<br />

" Mun saukar da shi a cikin dare mai albarka, lallai mun kasance masu gargadi. A<br />

wannan dare ake raba ko wane irin umarni".<br />

Yawancin masu Tafsiri sun yi imani cewa wannan aya tana nufin LAILATUL<br />

QADARI ko dare mai albarka wanda yake a cikin watan Ramdhaan. Kamar yadda<br />

muka gani a fassara, Allah SWT yace an saukar a cikin dare mai albarka, Allah<br />

SWT ya sake cewa a ciki Suratul Al Qadri aya ta 1:<br />

" Na saukar da Shi a dare mai albarka". Daga karshe, Allah SWT ya ce a cikin<br />

Suratul Baqarah, aya ta 185 :<br />

" Na saukar da Al Qur'ani a cikin watan Ramadhan."<br />

A nan ayar da ke a Surat Ad Dukhan tana nufin Lailatul qadri ne ba wai tsakiyar<br />

Sha'aban ba.<br />

A cikin littaifin shi ' At Targhib wat Targhib', al Imam Ibn Al Munzir ya kawo<br />

Hadisai goma sha hudu daga Manzon Allah SAW a kan watan Sha'aban, ga wasu<br />

daga cikin su:-<br />

Manzon Allah SAW ya ce " Ku bada muhimmanci na musamman ga watan<br />

Sha'abaan, saboda yana zuwa kaifn watan Ramadhaan". Watan Ramadhan wata<br />

ne mai tsarki wanda aka saukar da Alqur'an. A watan Ramadhan ne Musulmi su<br />

ke yin azumi. Ka shiryawa zuwan watan Ramadhan a cikin watan Sha'aban. Misali<br />

kuyi kowane irin shiryeye kafin muhimmin bako ya zo, haka nan ka yi shiryeshirye<br />

a cikin watan Sha'aban domin zuwan wata mai alfarma watan Ramdhan.


A wani Hadisin kuma, Manzon Allah SAW yana yawaita yin Azumi a cikin watan<br />

Sha'abaan. A'isha RA tace " Annabin Muhammad SAW yana yawaita yin Azumi a<br />

watan Sha'aban. Wani lokaci sai ya yi ta yi kamar ba zai tsallake kwana ba. A<br />

wadansu lokuttan ba zai yi azumi mai tsawo ba a cikin watan Sha'ban, wannan<br />

yana nuna mana wannan azumin na ganin dama ne domin neman Karin falala.<br />

A wani Hadisin kuma, Manzon Allah SAW ya ce " Allah SWT yana bada wata dama<br />

ga ababen halittar shi da dare. Me ake nufi da wannan? Allah yana kara bada<br />

dama ga ababen halittar shi su tuba, su kyautata halayen su da rayuwar su. Allah<br />

SWT yace " Akwai wanda ya ke son gafara in gafarta mashi? Akwai wanda yake<br />

son taimako in taimake shi? Akwai wanda yake cikin kunci yake rook na in yaye<br />

mashi kuncin?<br />

A nan kofa a bude take ga mai son taimakon Allah musamman a watan Sha'aban.<br />

A wani Hadisin kuma, Manzon Allah SAW yace " ku ziyarci kabarurruka cikin<br />

watan Sha'aban, yana da muhimmanci kuma cikakkiyar tunatarwa ce ". Manzo<br />

SAW ya kara da cewa " Idan wani bai sami wani darasi akan rayuwa da ranar<br />

karshe a wajen ziyarar kabari ba, wannan bashi da wani rabo na samun shiriya ta<br />

gaskiya.<br />

Ina rokon Allah SWT ya shiryar damu a kan hanyar Al Qur'ani da Sunnah, kuma<br />

ya sanya mu a kan hanya ta gaskiya, Ameen.<br />

LAILATUL QADAR<br />

Allah SWT yace a cikin Al Qur'ani a cikin Surat Al Qadar, aya ta 1-5:<br />

" Mun saukar da Al Qur'ani a cikin dare mai albarka. Dare mai albarka yafi<br />

watanni dubu. A wannan dare ne Mala'ika Jibrilu da sauran Mala'iku suke sauka<br />

da izini Allah SWT da umarni. Shi wanan daer amince ne cikin sa har gari ya<br />

waye"<br />

kamar yaddad yazo a wannan surah, Allah SWT ya saukar da Al Qur'ani a cikin<br />

dare mai alabarka. Sani kuma an saukarwa Annabi Muhammad SAW da Alqur'ani<br />

a cikin shekara ashirin da uku, kadan kadan. Hakika, abin tambaya anan shine<br />

me ya sanar da kai cewa an saukar da Alqur'ani a cikin dare mai albarka ?<br />

Yana nufin cewa an sauko da Alqur'ni daga wata muhimmiyar ma'adana ta Allah<br />

wadda ake kira LAUHUL MAHFUZ zuwa duniya a cikin dare mai albarka. Kuma<br />

yana nufin cewa wahayi ma farko da aka yi wa Annabki Muhammad SAW a kogon<br />

Hira' an yi shi ne a cikin LAILATUL KADAR dare mai albarka. Yana da ban sha'awa<br />

mu gane cewa wannnan sura ita ce ta gamo da suratul Alaq, tana nunawa wahayi<br />

na farko an yi shi ne a dare mai albarka.


Me kadar take nufi ? Kadar yana nufin mai daraja, mai karfi. Me ya maida<br />

wannan dare mai girma? Saukar da Al Qur'ani da aka yi a wannan dare shine ya<br />

maida shi mai daraaja da girma.<br />

Haka nan kuma, mutum da ba shi da wata daraja sai ya zama mai daraja mai<br />

farga da Allah idan yayi bauta a wannan dare.<br />

Abu na biyu da ake nufi da KADAR shine Kaddara, ko da yake Allah SWT ya yanke<br />

hukunci tun ma kafin a halicce mu, amma abubuwan da za a yi a wannan shekara<br />

an damkawa Mala'iku domin a zartar a wannan dare. Kamar yadda wadansu<br />

malamai su ka ce., kadan daga cikin ayoyin Surat Addukhan suna nufin wannan<br />

dar kuma suna tabbatar da wannan Magana. Allah SWT ya ce a cikin Surat Ad<br />

Dukhan aya ta 1-4 :<br />

" Wannan littafi yana warware abubuwa da bayyan. Mun saukar da wannan Al<br />

Qur'ani a dare mai albark. Hakika, muna gargadin mutane. A wannan dare<br />

abubuwa masu faruwa a bayyane suke (kamar mutuwa da haihuwa).<br />

Wadansu malamai suna ganin wannan ayoyi na suratud Dukhan suna nufin watan<br />

Sha'aban. Sun ce yanke hukunci an yi shi ne a watan Sha'aba an baiwa Mala'iku<br />

su zartar a cikin wannan dare mai girma. Allah SWT shi ya san dai dai.<br />

A gaba, sai Allah SWT yace wannan dare mai girma yafi dare dubu. Me ake nufi<br />

da wannan? Larabawa wannan lokacin sun dauki dubu wani abu mai yawa. Ana<br />

nufin yin bauta a wannan dare yafi darare masu yawa.<br />

Watanni dubu dai dai ne da shekara tamanin da uku ko da hudu, larabawa su na<br />

ganin mutumen da ya shekara tamanin ya zama cikakkiyar ibada ko mai yawan<br />

ibada tunda ya kasance mai ibada tsawon rayuwar shi. Amma yin ibada a cikin<br />

wanna dare ya fi yin ibada na sama da shekara tamanin.<br />

Har wa yau, Ibn Abi Hatim ya ruwaito daga Mujahid cewa : Annabi Muhammad<br />

SAW ya baiwa sahabban shi labarin wani mutum daga cikin Bani Isra'ila wanda<br />

yake ta yin bauta har tsawon shekara tamanin ba yankewa. Haka nan kuma Ibn<br />

Jarir ya ruwaito daga Mujahid cewa Ananbi Muhammad SAW ya ce " Wani mutum<br />

daga cikin Bani Isra'aila ya kasance yana yin ibada cikin dare kuma yana fita yaki<br />

don daukaka kalmar Allah da rana. Yayi wannan har tsawon shekara tamanin<br />

babu yankewa. Allah SWT yana cewa al'umar Annabi Muhammad SAW cewa yin<br />

ibada a wannan dare yafi ibadar wannan Bani Isra'aila ta shekara tamanin. Don<br />

haka, dare mai albarka wata muhimmiyar dama ce ta al'umar Annabi Muhammad<br />

SAW kuma kyauta ce ta musamman daga Allah zuwa Annabi Muhammad SAW da<br />

mabiyan Shi. Wannan ya gwada yadda Allah SWT ya ke son Annabi Muhammad<br />

SAW da mabiyan wannan Annabin, koda yake mabiyan Annabawa na farko an<br />

wajabta masu yin azumi amma al'ummar Annabi Muhammad SAW aka ba<br />

kebantacciyar daraja ta samin mai albarka a cikin watan azumi.


A daren lailatul kadar, Malai'aka Jibril da wasu Mala'iku wanda suke a Sidratul<br />

Muntaha suke saukowa a doron kasa su yi roko na musamman ga Allah ga<br />

wadanda suke tunawa da Allah a zaune suke ko a tsaye. Dare mai albarka na<br />

lailatul kadar dare ne na aminci da kyautatawa. Wannan yanayi na aminci yana<br />

tabbata har wayewar gari. Wadansu mutane suna kasancewa suna ganin<br />

wadansu ababen mamaki a wannan dare. Wadanda ma basu ga wani abin<br />

mamaki ba sun sami nasu rabon su a wanna dare mai albarka.<br />

A yaushe ne wannan dare Allah SWT ya ce a cikin Alqur'ani, suratul Baqrah, aya<br />

ta 135:<br />

" Mun saukar da Al qur'ani a cikin watan Ramadhan"<br />

a cikin Surat Al Qadar aya ta 1 Allah yace :<br />

" Mun saukar da Al Qur'ani a cikin dare mai albarka".<br />

A nan dare mai albarka ya kasance a wani lokaci a watan Ramdhan. Akwai<br />

Hadisai na Annabi Muhammad SAW da dama da suka yi bayanin hakan kamar<br />

yadda ya zo a Bukhari.<br />

A'isha RA tace Annabi SAW yace " ku dubi daren Lailatul qadar a kwanaki goma<br />

na karshe na watan Ramadhan.<br />

Kuma ya zo a Muslim daga dan Umar cewa Annabi Muhammad SAW yace " kubi<br />

dare a lokaci a kwananki na mara a kwanaki goma na karshen watan Ramdhan".<br />

Mutane da dama sun amince da daren 27 na watan Ramdhan. Ba a tantance shi<br />

ba saboda mu sami Karin rahma wurin Allah SWT mu nemi wannan dare mu yi<br />

tsaye wajen tunawa da Allah SWT. Wannan rahma ce ta Allah SWT a gare mu.<br />

Wani lokaci muna rayawa wannan dalili ne Allah SWT ya saukar da AlQur'ani mai<br />

girma a cikin dare ba da rana ba. Allah SWT shine masani. Har wa yau, muna iya<br />

cewa dare lokaci ne na aminci kuma lokaci ne na nutsuwa, kuma mun fi<br />

kasancewa cikin kamun-kai da nutsuwa kamar yadda Allah SWT yace a cikin<br />

Surat Al Muzzammil aya ta 6:<br />

" A cikin dare yanayin ya fi kuma kalmomi suna a kai tsaye"<br />

A wata fadar, kalmomi sun fi kasancewa da gaske da tasiri a cikin dare yanayin<br />

kuma yafi shudewa.<br />

Mun sani kuma dare kamar yadda wadansu manazarta suka ce yana nufin duhu<br />

kararre da babu. Idan gari ya waye komi sai ya kasance a bayyane. Lokacin da<br />

aka saukar da Al Qur'ani al'uma suna ciki duhu Al Qur'ni ya sauya wannan duhu<br />

zuwa ga haske. Wannan ita ce saukakkiyar hanyar shiriya ta Al Qur'ani wanda ya<br />

banbanta tsakanin abinda yake na daidai da wanda ba na daidai ba. Allah SWT ya<br />

ce a cikin Surat al Baqarah, aya ta 185:<br />

" Al Qur'ani shiriya ce ga mutane bayyananniyar hujjar shriya da za ta banbance<br />

tsakanin abinda yake (dai dai da wanda ba daidai ba)".


Ka sani ba wai shiriya ba ga larabawa kawai, ko wadanda suka yi imani kadai<br />

bane amma ga dukkanin al'umma. Allah SWT yace a Al Qur'ani:<br />

" Allah SWT ya saukar da Al Qur'ani ga bayan shi masu biyayya masoya bay.<br />

Wannan shiirya tana fitar da mutane daga cikin duhu ta sanya su a cikin haske.<br />

Allah SWT hakika mai tausayi ne mai rahma ga ababen halitta".<br />

Ka sani cikin duk alfarmar da Allah SWT ya yiwa al'umma babbar alfarma ita ce<br />

ya ba su shiriya. Hakika idan babu wannan shiriya mutane za su kasance a cikin<br />

hasara a cikin duhu.<br />

A karshe, A'isha RA ta tambayi Annabi Muhammad SAW " me zan yi idan na ga<br />

dare mai albarka?". Annabi Muhammad SAW sai yace yi wannan addua'r :<br />

Allahumma innka Afuwwun tuhibbul Afwa fa'afu anna".<br />

" Ya Allah kai mai gafara ne kuma son gafara, ka gafarta mana".<br />

Ya Allah muna rokon ka ka amshi wannan daaan kokari ka gafarta min da<br />

wadanda suke karantawa da masu sauraren wannan bayani amin.<br />

AL'UMMAR MUSULMI DA KE ZAUNE A MADINA<br />

Musulmi da suke zaune a birnin Madina a lokacin Annabi Muhammad SAW za a<br />

kasu su gida biyu : Yan Hijira (Muhajirun) sai 'yan gari (Ansar). Halayen<br />

wadannan rukuni na al'umma an yi bayanin shi a a cikin Surat Al Hashr aya ta.<br />

Allah SWT yace :<br />

" (Akwai rabo a cikin wannan ganima) ga talakawa masu Hijira wadanda aka kore<br />

su daga gidajen su da dukiyoyin su, suna neman yardar Allah da kuma kyautata


mashi da taimakon Allah (shine taimakon Addinin Shi) da manzon Shi, wannan<br />

hakika su ne masu gaskiya ( a cikin abinda suka ce)".<br />

Wadannan 'yan Hijira sun kasance ana ta gana masu akuba a Makkah, shine ya<br />

tilasta su su yi hijira zuwa Madina. Kafirai suka mamaye kayayyaki da kadarorin<br />

wadannan ma su hijira. Shine ya sanya Al Qur'ani mai girma yake kiran 'yan<br />

Hijira Faqeer watau talakawa kwarai. A mafi yawan lokaci mafi yawan su basu da<br />

ba su da abinda za su ci, ya kasance suna daura dutse a cikin su. Wadansu kuma<br />

sai su haka rami su zauna a ciki domin su kare kan su daga sanyi.<br />

Hali na biyu na wadanna Muhajirun shine dalilin da yasa suka bar gidajen su ba<br />

domin wani abin duniya ba. Hakika shine domin samun soyuwa a wurin Allah SWT<br />

a nan duniya da kuma samun rahmar Allah a gobe kiyama.<br />

Hali na uku na masu Hijira domin taimakon Allah SWT da Manzon Shi SAW. A<br />

nan taimakawa Allah yana nufin taimakawa wajen yada addinin Allah SWT. Sun yi<br />

mashahuriyar sadaukar da rayuwa domin cin nasarar wadannan ababe guda biyu.<br />

Hali na hudu na muhajirun shine su masu gaskiya ne a wajen maganganun su da<br />

huldayyar su. Sun tsaya akan dugadugan su a kan shaidawar da suka yi Allah<br />

SWT da Manzon Shi SAW a lokacin da suka shiga Musulunci. Allah SWT ya Fada a<br />

wannan ayar cewa dukkan Muhajirun masu gaskiya ne . a nan kayi batanci a kan<br />

su wannan kin yin biyayya ne ga fadar Allah SWT.<br />

A aya ta gaba, Allah SWT yayi bayanin halayen Ansar Suratul Hashr aya ta 9:<br />

" Da su wadana kafin su, suna da gidaje kuma suka yi imani suna son wadanda<br />

suka yi Hijira zuwa wajen su, ba su da bakin –ciki a ran su akan abinda aka basu<br />

da wadanda aka ba muhimmanci akan duk kuwa da suma mabukata ne. Duk<br />

wanda ya tsira daga bin son zuciyar shi, wadannan sune masu samun nasara".<br />

Yana da ban-sha'awa ka sani cewa Imam Malik ya dauki birnin Madina mai daraja<br />

a matsayin birni mafi mafi albarka da daraja a fadin duniya, saboda shi wannan<br />

birni an mamaye shi ne ta hanyar iman. Duk wadansu sauran birane har ma da<br />

Makka an mamaye su ne ta hanyar yaki. Allah SWT yace :<br />

" Hakika nasara ta farko ta Ansar shine sun tashi ne daga gari mai girma, wanda<br />

ya bada mafaka ga Manzon Allah da mabiyan shi".<br />

Abu na biyu, su Ansar basu dauki wadannan yan Hijira su zame masu matsala ba,<br />

sun karba ne da hannu bibbiyu kuma sun nuna masu soyayya ta gaskiya. Saboda<br />

wannan soyayya ne Ansar suka raba dukiyoyi da gidajen su da su. Ansar wanda<br />

yake da mace fiye da guda, sai ya saki matar shi guda domin ta auri dan gudun<br />

hijirar nan (Muhajirun). Ta wannan hanya , Ansar zai gabatar da Muhajir dan<br />

uwan shi ga matan shi sai ya bashi dama ya zabi wadda ya ke so. Sai ya kasance<br />

a wannan lokaci sanya hijabi ba a saukar da shi ba.


Hali na uku na Ansar shine da zuciya daya suke karbar duk abinda Manzon Allah<br />

SAW ya baiwa Muhajirun. Misali lokacin da Musulmi suka sami galaba a akan<br />

Banun Nadheer da Banu Qainuqa', an sami dukiyoyi ba tare da an yi wani yaki<br />

ba. Annabi Muhammad SAW ya rarraba wanann kaya ga kashi biyar wanda aka<br />

fadi a cikin Al Qur'ani mai girma. Annabi Muhammad SAW ya tamabayi Thabit bn<br />

Qais ya tattar dukkan Ansar. Annabi Muhammad SAW ya yi masu jawabi kuma ya<br />

yaba masu da halin su abin koyi wanda suka yi wa Muhajirun. Annabi Muhammad<br />

SAW ya kawo shawarwari guda biyu dangane da rarraba kayan da aka samu ,<br />

yace " idan na rarraba kayan ga Ansar da Muhajirun, a wannan hali to Muhajirun<br />

za su dinga kasancewa a gidajen Ansar. Amma idan na rarraba kayan nan ga<br />

Muhajirun za su kasance sun bar gidajen Ansar sun tafiyar da rayuwar su ta cin<br />

gashin kan su. Shuwagabannin Ansar Sa'ad Bn Ubbadah da Sa'ad Bn Mu'az suka<br />

ce ka rarrabawa masu hijirah su kadai kuma su ci gaba da zama a gidajen mu.<br />

Allah SWT ya ji dadin wannan abu da Ansar suka yi kuma ya saukar da aya yana<br />

cewa Ansar ba su sami wani rashin jin dadi ba a ransu wajen bayar da wannan<br />

manyan kadarori. Ansar su yi hakan ne tamkar su ba su bukatar waddannan<br />

kayayyaki .<br />

Sai ya kasance, wadannan kayayyaki Annabi Muhammad SAW ya rarrabawa<br />

Muhajirun har wadansu mutane daga cikin Ansaar wadanda ked a tsananin<br />

bukata Sahal Bn Haneef da Abu Dujanah.<br />

Halayya ta hudu ta Ansar shine sun fi son su biya bukatar Ansar sama da su biya<br />

bukatun kan su.<br />

Qurtabi RA yayi baayanin abubuwan da suka rika faruwa a tsakanin masu Hijira<br />

da Ansar. Wadannan abubuwa sune aka yi bayanin nan saboda suna da<br />

muhimmanci saboda rayuwar al'umma.<br />

Abu Hurairh RA ya ruwaito cewa wani lokaci wani mutum ya zo wajen Annabi<br />

Muhammad SAW yace " ina jin matsananciyar yunwa har ta kai ni ga wani<br />

matsayi bana iya daurewa". Annabi Muhammad SAW ya tambayi matan shi ko<br />

akwai abinci? Suka ce babu kome sai ruwa. Annabi Muhammad SAW ya ce wa<br />

sahabban shi wa zai dauki nauyin wannan dan uwa yau da dare? Wani Ansar ya<br />

dauki wannan dan uwa zuwa gidan shi, sai ya tambayi matar shi ta kawo abinci,<br />

sai ta amsa mashi " abincin ma ba zai ishi yaran su ba". Sai Ansar ya cewa matar<br />

ta shimfidar da yaran su yi barci. Yace ta kawo abincin kuma ta kasha fitila, zan<br />

yi kamar ina cin abincin da bakon, ba zai sani ba tunda cikin duhu ne. bakon yaci<br />

abincin, sai suka koma wajen Manzon Allah SAW kashe gari. Annabi Muhammad<br />

SAW ya taya wannan Ansar murna, yace " Allah ya ji dadin karimcin da ka yi jiya<br />

da dare.


Abdullah Bn Umar ya ruwaito cewa wani mutum ya aikawa wani dan uwa Musulmi<br />

kyautar naman akuya, sai wannan shima ya aikawa wani dan uwa Musulmi tunda<br />

yana ganin shi ya fi shi bukata, na uku shima ya aikawa mutum na hudu sai da ta<br />

tabi hannun mutum bakwai, har daga karshe ta koma hannun wanda ya fara<br />

badawa. Wannan an yi bayanin shi a kushari. Akwai wata riwaya irin ta<br />

daga Anas kamar yadda a ka yi bayani a Tha'labi<br />

A'isha RA tace wani almajiri yazo gidan ta yana bara, to biredi daya ya rage a<br />

gidan ta. A'isha ta umarci bawan ta ya ba wannan almajiri biredin nan, sai bawan<br />

yake mamakin ta yaya A'isha za ta yi buda baki a wannan yammaci. A'isha RA ta<br />

nace akan sai an baiwa almajirin biredin. To sai ya kasance da yamma sai aka<br />

aikowa Aisha dafaffen naman akuya. Aisha RA ta kira baiwar ta zo su ci.<br />

Nasa'i ya ruwaito cewa wani lokaci Abdullahi Bn Umar RA ya kasance baya da<br />

lafiya kuma yana son ya ci inabi. A nan aka sayo mashi inabi. Kwatsam sai<br />

almajiri ya zo, sai Bn Umar ya baiwa wannan alajiri wannan inabin. Wani daga<br />

cikin bakin Bn Umar ya je ya sayo wannan inabin daga wajen wannan almajirin<br />

ay kawowa Bn Umar, sai wannan almajirin ya sake dawowa, Bn Umar ya sake<br />

baiwa wannan almajiri wannan inabin, wannan almajiri ya sake sayo wannan<br />

inabi ya kawowa Bn Umar, yana tsammanin wannan inabi an sayo shi ne daga<br />

kasuwa , da ya san haka da ba zai ci ba inabin a karo na uku.<br />

Ibn Mubarak ya fada a cikin Musnad nashi cewa wani lokaci Khalifa Umar ya aikin<br />

bawan shi da dinari dari hudu wajen Abu Ubaida Bn Jarrah. Umar ya umarci<br />

bawan da ya lura da yadda zai yi da wannan kudi. Bawan nan ya fadawa Umar<br />

cewa Abu Ubada ya rarraba dukkan kudin ga masu bukata. Haka nan kuma Umar<br />

ya aikawa Mu'az Bn Jabal dinar dari hudu ta hannun bawan shi kuma ya umarce<br />

shi da ya lura da yadda zai yi da wannan kudi. Bawan nan ya dawo ya fadawa<br />

Umar cewa Mu'az Bn Jabal ya rarraba wannan kudin ga masu bukata, da sauran<br />

dinar biyu suka yi saura matar Mu'az ta ce " ni ma mabukaciya ce, a bani", sai<br />

Mu'az ya ragowar dinari biyu. Khalifa Umar RA ya cewa bawan shi " Yan uwa na<br />

kamar su daya a halin su ".<br />

Huzaifa Adawi ya ruwaito : na tafi neman kawu na a yakin Yarmouk ina rike da<br />

ruwa ga wadanda suke da sauran rai. Na sami kawu ya kusa mutuwa. Na ba shi<br />

rowan da nake dauke da shi, sai ya ji wani dan uwa yana kuka kusa da shi, kawu<br />

na ya ki shan rowan matsa in kaiwa wannan dan uwan. Shi na biyu sai ya ji<br />

kukan wani dan uwa na uku, sai ya umarce ni in yi sauri in kaiwa wannan na uku.<br />

A haka sai da na kai kan mutum na bakwai, a lokacin da na kai kan mutum na<br />

bakwai har ya riga ya cika, na hamzarta wurin kawu na, shi ma har ya riga ya<br />

rasu.


Allah SWT ya kasa al'ummar Annabi Muhammad SAW kashi uku : masu hihira,<br />

Ansar, da kuma sauran al'mmah. Allah SWT yayi bayani nagartar Muhajirum da<br />

Ansar a cikin Al Qurani. Har way au, yayi bayanin nagarta daya ta sauran<br />

al'umma. Wannan kashi na uku dole su kasance suna yabawa sahabban Manzon<br />

Allah SAW ba wai don sun kasance ba sun banbanta saboda irin imanin su ba,<br />

amma sai saboda imani yazo mana ne ta hannun su. A nan su wadannan rukuni<br />

na uku, su kasance suna yi wa sahabban Annabi Muhammad SAW addu'a, kada<br />

kuma su dauki wata kiyayya a ran su a kan sahabban Annabi Muhammad SAW.<br />

Aya ta 10 a suratul Hashri addu'a ce mai kyau:<br />

" da wadanda suka zo bayan su, ya Allah ka yafe mana da yan uwan mu da suka<br />

zarce mu imani, kada ka sanya a cikin ran mu wata kiyayya akan wadanda suka<br />

yi imani. Ya Allah hakika kana da cikakkken jin-kai, mai rahama".<br />

Mus'ab Bn Sa'id yace muna iya kasancewa kadai a cikin wannan rukuni idan<br />

muka sami halayen da aka zayyana a sama.<br />

Qurtubi ya tsamo a cikin wannan aya cewa wajibi ne mu kasance muna mutunta<br />

sahabban Annabi Muhammad SAW. Imam Malik yace " musulmi bashi da wani<br />

kaso a kowace ganima idan ba shi da kyakykyawar alaka ta mutunci da sahabban<br />

Annabi Muhammad SAW".<br />

Abdullah Bn Abbas yace " Allah SWT yayi umarni ga daukacin musulmi su yi<br />

addu'a ga sahabban Annabi Muhammad SAW. Allah ya sani, za su sami sabani a<br />

tsakanin su, kuma za su yi fada a tsakanin su, duk da haka mu kyautata<br />

tsammani ga sahabban Annabi Muhammad SAW.<br />

An karbo daga A'isha RA daga Annabi Muhammad SAW yace : al'ummar shi ba za<br />

su wargaje ba idan basu zagi wadanda suka shude gabanin su ba.<br />

Abdullahi Bn Umar RA yace idan ka gamu da wani wanda yake la'antar sahabban<br />

Annabi Muhammad SAW sai kawai kace " Uban giji Allah ya la'anci wanda yake<br />

mafi muni daga gare ku". A wannan hali Allah SWT sai yayi maganin shi.<br />

Awwam Bn Jush'ab yace" na sami Musulman farko suna tunatar da saura akan<br />

baiwar sahabban Annabi Muhammad SAW, su kara soyayya a gare su, su kauce<br />

fadar sabani da rigingimu tsakanin sahabbai, saboda ba za su kasance kanana<br />

suna zargin sahabban Annabi Muhammad SAW.<br />

Ya Allah mu yabo da kirki irin na sahabban Annabi Muhammad SAW domin mu<br />

kasance cikin rukuni na uku mu sami cin nasara a rayuwa da rayuwa ta ranar<br />

karshe. Amen.


JARRABAWAR DA AKA YIWA ANNABI IBRAHIM AS<br />

Aya ta 124 a suratul Baqarah, Allah SWT yace:<br />

" Da Allah SWT ya jarraba Annabi Ibrahim AS, Annabi Ibrahim AS ya ci<br />

jarrabawar. Allah SWT yace da shi " zan maida kai shugaban duka al'uma".<br />

Annabi Ibrahim AS yace ya Allah wannan alkwali har da yara suma ! Allah SWT<br />

ya bada amsa "I" amma banda wanda suka fandare".<br />

Tambaya da yawa ta zo a rai, ko menene ya sa Allah SWT zai jarraba wani,<br />

wanda kuma shi masani ne a kan komi? Yaya yanayin wannan jarrabar take?<br />

Menene sakamako wannan jarabawar ? idan akwai ko yaya? Za mu amsa wannan<br />

tambayoyi daya bayan daya.<br />

Dalilin wannan jarrabawa ba wai domin a bada wani maki bane, ci ko faduwa.<br />

Dalilin wannan yana nuna da kalmar 'Rab' a wannnan ayar. Allah SWT ya zabi<br />

wannan kalma domin kan shi, kuma amfanin wannan jarrabawa domin sanya<br />

mutum akan wani a kan wani ruhu da kuma koyar da shi a kan mataki na<br />

kokkoliya. Waka a Urdhu ta ce :<br />

Kai meke kada kaji tsoron iska da ya kiye maka, wannan zai kai ka sama da<br />

kokkoliya. A nan wahala tana koyar da mutum ya kai babban matsayi.<br />

Mun sani cewa Allah SWT yana fada mana sakamakon jarrabawar Ibrahim AS,<br />

yana cewa ya cika wanna jarrabawa. Wannan yana nufin Ibrahim AS ya fada da<br />

kyakykyawar sifa cewa " Ibrahim AS wanda ya aika alkawalin shi". A aya ta 37 a<br />

surat An Najm.<br />

A anan, sai mu yanke cewa Ibrahim AS ya ci dukkan jarrabawar shi. A bisa<br />

wannan sakamako ne Allah SWT yace dashi " Zan maida kai shugaban dukkan


talikai". Annabi Ibrahim AS yayi farin ciki amma kuma yana tunanin bayan shi.<br />

Allah SWT yace " Hakika akwai shuwagabannin talikai daga zuriyar ka sai dai<br />

wadanda suka fandare.<br />

A nan mutanen littafi ba su kasance shuwagabanni ba tunda sun hada Allah da<br />

wanin sa.<br />

Yanzu za mu yi bayanin jarrabawar da aka Annabi Ibrahim AS. Za mu fara da<br />

lokacin da yake yare da iyayen shi da mutanen su. Ya same su suna bautar<br />

gumaka wanda suke sassakawa da hannun su. Annabi Ibrahim AS yayi jawabi ga<br />

wadannan gumaka kamar yadda bayani ya zo a suratus Saffat aya ta 91-98:<br />

" sai ya juya ga gumakan ya ce " ba za ku ci (abubuwan da ake kawo maka ba)?<br />

Menene ya same ku da ba za ku yi Magana ba? Sai ya juya gaba gare su yana<br />

bugon (su) da (hannun shi)na dama. Sai masu bautar gumakan suka juyo gare<br />

shi a gaggauce. Yace da su " kuna bautawa abinda ku da (kan ku) kuka sassaka?<br />

" bayan da Allah ya halicce ku da kuma abinda ku ke yi". Sai suka ce " ku gina<br />

mashi wani gini (wannan gini tamkar wurin narka karfe), ku jefa shi cikin wuta<br />

mai kuna". Sai suka shirya wannan makarkashiya a kan shi, sai muka maishe shi<br />

kaskantattu".<br />

Annabi Ibrahim AS yace " Hasbunallahu wa ni'mal wakilu". "Allah SWT shine ya<br />

isa ya kare ni shine mai jibinta ta".<br />

Allah SWT ya umarci wannan giwat wutar ta kasance mai sanyi ba mai cutarwa<br />

ba ga Annabi Ibrahim AS.<br />

A yanzu Annabi Ibrahim AS dole ya bar mahaifin sa da mutanen shi da abinda<br />

suke bautawa. Sai ya tafi Syria da matar shi. Wannan al'amari ma an yi bayanin<br />

shi a suratus Saffaat aya ta 99-100 :<br />

" (Annabi Ibrahim AS) ya ce " na bi hanyar Allah SWT wanda shine hakikan<br />

wanda zai shiryar dani. Ya Uban-giji ka ba ni 'ya'ya daga masu adalci".<br />

Daga nan ne malamai suka ce sunna ce ta kowane Annabi yayi aure ya sami yaya<br />

ma su shiriya, saboda su kasance sun ci gaba da aikin Allah SWT. Misali kuma<br />

shine na Annabi Zakariyya' AS, aya ta 38 Surat Aal Imaran:<br />

" A lokacin da Zakariyya ya rokin Uban-gijin shi : Ya Uban-giji ka bani daga gare<br />

ka 'ya'ya na gari. Hakika kai mai jin roko ne".<br />

to dole ne mu yi addu'a ga Allah SWT ya bamu 'ya'ya na gari salihai.<br />

Allah SWT ya baiwa Annabi Ibrahim AS shiryayyen da wanda zai gwada wata irin<br />

mu'ujiza ta yin hakuri da kamun-kai. Hajara matar Annabi Ibrahim AS ta haifai da<br />

Isma'il AS.<br />

Allah SWT ya umurci Jibril ya dauki Annabi Ibrahim AS da matar shi da kuma<br />

jaririn su wani waje ana kiran shi Makka a yanzu. An umarci Annabi Ibrahim AS<br />

da ya koma Syria da zaran sun je wajen. Ruhin mika wuya ga umarnin Allah ya yi


girma a zuciyar Annabi Ibrahim AS, nan da nan ya kama hanya zuwa Syria. Sai<br />

matar shi tace " ina za ka tafi ka bar mu nan inda babu wasu gidaje ba ruwa ba<br />

ciyayi? Duk da haka bai amsa mata ba. Daga karshe tace " ko Allah ya kai ka<br />

haka?" Annabi Ibrahim AS ya amsa "I". Sai tace " ba koma wanda ya tura ka zai<br />

jibinci al'amarin mu".<br />

Da Annabi Ibrahim AS yaje akan dutse sai ya juyo yayi addu'a " ya Allah SWT na<br />

ajiye iyalai ba a wajen da babu alamar tsirrai ko kadan! Ka basu abinda za su<br />

rayu domin su yi sallah domin su kasance sun mika wuya a gare ka".<br />

Yana da ban sha'awa muga yadda annabawa suke daidaitawa tsakanin hakkin<br />

Allah SWT da hakkin mutane.A wani hannun kuma ' Sufaye' suna tsunduma ne<br />

wajen cika hakkin Allah SWT kawai.<br />

Wannan ita ce babbar jarabawa ga dukkan iyalan Annabi Ibrahim AS . Hajara ta<br />

sami jaririn ta yana kuka a bashi ruwa sai ta ruga kan wani tsauni tana neman<br />

ruwa, sai ta je bata samo ba, ta ruga da gudu wajen yaron da yake kuka. Sai ta<br />

sake rugawa a kan wani dutsen da ake kira 'MARWAH' ta gani ko ta sami ruwa.<br />

Nan ma bata samu ba. Hajara sai da tayi zarya sau bakwai tsakanin safa da<br />

Marwa ta neman rowan da zata bai wa dan ta. A yayin da ta dawo wajen wannan<br />

zarya sau bakwai, sai ta sami dan ta yana buga kafar shi a kasa. Abin mamaki,<br />

sai ta sami ruwa yana bulbulowa daga wurin wanda da yanzu ake kira ZAM ZAM.<br />

Har yanzu wannan ruwa yana nan yaan kwararowa yana amfanar al'umma.<br />

Annabi Ibrahim AS ya kasance yana ziyartar iyalin shi lokaci zuwa lokaci. Da dan<br />

shi Isma'il ya kai saurayi, Annabi Ibrahim AS yace da shi " ya kai da na na gani a<br />

mafarki zan yi layya da kai me kake gani game da wannan?". Wannan ya gwada<br />

mana yadda uba zai yi Magana da dan shi. Annabi Ibrahim AS yayi mashi<br />

cikakken bayani ya jira ya saurari abinda zai ce. Wannan ya bar faffadar Magana<br />

ta nasiha idan ya kama. Wannan kuma ya jarraba irin matsayin mika wuya ga<br />

Allah SWT na dan shi, kuma ya sake gwada mana wannan shine lokacin da da<br />

yake taimakon iyayen shi, ko wadanne iyaye a kagare suke suna jiran wannan<br />

lokaci. Allah SWT ya umarci Annabi Ibrahim AS yayi hadaya da dan sa a halin<br />

kuruciyar shi. Wannan ma babbar jarrabawa ce ga iyalan Annabi Ibrahim AS.<br />

Amsar da dan yayi tana da ban-al'ajabi. Yace " ya kai baba na, ka ci gaba da<br />

abinda aka umurce ka".<br />

Wannan saurayin yaro karara ya fahimci cewa ko da mafarkin Annabi kamar<br />

wahayi ne daga Allah SWT kuma umarni daga Allah SWT. Kuma Isma'il ya kara<br />

da cewa " In sha Allah za ka same ni daga cikin masu hakuri". Wannan amsar<br />

tana da darasi da yawa a kan mu. Abu na farko mu rika sanya In sha Allah a cikin<br />

zantuttukan mu, kamar yadda a gwada mana mu yi a cikin suratul Kahf da suratu<br />

Noun. Abu na biyu Isma'il ya gane cewa akwai mutane kafin wadanda suke da


matsananciyar dangana. Maimakon ya cika baki game da hakurin shi sai ya<br />

kaskantar da kan shi ya ce " da yardar Allah za ka same ni a cikin masu hakuri.<br />

Uba da dan sa tare sai suka tafi wani wuri da ake kira Mina. A kan hanyar su<br />

shedan yayi kokari ya hana uban, si yace " mafarkin ne kadai ka yi me ya sa za<br />

ka yanka dan ka a kuruciyar shi?" Annabi Ibrahim AS ya dauki duwatsu ya jefi<br />

Shaidan ya kore shi. Sai Shaidan ya dawo yana jawo hankalin Isma'il da<br />

mahaifiyar shi. Suma suka dauki duwatsu suka rika jifar shi suka kore shi da<br />

karfin imanin su.<br />

Da da uba a shirye suke da yin hadaya. Maganganu masu cin rai suka afku a<br />

tsakanin su. Da ya cewa uban shi wadannnan abubuwa :-<br />

* Ya baba na ka daure hannu na da kafa ta domin kada in yi ta tsalle.<br />

* Ka wasa wukar ta yi kaifi domin ka yi saurin yanka makogaro na, domin rai na<br />

yayi saurin fita, mutuwa tana da wuya kwarai.<br />

* Ka janye tufafi daga jini na domin kada lada ta ta ragu kuma uwa ta hankalin<br />

ta kada ya tashi idan ta ga jinin.<br />

* Ka yi sallama ga uwa ta, ka bata riga ta, wannan zai iya kwantar mata da<br />

hankalin ta.<br />

Annabi Ibrahim AS ya saurari wannan jawabi mai tada hankali daga bakin dan<br />

shi, amma Annabi Ibrahim AS bai karaya ba. Sai yace ga dan shi " Ya kai da na<br />

kana da taimako wajen aiwatar da aikin Allah SWT.<br />

Wannan bayani ya zo a Surat As Saffat aya ta 103-107 :<br />

" Lokacin da dukkan suka mika wuya ga Allah SWT, Annabi Ibrahim ya kwantar<br />

da dan shi a kan fuskar shi. Allah ya kirawo Ibahim " ya Ibrahim ! ka cika<br />

wahayin abinda ka gani a mafarki. Muna bayar da lada ga aiki mai kyau irin<br />

wannan. Hakika wannan bayyananniyar jarrabawa ce. Mun sauya maka da<br />

babbar hadaya".<br />

Rago aka bayar a maimakon Isma'il AS. Allah SWT ya shaidar Annabi Ibrahim AS<br />

kuma ya umarci duk wadanda za su zo bayan shi su girmama shi. Allah SWT ba<br />

kawia ya ceto Isma'il bane, kuma ba shi wani da Isaac. Dukkan su mashahuran<br />

Annabawan Allah ne.<br />

Allah SWT yana son mika wuya irin na kowane daya daga cikin iyalan Ibrahim AS<br />

sosai ya sanya shi ya zamo alama ga sauran baya su mayar da ita bangaren aikin<br />

Hajji.<br />

Ya Allah SWT ka bamu kwarin gwiwa da zuciyar mika wuya ta bin Allah kamar ta<br />

iyalin Annabi Ibrahim, Amin.


MARYAM<br />

Kafin kirsimati, ko lokacin kirsimati ko bayan kirsimati, muna jin maganganu da<br />

yawa game da Maryam (Mary) daga kiristoci. Za ka ga an baje kolin kamannin<br />

Maryam a coci-coci da wuraren ciniki da wake-wake da dama. Wannan tana<br />

kawowa Musulmi da yawan su rudani. Ya kamata mu san ko wacece wannan<br />

Maryam din (Mary). Yana da ban-sha'awa mu juyo mu dubi yarintar ta, yadda ta<br />

tashi, kuruciyar ta, da kasancewar ta cikakkiyar mutum ta haske da shiriyarwar<br />

ta a Al Qur'ani. Yadda Maryam ta dauki ciki da hanyar da ta haifi mashahurin da<br />

(Jesus) Isa AS. Yana daga ayoyin Allah SWT ga ababen halitta. Abinda ya faru da<br />

haihuwar Maryam an yi bayanin sa a cikin Surat Aal Imran aya ta 35-36:<br />

Yayin da mahaifiyar Maryam take tsammanin haihuwa sai ta ce " Ya Allah":<br />

" Na damka wannan da nake dauke da shi a ciki na domin yayi dawainiya domin<br />

ka, ka amsa ka san sahihancin abinda na ce kuma kana jin duk abinda muke<br />

cewa".<br />

" Sa'annan da ta haifi jaririyar ta (Maryam) sai tace " Ya Ubangiji! Na haifi diya<br />

mace. Allah shine ya fi cancantar ya san abinda ta haifa, kuma na-miji ba kamar<br />

mace bane, kuma na sanya mata suna Maryam. Ina neman kariya daga gare ka<br />

Allah domin ta da 'ya'yan ta daga shaidan wulakantacce".<br />

Lokacin da mahaifiyar Maryam ta haihu ta yi mamakin abinda ta haifa yarinya ce.<br />

Wannan wani abu ne da kowa ya amince; yaro na-miji shine ke iya daawiniya a<br />

masallaci. Duk da haka ta sanyawa wannan yarinya suna 'MARYAM', kuma tayi<br />

roko ga Allah " Na damka ta da 'ya'yan ta karkarshin kariya ta Allah daga shaidan<br />

wulakantacce. Sai kuma abinda ya wanzu a haihuwar wannan jaririya (Maryam),<br />

an kara bayani. A wannan surah Allah SWT yace:<br />

" Hakika, yarinya ba kamar yaro ta ke ba". A wata fadar, kuma yarinya za ta<br />

zama ta da ban daga yaro. Kuma yazo hakika daga wannan ayar uwa tana da<br />

dama ta sanyawa dan ta suna kamar yadda uba yake. A wata fadar kuma ba<br />

dama bace ta uba ya sanyawa dan shi suna. A gaske dama ta mace da namiji<br />

daya take a musulunci. Sai dai kawai dawainiyar da zai yi ya banbanta, wannan<br />

dawainiya Allah ya sanya ta shine ya fi cancantar sanin abinda abin halittar sa zai<br />

iya.<br />

Allah SWT ya kuma kawo bayanin yadda wannan yarinya ta tashi a Surat Aal<br />

Imran aya ta 37:<br />

" Allah SWT ya karbi wannan yarinya ta hanya wace take mafificiya, kuma ya<br />

rayar da ita akan tafarkin mafifici, ya damka ta a bisa kulawar Zakariyya'. Duk<br />

lokacin da Zakariyya' ya je wajen ta a masallaci sai ya gani tana da abnci ( da


dama na kowane irin yanayi) sai ya ce ya Maryam! Daga ina kika kika kawo<br />

maki? Sai ta ce daga Allah, yana bayarwa da dama ga wanda yake so". Wannan<br />

ne yasa Zakariyya yaga ya dace ya roki Allah SWT ya bashi da, tunda bashi da da<br />

ga shi kuma tsufa ya zo mashi. Ya gane cewa tunda Allah SWT zai samarwa<br />

wannan yarinya abinci na kowane irin yanayi da yawa, to zai iya bashi da duk<br />

kuwa da tsufan shi. Addu'ar shi an yi bayanin ta a Surat Aal Imran aya ta 38:<br />

" Sai Zakariyya yayi addu'a ga Allah yace " Ya Ubangiji na, ka bani da wana yake<br />

salihi, hakika kai mai jin addu'a ne".<br />

Yana da ban sha'awa an sa a Musulnci mutum yayi aure ba domin kawai ka haifi<br />

'ya'ya ba, har ka tarbiyyantar da su su kasance salhai a bisa tafarkin addinin<br />

Musulunci da koyarwar sa. Shine dalilin da ya sanya Annabawa kamar su<br />

Zakariyya da Ibrahim AS suka yi addu'a a basu 'ya'ya a lokacin da suke tsofaffi,<br />

saboda 'ya'ya na gari domin su ci gaba da aikin Allah SWT ko bayan mutuwar su.<br />

Allah SWT ya karbi wannan addu'a ta Zakariyya kamar yadda aka yi bayani a aya<br />

ta 39, Surat Aal Imran:<br />

" Sai Mala'ika ya kira Zakariyya a yayin da yake addu'a a masallaci. Allah yana yi<br />

maka albishir da da ana kiran shi 'YAHYA' wanda zai zo ya jaddada kalmomin<br />

Allah. Yahya zai kasance mai matsayi a wajen Ubangiji kuma Annabi jaddada<br />

gaskiya".<br />

Muna iya ganin cewa addu'ar mutum tana iya kasancewa karbabbiya wajen Allah<br />

SWT idan yana sallah a masallaci. Allah SWT yana gwadawa mutane na kowane<br />

karni tunda zai iya ba Zakariyya da lokacin da ya tsufa tukuf. Haka nan kuma<br />

yana iya baiwa Maryam duk da cewa babu wani mahaluki da ya taba taba ta.<br />

Zakariyya yace da Allah SWT, suratu Aal Imran, aya ta 40-41:<br />

" Sai ya ce " ya Allah yaya zan yi in sami da bayan da tsufa ya baibaye ni kuma<br />

mata ta bakararra ce?" Mala'ka ya ce " haka yake, Allah yana yin abinda ya so".<br />

Zakariyya ya ce " ya Allah ka bani wata alama". Mala'ika yace " alamar ka itace;<br />

ba za ka iya magana da kowane irin mahaluki ba, sai bayan kwana uku, sai dai<br />

da nuni. A wannan lokaci kayi tasbihi ga Allah safiya da marece".<br />

Bari kuma mu ga yadda Musulmi suke daukar Maryam a lokacin da ta kasance<br />

cikakkiyar mutum. Allah SWT ya ce a cikin Surat Aal Imran aya ta 42-43:<br />

" Da mala'aka ya cewa Maryam Allah ya zabe ki, ya tsarkake ki daga (bata) ya<br />

zabe ki sama da dukkan mata da ke a doron kasa da kuma aljannu. Ya Maryam!<br />

Ki kasance mai biyayya ga Ubangijin ki, ki kame kan ki, kiyi sujada tare da wanda<br />

suke yin sujuda wajen bauta".<br />

Mun gane cewa idan Allah ya kara ma kyauta ya kamata ya kamata ya kara mika<br />

wuya ta wajen yin salloli. Umunin yin sujuda ya gwada cewa an fi son ayi salla a<br />

cikin jam'i. Mala'ika sai ya kara cewa Maryam, Aal Imran aya ta 45-46:


" (tuna) Yayin da Mala'ika ya ce " Ya Maryam ! hakika Allah ya yi maki<br />

kyakykyawan albishir da da daga gare shi, sunan shi Isa dan Maryam. Amintacce<br />

a nan duniya da kuma lahira, daya daga wadanda suke da kusanci da Allah SWT.<br />

Wannan yaro zai yi magana da mutane a cikin dan-goyon shi. Idan kuma ya kai<br />

munzalin cikakken mutum zai kasance daga cikin masu gaskiya".<br />

Maryam sai ta cika da mamaki, sai ta ce : Aal Imran, aya ta 47:<br />

" ta ce " Ya Allah ! yaya za a ayi in sami da bayan da babu mahalukin da ya taba<br />

ni" sai ya ce " haka yake ! wajen Allah, yana halittara abinda ya ga dam, idan<br />

yace da abu ya zama sai ya zama".<br />

A nan, haihuwar Isa an yi ta ne kawai da kalmar Allah SWT wanda aka samu<br />

tabbaci daga Yahya AS. Karin dadawa, a bayyane yake karara haihuwar Isa AS ta<br />

faru ne inda babu mahalukin da ya taba taba Maryam.<br />

Al Qur'ani yayi bayanin yadda Maryam ta dauki ciki da tayi da kanta lokacin da<br />

tana da ciki. Suratu Maryam Allah SWT ya ce , aya ta 16-26 :<br />

" An yi bayani a cikin littafi (Al Qur'ani) Maryam. Lokacin da ta fita daga mutanen<br />

ta, zuwa wani dakin da ke dubar gabas, ta zama ta kaurace daga gare su. Sai<br />

muka turo mata Ruhin Mu (Mala'ika) ya zo mata tamkar wani mutum. Sai ta ce<br />

dubi ! ina neman tsari wajen mai rahma daga gare ka idan kana tsoron Allah".<br />

Mala'ika yace " Ni kawai manzo ne na Allah, za a baki da wanda yake salihi".<br />

Maryam tace " yaya za a yi in sami da tunda babu mutumin da ya taba taba ni,<br />

kuma ban kasance ba mai tsarki ba". Mala'ika yace " Allah ya ce abu ne mai sauki<br />

gare shi, haka zai kasance tunda abinda ya nufa ke nan. Allah zai maida shi wata<br />

alama ga mutane da jin-kan shi. Maryam ta tafi wani waje mai nisa. Lokacin da<br />

ciwon nakuda ya kai ta a gindin wani dabino, sai ta ce " Kash, na gwammace ma<br />

in mutu a kan wannan in kasance wani abinda za a manta da shi". Sai wani yayi<br />

magana ta kasan ta yace " kada ki damu! Allah ya sanya a kasar ki. Ki<br />

girgiza gindin itaciyar nan nunannun dabino za su fado maki, ki ci ki sha ki<br />

kwantar da hankalin ki. Idan kika gamu da wani mutum, ki ce " ina yin azumi ne<br />

ba zan yi zance da kowane mutum ba".<br />

Mun ji an ce Maryam ta girgiza itaciyar dabino ta sami nunannun dabino. Wannan<br />

yana koya mana mu yi bakin kokarin mu mu sami na kan mu. Wannan kokari ba<br />

wai kin yarda da Allah ne ba.<br />

Bayan kwana arba'in, Maryam ta koma ga mutanen ta da dan ta a hannun ta.<br />

Yadda al'amarin ya kasance tsakanin ta da mutanen ta an yi bayanin shi a Surat<br />

Maryam aya ta 27-32:<br />

" Sai ta kawo shi zuwa ga mutanen ta tana dauke da shi, sai su ka ce "Ya Maryam<br />

kin zo da abin mamaki. Ya ke yar uwar Haruon, baban ki ba mugun mutum ne ba<br />

haka nan babar ki ba karuwa bace". Sai ta nuna shi, sai suka ce to yaya zamu yi


magana da wanda ke cikin magoyi yaro karami". Sai Isa yace " ku sani ni bawan<br />

Allah ne, ya bani littafi, ya nada ni Annabi, ya albarkace ni a duk inda na ke, ya<br />

umarce ni in yi salla da bayar da zakka in har ina da rai. Allah ya umar ce ni da in<br />

yi biyayya gare ta wadda ta haife ni, bai maida ni ba mai girman kai maras<br />

albarka".<br />

A abinda aka gutsuro, kalma ta farko wanda Isa yayi shine 'bawan Allah', don<br />

haka, bai kasance ba abokin tarayya a kowane lokaci. Abu na biyu sallah zakka<br />

dole ga kowace irin alu'mma dole mutane su cika wannan umarni idan har sun<br />

kasance rayayyu.<br />

Mun ga Maryam tana jaririya, yadda ta tashi, kasancewar ta cikakkiyar mace,ta<br />

kuma uwa. Akwai almomi na shiryiwa ga Allah SWT ga wadanda suke neman<br />

yardar Allah. Maryam tana da banbanci da Maryam wacce kiristoci suke<br />

gwadawa.<br />

Allah SWT ka tsare daga kowace iri shirka, mai sai mu bayi masu biyayya, Amin.<br />

WASIYYAR ANNABI MUHAMMAD SAW ( KASHI NA FARKO)<br />

Allah SWT ya ce a cikin Surat al An'am aya ta 151:<br />

" ka ce zo, zan karanta maku abinda Ubangijin ku ya haramta a kan ku : kada ku<br />

hada shi da wani, kuma ku kyautatawa mahaifan ku, kada ku kashe 'ya'yan ku<br />

saboda talauci, mu ke ciyar da su (yaran) da ku, kada ku kusanci abubuwa<br />

marasa kyau ko a bayyane ko a boye. Kada ku kashe rai wadda Allah SWT ya<br />

haramta (tsare) sai da gaskiya, da wannan ne ya umarce ku ko kun fahimta.<br />

Wannan ya umarce ku ko da kun fahimta".<br />

Wannan aya da ayoyi biyu bayan ta sun yi amfani da kalmar wasiyya sau ukku a<br />

wata fadar kuma Allah SWT yana umartar mu ko jaddada mana mu bi wadannan<br />

ka'aidoji.<br />

An fada a cikin tafsin Ibn Katheer cewa Abdullah Bn Mas'ud RA yace idan wani<br />

yana so ya ga wasiyyar Annabi Muhammad SAW da hatimi a jiki to ya karanta<br />

wadannan ayoyi wadanda ya barwa al'umar shi.


Haka nan ya rubuta cewa Ubaadah Bn As Samit RA ya ruwaito cewa Annabi SAW<br />

ya taba yi wa sahabbai bayani cewa kowa zai yi mashi alkawali akan wadannan<br />

ayoyi guda uku. Annabi SAW ya kara da cewa duk wanda ya cika alkawalin ladar<br />

shi tabbatacciya ce a wurin Allah.<br />

A wannan ayoyi abubuwa daban daban an kira su HARAM. Ta yadda Al Quar'ani<br />

ya fiti abin yana gayyato tunda yana umarni ne ya fara da kalma zo. Barin in fada<br />

maka kamar wani yana gayyatar wani daga wani wuri mai tsawo domin ya daga<br />

mai saurare na sama da gaba sama can. Ya ce " bari fada maku abinda Allah SWT<br />

ya haramta maku". Yana jaddadawa kada ka aikata haram a kan ka. Bayan<br />

wannan bayani na bai-daya, ko wace haram an bayyana ta da ban.<br />

- Abu na farko, kada ka hada Allah da wani. Ana yin shirka ta bangarori da dama.<br />

- hada Allah da wani kamar yadda yahudawa da kiristoci su ke yi.<br />

- Duk da yadda cewa Allah SWT yana yin komi amma ka dauka cin ma wata<br />

nasara akan rayuwa bisa wasu abubuwa na harkoki.<br />

- Ka yi addu'a amma kada ka sare.<br />

- Ka ciyar domin Allah SWT domin samun wani matsayi.<br />

Annabi Muhammad SAW yace " babu abinda zai cutar da ku ba tare da yardar<br />

Allah ba SWT.<br />

Shirka an fara ambaton ta saboda ita ce mafi girman laifi, Allah SWT baya yafe ta<br />

har abada.<br />

Ubbada Bn Samit da Abu Darda' sun ce Annabi Muhammad SAW<br />

Yace " kada ka hada Allah da wani ko da za a rataye ka ko kuma za a kona ka da<br />

ran ka".<br />

Na gaba, an yi mana umarni mu kyautatawa iyayen mu. Yana da ban-sha'awada<br />

an ce " kada ku ki biyayya ga iyayen ku". Amma fuskanta ta Al Qur'ani yana da<br />

ban sha'awa. Allah SWT yace ba wai ku yi biyayya amma ku kyautata masu<br />

domin su ji dadin ku. Allah SWT ya kara cewa :<br />

" Ku kasance masu biyayya gare su".<br />

Allah ya sake cewa: " Ubangijin ku ya yanke wannan shawara domin kada ku<br />

bautawa wani ba shi ba, kuma ku kyautatawa iyayen ku".<br />

A cikin Surat Lukman aya ta 14, Allah SWT ya ce " ku gode mani da iyayen ku,<br />

saboda za ku dawo gare ni".<br />

A wata fadar kuma, Allah SWT yace idan baka gode mashi ba kuma iyayen ka za<br />

a azabtar da kai idan ka koma gare sh. A dukkan wadannan ayoyi, hakkin iyaye<br />

an sanya shi bayan hakkin Allah SWT. Hakkin iyaye yana da muhimmanci a<br />

wurin Allah.<br />

Abdullah Bn Masuud RA ya ce na tambayi Annabi SAW " wane aiki ya fi ?" sai ya<br />

amsa mani " yin sallah cikin lokaci". Sai na tambaye shi "sai me?" yace


"kyautatawa iyaye". Na tambaye shi " Sai me ?" ya ce " kayi yaki ta hanyar Allah<br />

SWT. (Saheehan)<br />

Abu Hurairah RA ya ruwaito cewa wata rana Annabi Muhammad SAW<br />

Ya ce har sau ukku " Ya halaka", sahabbai suka tambaya " Ya manzon Allah<br />

wanene ya halaka? Sai ya ce wanda duk ya riski iyayen shi sun tsufa amma bai<br />

shiga aljanna ba.<br />

Wanna yana nufin idan wani yayi dawayiniya da iyayen shi cikin kwanciyar<br />

hankali, an yiwa wannan mutumen alkawalin shiga aljanna.<br />

A gaba, Allah SWT ya yi bayanin damar 'ya'ya. Allah SWT yana umartar mu kada<br />

mu kashe 'ya'yan mu domin jin tsoron talauci. Allah SWT zai ba su kamar yadda<br />

ya ke baku. A cikin Surat Al Isra', Allah SWT ya ce : " Muna bayar gare su da<br />

kuma ".<br />

A nan ana gwadawa 'ya'ya wadanda suke masu rauni wadanda suke basu iya<br />

daukar dawainiyar kan su sun fi dacewa a basu fiye da ku. Haka nan Allah SWT<br />

yana budawa gare ku domin su, su wata rahama ce a gare ku, don haka wata<br />

larura ba ce. Subhanallah.<br />

Dubi yadda iri zai girma ya zama itace ya rika samar da 'ya'ya, iyaye ba su yin<br />

wani abu da zai girma, Allah ne ya ke yi. Ta wannan hanya ne Allah zai samar<br />

maku da kyauta wanda babu iyaka ta hanyoyi da ba ku sani ba. Idan ba mu<br />

baiwa diyan mu ba ilmi da tarbiyya ta addinin Musulunci ba mun kashe su.<br />

Saboda Alqur'ani yana kiran irin wadannan mutanen matattu wanda bai ba bin<br />

Allah SWT muhimmanci ba. A nan wadanda suka kauda kai daga baiwa diyan su<br />

ilmi da tarbiyya ta addinin Musulunci suke da hakkin kashe diyan su. Kisa kisa na<br />

rashin bin shiriya ya fi kisa domin wani abin duniya. Zunuban da diya suka aikata<br />

saboda rashin bin tafarkin shiriya kwata kwata ya lalata masu rayuwa.<br />

Allah SWT ya umarce mu kada mu kusanci abubuwa wadanda basu da kyau a<br />

bayyane ne ko a boye. Abubuwa na bayyane suna nufin da harshe ne ko hannu<br />

ko kafa da dai ire-iren su. Abubuwa na boye suna nufin bakin-ciki, muguwar<br />

sha'awa, rashin godiya da rashin hakuri. Har wa yau, ayyuka na bayyane suna<br />

nufin kamar dubar mace da mugun tunani, taba ta da hannu ko yin Magana da ita<br />

da mugun nufi. Kuma abubuwa na boye suna nufin yin wani abu a suturce domin<br />

aikata abubuwan da aka ambata a sama. Annabi Muhammad SAW ya hane mu<br />

kada mu yi kutse abinda bamu da tabbas ko gonar da ba tamu ba zai kai mu ga<br />

halaka.<br />

Annabi Muhammad SAW ya ce:<br />

Duk wanda yayi shawagi a wuraren da aka haramta mashi, yana iya kasancewa<br />

ya shiga wannan .<br />

Allah SWT yana umartar mu kada mu kashe wanda aka haramta mana mu kashe.


Abdullah Bn Mas'uud ya karbo daga Annabi Muhammad SAW yace " ba a yarda<br />

ba a kashe daya daga cikin Musulmi sai a bisa wadannan dalilai:<br />

· Mutum mai aure da ya aikata zina.<br />

· Wanda ya kashe wani haka nan.<br />

· Wanda yayi ridda bayan ya karbi musulunci.<br />

Bukhari da Muslim.<br />

Halifa Usman RA ya tunatar da mutanen da mutanen da suka zo kashe shi<br />

wannan Hadisi.<br />

Haka nan kuma kashe wanda ba musulmi ba haka nan kawai ba a yarda ba a<br />

Musulunci.<br />

Abu Hurairah ya karbo daga Annabi Muhammad SAW yace " Duk wani wanda ya<br />

kashe wanda ba Musulmi ba a kasar Musulmi ya karya alkawarin Allah SWT. Duk<br />

wanda ya karya alkawarin Allah bai zai ji kamshin aljanna ba duk kuwa da ana jin<br />

shi tafiyar shekara ashirin.<br />

Wannan shine umarnin Allah SWT gare mu.<br />

Ina rokon Allah ya bamu ikon bin wannan umarni kuma bisu kamar yadda ya<br />

dace, Ameen.<br />

WASIYYAR ANNABI MUHAMMAD SAW ( KASHI NA biyu)


Allah SWT a cikin surat Al an'am aya ta 152-153 ya ce:<br />

Kada ku kusanci dukiyar maraya sai adi da abinda ya ke mai kyau, har sai ya<br />

balaga. Ku bayar da cikakken awo da cikakken ma'auni cikin adalci. Kada mu yi<br />

harajin da ya zarce iyaka. Idan ka yi Magana ka yi adalci a kan ta ko da ba a bisa<br />

son ran mutane ba. Kuma ku cika alkawalin Allah. Shine ya umarce ku ko da kun<br />

tuna shi. Allah SWT ya sake umarta cewa : wannan ita ce mikakkiyar hanya ka<br />

bita kada ka bi sauran hanyoyi ko ka yaudare daga hanayar sa. Allah ya yi maku<br />

haka don ku yi imani.<br />

Da farko, an umarce mu kada muci kayan maraya dake a ajiye a wajen mu, mu<br />

ba su dukiyar su idan sun mallaki hankalin su. Kamar yadda Imam Abu Haneefa<br />

yace mu dakata har sai maraya ya kai munzalin da zai iya jibintar al'amarin shi.<br />

Kuma mu mayar masu kafin marayan ya kai shekara 25, sai dai idan ba shi da<br />

cikakken hankali. Wadansu malaman kuma suka ce a mayar da dukiyar a kotu<br />

ita kuma ta nada wani amintaccen mutum ya kula da ita.<br />

Allah SWT ya ce : " idan shekarun maraya sun kai kuma yana kuma yana jibintar<br />

al'amuran shi to ku bashi dukiyar shi".<br />

A nan muna iya yanke hukuncin cewa cikar shekaru bai isa ba, amma karfin<br />

jibintar al'amura yana da muhimmanci. Allah SWT ya sake cewa : " wadanda<br />

suke cin dukiyar maraya suna cika cikin su da wuta ne".<br />

A nan, Allah SWT har wa yau ya umarce mu da mu bayar da cikakken awo da<br />

cika ma'auni. Mutanen Annabi Shu'aib an dirkake su ne saboda kin bin wannan<br />

umarni. Akwai gargadi mai tsanani a cikin Al Qu'rani mai girma a kan wadanda su<br />

ke tauye ma'auni. Ka sani fa kin yin adalci a kan aikin ka shima tauye ma'auni ne.<br />

A nan mutum yayi kokari iyakar iyawar shi, duk abinda ya wuce iyawar shi ba<br />

matsalar shi bace. Sa'id Bn Qais ya ji da ga Annabi Muhammad SAW cewa " auna<br />

kuma ka kara abinda yafi".<br />

Abu Dawoud da Tirmidhi<br />

Jaber yaji daga Annabi Muhammad SAW yace " jikan kan ya kasance a kan<br />

mutumin da yake da sassauakar zuciya a wurin cininki kuma yana bada kadan da<br />

ya zarce abinda ake bukata, da kuma mai saye wanda yake da sassaukar zuciya<br />

wanda zai karba koda ya gaza kadan".<br />

Bukhari.<br />

A gaba, Allah SWT ya umarce mu idan za mu yi Magana mu fadi gaskiya ko da<br />

kuwa ga 'yan uwan mu ne na kusa. Annabi Muhammad SAW ya ce shaidar zur<br />

kamar hada Allah da wani ne " har sai da ya maimaita sau uku sa'annan ya<br />

karanta wannan ayar:<br />

Ka tsare kan ka daga bautar gumaka da shaidar zur da hada Allah da wani"<br />

Abu Dawoud da Ibn Majah


Burraida ya ruwaito cewa Annabi Muhammad SAW ya ce " alkalai iri uku ne, daya<br />

zai shiga aljanna sauran biyun kuma za su shiga wuta. Wanda yayi bincike akan<br />

abinda aka kawo gaban shi a kan koyarwar Islama yayi kokari ya gano gaskiya<br />

kuma ya zartar da hukunci na gaskiya zai shiga aljanna. Wanda kuma ya gano<br />

gaskiya ta hanyar sani da bincike amma kuma sai ya yi hukunci ba daidai ba zai<br />

shiga wuta. Haka kuma wanda ba shi da ilmi ko yin bincike da ya dace a kan<br />

al'amarin kuma ya yanke hukunci cikin rashin sani shine zai shiga wuta.<br />

Al Qur'ni ya shiryar da mu akan yin shaida : " ka fadi gaskiya da a kan ka ne ko<br />

iyayen ka ko yan uwan ka".<br />

Musulunci yana da cikakkiayar da'a. Allah SWT ya ce :<br />

" Zamantakewa kada ta hane ku daga shaida ta gaskiya da zartar da abu kamar<br />

yadda ya ke".<br />

A nan an shawarce mu bi a sannu ko da a huldayyar mu ta yau da kullum ce, da<br />

hirar bai kamata ba mu yi karya, yi da wani ko kuma mu fadi abinda zai cutar da<br />

wani ko jawowa wasu asarar kudaden su.<br />

Allah SWT ya umarce mu mu cika alkawali. Allah SWT ya ce a cikin surat Al<br />

Baqarah aya ta 177:<br />

" Ma su imani na gaske suna cika alkawali idan sun yi".<br />

Yana da ban-sha'awa mu sani cewa wannan ayar ta na cewa ya kamata ya zame<br />

hali na wadanda suka yi imani su cika alkawali tunda wadanda ba su yi ba imani<br />

kan cika alkawalin su.<br />

Haka nan kuma Allah SWT ya ce a cikin Surat Al Ma'arij aya ta 32:<br />

Alamar muminai na gaskiya shine :<br />

" Suna da rikon amana da alkawali".<br />

A karshe Allah SWT ya na ce mana wannan ita ce mikakkiyar hanya ta don haka<br />

ku bi ta, kada ku bi sauran hanyoyi tunda za su kawar da ku daga hanyar Allah.<br />

Abdullahi dan Mas'uud RA ya ruwaito cewa : wani lokaci Annabi Muhammad SAW<br />

ya zana wani mikakken layi ya ce " wannan ita ce hanyar Allah SWT. Sai ya sake<br />

zana wadansu layika a jikin wannan ya ce "Wadannan su ne 'Subul', shaidan yana<br />

a dukkan wadannan layuka yana kokarin ya kawadda mutane daga hanyar Allah<br />

SWT. Annabi Muhammad SAW sai ya karanta aya daga cikin Surat Al An'am<br />

kamar yadda aka yanko daga farko.<br />

Za mu takaice ta kuma mu yi cikakken lura a kan wadannan ayoyi guda uku na<br />

surat Al An'am.<br />

Aya ta farko: ya yi bayani akan rukunnai guda biyar :-<br />

· Kada ka hada Allah SWT da wani.<br />

· Yin biyayya ga mahaifa.<br />

· Kada ku kashe diyan ku.


· Ku tsare daga munan dabi'u.<br />

· Kada ku kashe wani da gangan.<br />

Sai Allah SWT ya ce " saboda ko kun fahimta". Tunda wadannan ba a dauka ba<br />

wani mummunan abu kafin zuwan Musulunci. Allah SWT yana bamu shawara mu<br />

bar wadannan dabi'u na jahiliyya, ku koma cikin hankalin ku.<br />

Aya ta biyu, tana bayanin akan rukunai guda hudu :<br />

· Kada ku ci kayan maraya.<br />

· Kuyi awo daidai.<br />

· Ka fadi kuma ka tsaya a kan gaskiya.<br />

· Ka cika alkwali.<br />

Wadanna abubuwa hakikanin gaskiya ne kowa zai iya ganin kyawun su. Mafi<br />

yawancin mu ba mu da wadannan abubuwa ba. Maganin wannan rashin damuwa<br />

shine tunatarwa, shine a karkashin wannan aya Allah SWT ya ce :" ko da wannan<br />

shiriya ta zame maku tunatarwa".<br />

Aya ta uku.<br />

Aya ta uku an ce mu bi hanya madaidaiciya mu guji sauran hanyoyi. Wannan ba<br />

ya samuwa sai ana tuna Allah SWT kuma ana kokarin cikakken imani. Kuma a<br />

cikin wadannan ayoyi akwai rukunai guda goma. Wadannan ayoyi guda uku sana<br />

da muhimmaci. Ka'bul Ahbar RA shi bayahude ne masanin At Taurah. Ya ce<br />

bayan ya karbi Musulunci : " At Taurah ta fara da wadannan rukunnai guda goma<br />

wadanda aka ambata a cikin Al Qur'ani a cikin wadannan ayoyi guda uku.<br />

Wadannan su ne rukunnai guda goma da aka saukarwa Annabi Musa AS.<br />

Abdullahi dan Abbas RTA ya ce "wadannan sune bayyanannen wahayi wanda aka<br />

ambata a cikin Surat Aal Imran. Har wa yau, duk wasu tsare-tsare tun daga kan<br />

Annabi Adam AS zuwa Annabi Muhammad SAW duka sun kunshi wadannan<br />

rukunai guda goma babu inda aka goge su a kowace irin Shari'a.<br />

A tafsirin Ibn Katheer an tuwaito daga Abdullah Bn Mas'ud RA cewa idan wani<br />

yana son ya ga wasiyyar Annabi Muhammad SAW an danbara hatimi a jikin ta to<br />

ya karanta wadannan ayoyi guda uku na Surat Al An'am.<br />

Haka kuma Hakam yayi bayanin ta kamar yadda aka ruwaitodaga Ubbadah Bn<br />

Samit cewa wata rana Annabi SAW ya yiwa sahabban shi Bayani yace " wa zai yi<br />

mani alkawali akan wadannan ayoyi?" sai ya karanta wadannan ayoyi guda uku<br />

na suratul An'am, daga nan sai yace " duk wanda ya cika alkawalin shi ya<br />

tabbatar da ladar shi a wajen Allah SWT.<br />

Ina rokon Allah SWT ya bamu ikon bin wasiyyar Annabi Muhammad SAW.


CIYARWA TA HANYAR ALLAH (SWT)<br />

Ciyarwa ta hanyar Allah yana daga cikin halayya mai muhimmanci ta wadanda<br />

suka yi imani na gaskiya. Allah SWT bai umarce mu ba kawai har ma ya<br />

kwadaitar da mu ta haya mai kyau. Misali, Allah SWT yace a ciki Surat Al<br />

Baqarah aya ta 265:<br />

" Kamanni wadanda suke ciyarwa a dukiyoyin su domin neman yardar Allah da<br />

kuma tabbatar da kawunan su, kamar lambu ne wanda yake a jigawa idan ruwa<br />

ya sauka a kan shi sai ya samar da 'ya'yan itace launi biyu, idan kuma ruwa bai<br />

sauka a kan shi ba ko da yayyafi ma ya isa. Allah yana ganin abinda kuke yi".<br />

Yana da sauki ka yi Magana a kan ciyarwa domin Allah, amma yana bukatar<br />

karfin hali kafin ka aiwatar da hakan. Saboda haka ciyarwa domin Allah yana<br />

mikar da rai da halayyar mutum. Karin dadawa, ka ciyar da wani abu kalilan<br />

wanda za ka yi da zuciya daya ya isa ya samar da lada babba a wajen Allah.<br />

A aya ta 7cikin Suarat Al Hadeed Allah SWT ya kwadaitar damu a kan wata<br />

hanyar da ban. Ya ce:<br />

" ka yi imani da Allah SWT da Manzon Shi kuma ka ciyar da abinda Allah ya<br />

maida mai tsaro".<br />

A nan, Allah SWT yana bayyana mana cewa duk wani abu da muka mallaka wani<br />

ya same shi kafin mu. Haka nan duk abinda muka mallaka zai kasance mallakar<br />

wani bayan mu. Don haka, muna ajiye da ita ne na wucin-gadi ko masu rike da<br />

amana. Don haka kada muyi wata wata wajen ciyar da abinda yake a gare mu na<br />

wucin gadi.<br />

Na biyu, a bayyane yake cewa sai wadanda suke da imani suke ciyarwa ta hanyar<br />

Allah SWT za su sami gagarumar lada daga gare Shi. Muna iya yanke hukunci<br />

wanda bai yi imani ba idan ya ciyar ba shi da lada gobe kiyama, ko da yake zai<br />

sami sakamako a nan duiya.<br />

A surat Al Hadeed, aya ta 10 Allah SWT ya ce :<br />

" Wannan kai komo gare ku wajen ciyarwa saboda Allah SWT bayan duk abinda<br />

yake sama da kasa duk na Allan ne".<br />

Nan wata hanya ce mai ban-sha'awa wadda za ta kwadaitar da mu da shiryar da<br />

mu mu ciyar ta hanyar Allah SWT. Misali akwai wani daga cikin mu da ya mallaki<br />

wani bangare na sama? Hakikanin gaskiya babu. Dukkan sammai na Allah SWT<br />

ne shi kadai. Haka nan kuma a makaman ciyar wannan hanya gaskiya duk abinda<br />

ke a bayan kasa na Allah ne. ko da yake muna yin kuskure mu ce " wannan mota


ta ce, ko gida na ko wannan asibiti na ne. Allah SWT ya kawo kalmar sammai<br />

yana bayyana mana cewa duka abinda yake a sammai na Allah ne kuma duk<br />

abinda ya ke a bayan kasa na Allah ne, don haka kada mu sami wani jimami<br />

wajen ciyarwa ta hanyar Allah SWT daga abinda yake daman can na Allah ne. Sai<br />

Allah SWT ya gayyace mu a Surat Al Hadeed aya ta 11:<br />

" Wa yake da ya ba Allah rance domin ya rubanya mashi kuma ya bashi lada mai<br />

girma bayan shi?".<br />

Me ake nufi da babbar lada 'ajarun kareem'? wannan za a fi fahimtar shi daga<br />

wannan ayar ta Surat an Naba' aya ta 36:<br />

" Akwai lada gare ka daga Ubangiji da Karin lada dangane ga imanin ku".<br />

Rahamar aljannan nesa ta zarce ladar da za a bamu saboda kyawawan ayyukan<br />

mu. A nan kari daga ladar akwai kyau daga wajen Allah SWT girman wannan<br />

kyauta danganta ne a kan imani da niyya. Allah SWT ya banbance ta babbar lada<br />

a bangarori da dama a cikin Al Qur'ani. Za a bamu lada domin ciyarwa don Allah<br />

SWT dagane da imani da niyya.<br />

Anas RA ya ruwaito cewa Annabi Muhammad SAW yace " idan mutum yana da<br />

tafki cike da gold ba zai taba wadata ba. Wannan mutum zai so y asami wani<br />

tafkin cike da gold. A halin gaskiya kurar kabari kadai za ta cika bakin mutum.<br />

Bukhari.<br />

Ubayy Bn Ka'ab RA yace wannan Hadisin an maimaita shi da yawa, mun yi<br />

tunanin wani bangare ne na Al Qur'ni, sai da da aka saukar da Surat at Takaathur<br />

aya ta 1-8 inda Allah SWT ya ce:<br />

" Gasa da juna ta shagaltar da ku har sai kun ziyarci kaburra. Lallai ! za ku sani !<br />

Har wa yau lallai za ku sani ! Lallai idan kuna sane da tabbataccen sani. Hakika za<br />

ku ga wuta ! kuma za ku gan ta da tabbataccen gani !. A wannan rana za a<br />

tambaye ka jin dadin da ka yi a duniya".<br />

Dan Umar ya ruwaito cewa wani lokaci Annabi Muhammad SAW ya yiwa sahabbai<br />

jawabi ya ce " Karanta aya 1000 ta Al Qur'ani a kowace rana" sahabbai suka ce "<br />

wata kila wani wani zamu karanta aya 1000 na Al Qur'ani". Annabi SAW ya ce ba<br />

za ku karanta Surat at Takaathur".<br />

Al mazhari<br />

Yana nufin sakon dake a wannan sura daidai yake da ayoyi dubu. Haka nan rauni<br />

ne na mutum yayi ta tara dukiya har sai mutuwa ta riske shi. A wajibi ne wanda<br />

yayi imani ya biya zakka wadda take 2-1/2 cikin dari na abinda mutum yake<br />

samu. Allah SWT ya fadi zakka da salla a cikin Alqur'ani a mafi yawan lokaci. A<br />

wata fadar sallah ma ba ta rabuwa da zakka. Khalifa Abubakar ya fahimci wannan<br />

sosai. Ya tura runduna ga wanda su ka ki su bada zakka, duk da yake suna salla<br />

suna azumi.


Allah SWT yace a cikin Surat al Muzzammil aya ta 20:<br />

" Ku tsaida salla ku bada zakka ku baiwa Allah rance".<br />

A nan Allah SWT yana shiryar damu, ba wai kawai mu biya zakka ba, mu kara<br />

baya da kyau.<br />

Halayen wadanda suka yi imani na gaskiya an ambace shi a wurare da daman na<br />

Al Qur'ani mai girma. Allah SWT ya ce a cikin Surat az Zariyaat aya ta 17-19:<br />

" Suna yin barci kadan da dare. Kafin dare a kowace rana suna neman gafarar<br />

Allah. Kuma a cikin dukiyar su akwai rabon masakai da fakirai".<br />

Wannan bayyanannen kaso, Allah ya sanya shi a kan zakkah a kowane lokaci 2-<br />

1/2 kan abinda mutum ke da shi.<br />

Allah SWT ya sake cewa a surat al Insan aya ta 8-9:<br />

" Suna bayar da abinci ga mabukata, maraya da yan kaso, domin samun soyuwa<br />

a wurin Allah kadai. Bamu bukatar wata lada ko godiya daga gare ku".<br />

Wani lokaci sai mu yi tunani ko me yasa Allah SWT ya maida Annabi SAW<br />

maraya?. Allah SWT shine mafi sani, wata kila dalili daya yana iya kasancewa<br />

Allah SWT yana so ya gwadawa Annabi SAW yadda rayuwaar maraya take.<br />

Wannan wani koyami ne ga wanda zai kasance rahma ga dukkan duniya.<br />

Sahabban Annabi SAW sun sami wata irin shiriya daga Allah SWT. Misali ka tuna<br />

aya ta 92 a Surat Aal Imran :<br />

" Ba ka samin taqwa ta gaskiya har sai ka ciyar da abinda kafi so".<br />

A lokacin da Abu Talha ya saurari wannan ayar, sai ya rugo wajen Annabi SAW<br />

ya bada kambun binshi wanda ya fi kyauta. Haka nan, kuma Zaid bn Haris ya<br />

bayar da dokin shi wanda ya fi kyauta.<br />

Ina rokon Allah SWT ya bamu ikon bada zakka da sadaka da zuciya daya ko da<br />

yaushe, Amin.


HALAYEN WADANDA SUKA YI IMANI<br />

Allah SWT ya ce a surat al Jinn aya ta 14 :<br />

" Duk wanda ya karbi Musulunci hakika ya zabi hanya madaidaiciya".<br />

Ko bayan daukar wannan mataki na gaskiya Musulmi ba zai ce ba zai shiga<br />

aljanna kamar yadda yahudawa da kiristoci su ke ikirari. Shiga aljanna ya<br />

kasance ne kawai ta rahmar Allah SWT. Allah SWT ya yi bayani game da mutanen<br />

gidan aljanna a aya ta 107 surat Aal Imran :<br />

" Ga wadanda fuskokin su za su kasance farare, suna a cikin rahmar Allah<br />

(aljanna) nan za su dawwama har abada".<br />

A nan kalmar rahma an yi amfani da ita ne a maimakon aljanna yana tunatar da<br />

mu cewa shiga aljanna sai da rahamar Allah SWT.<br />

Allah SWT har wa yau yana shiryar da mu a cikin Al Qur'ani a kan halaye da<br />

dama na mutane wadanda za su cancanci shiga aljanna. Wadannan halaye an<br />

bayyana su a cikin surat Al Mu'minun da surat al Ma'arij. Za mu bi surat Al Ma'arij<br />

aya ta 19-21.<br />

Tun farko, Allah SWT yayi jawabi ga daukacin al'umma.<br />

Allah SWT ya ce : " Mutane da dama basu da hakuri. Idan suka gamu da<br />

wadansu matsaloli sai su dimauce, idan Allah ya sauya masu wannan matsi da<br />

abu mai kyau sai su ki cika damar mutane da damar Allah".<br />

To a nan anyi zabe daga wadannan, akwai nau'in wasu mutane na musamman da<br />

ba su yin haka halayen shine aka yi bayanin su a surat al Ma'arij aya ta 22-25:<br />

" Wadannan suna tsayar da sallah, wajen yin salla suna yin ta a kan lokaci cikin<br />

nutsuwa. Na biyu suna ciyar da wani bangare na dukiyar su ga masakai da<br />

marasa karfi".<br />

Da ban-sha'awa mu sani Allah SWT ya tabbatar da cewa suna kyautatawa<br />

mabukata. Allah SWT ya sake cewa wadannan masu imani suna ciyar da wani<br />

kayyadadde lissafaffen bangare na dukiyar su ga mabukata da matalauta. Ko<br />

kuma a ce koda yaushe suna bayar da zakka wanda aka kayyade biyu da rabi a<br />

kowane lokaci. Sayyidina Abubakar RA ya fi kowa fahimtar wannan ayar ta tura<br />

wata runduna su je su murkushe wadanda su ka ki su bayar da Zakka duk da


yake sun tsaida salla. An ce sallar mutum ba za ta karbu ba har sai ya bada<br />

zakka. Shine ya sa Allah SWT ya ambace salla da zakka tare a cikin Al Qur'ani a<br />

mafi yawan lokaci. Allah SWT ya kara shiryar da mu cewa mu bada kyauta kari a<br />

kan bada zakka a cikin ayoyi masu yawa na Al Qur'ani. Surat al Muzzammil aya<br />

ta 20:<br />

" Ku tsaida salla ku bada zakka kuma ku baiwa Allah rance mai kyau".<br />

Halaye na gaba na wadannan zababbun mutane shine yin yarda da ranar Hisabi,<br />

ba wai a baki ba, su na sane za su kididdiga ayyukan su a ranar hisabi. Misali,<br />

wadannan mutane su ne wadanda za a basu sakamakon su a hannun dama a<br />

ranar hisabi, za su ce sirrin nasarar su shine surat al Haqqah aya ta 20:<br />

" ko da yaushe mu na rayawa a ran mu za mu ga sakamakon mu".<br />

Surat al Ma'arij aya ta 26,27,28:<br />

" Kuma wadanda suka yi imani da ranar sakamako da wadanda suke tsoron<br />

azabar Allah. Hakika! Azabar Allah ita ce wadda babu wanda ya tsira".<br />

A nan, halaye na gaba na wadanda suka yi imani shine suna jin tsoron azabar<br />

Allah. Lokacin da sahabbai suka saurari wannan ayar suka tambayi Annabi<br />

Muhammad SAW " Ya Annabi SAW, kai ma kana jin tsoron azabar Allah? Sai ya<br />

amsa "e! ni ma ina jin tsoron azabar Allah tunda babu wanda zai dauki kan shi ya<br />

fi karfin azabar Allah".<br />

Har wa yau, babu wani musulmi da zai bugi gaba yayi alfahari a kan ayyukan shi<br />

na Musulunci sai dai yayi kuma ya ji tsoron azabar Allah. A gaba, Allah SWT ya<br />

ce, suratul Ma'arij aya ta 29-31:<br />

Halaye na gaba na wadannan mutane shine : " Suna kamewa daga sha'awa sai<br />

dai ga matan su da wadanda aka kamo a wajen yaki. Basu da wani laifi a nanj.<br />

Wadannan iyakoki wanda Allah SWT ya sanya, duk wanda ya zarce wannan ya<br />

kasance ya zarce kan iyaka.<br />

Nan duk wani yanayi da mutum bai bi wajen biyawa kan shi bukata idan dai ba<br />

wannan ba ne kwata-kwata baya kan hanya, Allah SWT ya haramta shi.<br />

Allah SWT ya ce a suratul Ma'arij aya ta 32:<br />

Wani halayen wadannan mutanen shine : " Suna tsayar da Magana da alkawalin<br />

su".<br />

Cin amana da karya alkawali manyan zunubai ne.<br />

"Annabi Muhammad SAW ya ce alkawalin wani bashi ne dole ka biya"<br />

Suratul Ma'arij aya ta 33:<br />

" Suna tsayuwa kyam a kan abinda suka shaida".<br />

Wannan yana nufin sun rike a ran su alkawalin da suka yi da Allah SWT yayi da<br />

suka karbi Musulunci :<br />

Alma'arij aya ta 34


" Wanda suke tsare sallar su da kyau".<br />

A nan Allah SWT ya ce wadannan mutane suna da cikakkiyar nutsuwa wajen<br />

sallar su kuma suna yin ta da farillai da sunna.<br />

Yana da ban-sha'awa Allah SWT ya fara wannan halaye da yin sallah kuma ya<br />

rufe da ita. Wannan ya zamana a bayyane sallah tafi muhimmanci a wurin Allah<br />

SWT. Shine ya sa abinda za a fara tambayar kowa shine salla a ranar hisabi. Al<br />

Ma'arij aya ta 35:<br />

"Allah yana yanke hukunci cewa mutane wadanda suke da wadannan halaye<br />

wanda aka ambata a sama za a girmama su a lambun aljanna"<br />

Wannan ya gwada akwai abubuwa da mutum zai yi ya cancanci shiga aljanna. A<br />

gakiya, idan wani ya aikata abu daya daga cikin wadannan abubuwa yadda ya<br />

kamata duk sauran ma za a iya samara da su a cikin sauki. Idan mutum ya aikata<br />

abubuwan da aka zayyana zai shiga aljanna da rahmar Allah SWT. Allah SWT ka<br />

bamu ikon mu bi wadannan da aka ambata duka cikakke.<br />

Kyauta mafi muhimmanci da Allah SWT ya yiwa mutane shine samar da shiriya<br />

wadda za ta fitar da mu kowane irin duhu zuwa ga haske. Allah SWT ya ce a<br />

suratul Ahzab aya ta 43-44:<br />

" Allah ya saukar da rahamar shi gare ka da kuma Mala'ikun shi domin ya fito da<br />

ku daga tsananin duhu zuwa ga haske. Shi mai rahma ne ko yaushe ga masu<br />

imani. Za a tarye su da sallama idan suka sadu da Allah. Allah ya tanadar masu<br />

lada mai girma".<br />

Allah SWT ya ce da Annabi Muhammad SAW, har wa-yau, aya ta 47:<br />

" Ka yi bushara ga masu imani. Za su sami babbar kyauta daga wajen Allah".<br />

Allah SWT ka sanya mu cikin wadanda za su sami babbar kyauta a wajen Ka,<br />

Amin.


KIBLAH<br />

Me 'Kibla' ta ke nufi? Wajen da ake duba a yi salla<br />

Allah SWT yace a surat al Baqarah aya ta 115:<br />

" Na Allah ne gabas da yamma, duk inda ka juya kan ka ko fuskar ka akwai<br />

fuskar Allah! Hakika, Allah ya isa ga dukkan bukatun ababen halittar sa".<br />

Yana nuna cewa babu wani kebabben bangare wajen bautar Allah SWT daya.<br />

Idan babu wani wuri da aka tsaida Magana ta hakika kowa zai dubi bangaren a<br />

kowane lokaci.<br />

Menene dubarar tsaida Kibla? Mun sani azumi da tuna Allah ayyuka ne na mutum<br />

shi kadai. Salla da aikin Hajji ana yin su ne a taron jama'a. wajen tsaida Kibla,<br />

anyi niyyar a gwada a koyar da da'a da ka'idojin zaman tare. Muhimmiyar ka'ida<br />

da samun hadin kai da sadaukar da kan al'umma shine samun abu daya na inda<br />

suka dosa, wanda ya wuce wani launin fata, kabila, bangare, harshe, da kuma<br />

kasar da ka fito. Allah SWT ya zabi KIBLA domin ya warware wadannan matsaloli<br />

tunda wasu zabi za su kawo rarrabuwar kai maimaikon kawo hadin kan kasa.<br />

Musulunci addini ne na dukkana Annabawa, saboda haka daya bangare daya na<br />

bauta ya gwada kadaitakar koyarwar dukkan Annabawa.<br />

Kasancewar KIBLA daya ga dukkan mutanen duniya ya kawo hadin kai, abu na<br />

bai-daya a tsakanin su. Wannan umarni yana da sauki a bishi ga duk mazaje da


mata, masu ilmi da wadanda ba su da ilmi, na kauye ko na birni, masu arziki da<br />

talakawa. Wannan ya nuna sauki da kyawun Musulunci.<br />

Ka sani fa idan idan aka bar mutane su zartar da an sami gagarumar rashin<br />

jituwa, amma Allah SWT cikin rahamar sa ya zartar da wannan har abada domin<br />

ya taimaka a sami hadin kai kuma ya kawo abu na bai-daya ga kasashen<br />

Musulmi. Lokacin da Adam AS ya zo duniya, fandeshan na dakin Allah Mala'iku<br />

suka yi. Kiblar Adam da mutanen shi ita ce wannan kibla. Allah SWT ya ce a cikin<br />

surat Aal Imran aya ta 36:<br />

" Hakika daki na bauta na farko da aka sanyawa al'umma shine na Bakka<br />

(Makka) ciki da albarka da shiryuwa ga daukacin al'umomi (mutane da aljannu) ".<br />

kowa yana bin wannan kibla ne har lokacin Annabi Nuhu AS, rowan dufana ya<br />

rugurguza a zamanin Annabi AS. Daga baya, Ibrahim da Isma'il AS suka sake<br />

gina ta a bisa umarnin Allah SWT da shiryarwar shi. Wannan kuma ita ce KIBLAR<br />

su tare da mabiyan su. Daga baya kuma aka sanya AL QUDS ga wadansu<br />

Annabawa daga Banu Isra'ila. Wadannan Annabawa idan suna yin salla a kuds<br />

sun kasance suna dubar inda kuds da dakin Allah SWT suna daidaita gaban su.<br />

Har wa-yau, an karbo daga Kurtubi, lokaci da aka sanya sallah farilla ga Annabi<br />

Muhammad SAW da mabiyan shi. Da farko KIBLAR shi ta kasance kamar ta kakan<br />

shi Ibrahim AS. Bayan Hijira zuwa Madina, kuma kamar yadda wasu malamai<br />

suka ce kafin Hijira zuwa Madina Allah SWT ya umarce shi ya dubi Kuds. Annabi<br />

Muhammad SAW ya kasance yana tsayuwa tsakanin Al Hajar Aswad da Rukn Al<br />

Yamani domin duka dakin Allah da Kuds su zamana a gaban shi. Kamar yadda<br />

aka sami Hadisi a Bukhari, Annabi Muhammad SAW ya yi salla a Madina yana<br />

dubar Kuds har tsawon watanni goma sha shida ko sha bakwai. Manzo SAW ya<br />

mika wuya kwata-kwata ga umarni Allah SWT. Sannan sai yayi fata Kiblar shi<br />

zama daya da wadda ta kasance ta Adam AS da Ibrahim AS. Allah SWT yana cika<br />

fatan zababbun mutanen Shi. Annabi Muhammad SAW yana da cikakken fata<br />

wannan guri nashi zai cika, ya kasance yana jiran wahyi yana ta dubar sama sai<br />

Allah SWT ya ce a cikin Surat al Baqarah aya ta 144:<br />

" Hakika mun ga fuskar ka tana dubar sama, hakika zamu juya Kibla ga abinda<br />

ya fi soyuwa a gare ka. To ka juya fuskar ka ga wajen Al masjid Al haram a<br />

Makka".<br />

A nan wajen Allah SWT ya cika gurin Annabi Muhammad SAW. Ka rike fa kalamar<br />

'Shatra' na nufin mutanen da suke yin salla a wasu kasashe su yi bakin kokarin<br />

su su dubi wajen wannan masallaci. Ba wai sai sun daidaita wa daida ba. Amma<br />

kuma wadanda suke ganin dakin Allah dole su duba daidai shi idan za su yi salla.<br />

Tun farkon da yahudawan Madina suka samu cewa Kiblar Musulmi ita ce<br />

masallacin al Haram ba Kuds ba sai suka maida abin barkwanci suna yi masu


dariya. Amma kuma hankalin su ya tashi da wannan sauyi. Amma matukar<br />

Musulmi suna amfani da Kiblar da Yahudawa suke amfani da ita Musulmi sun<br />

sami karbuwa a hannun yahudawa. Amma yanzu an rabu, Kiblar tana nufin<br />

Musulmi sun rarraba, wasu alumma ne da ban. A nan sai yahudawa suka zafafa<br />

adawar su ga Musulmi kuma sun dauke su makiya. Allah SWT ya ce a cikin<br />

Baqarah aya ta 177 :<br />

" Juyar da fuskar ku gabas ko yamma ba shi bane tsoron Allah. Tsoron Allah na<br />

gaskiya shine mika wuya ga al'amarin Allah".<br />

Halayen masallacin Kuds da masallacin Baitul Haram ba wani abu bane illa<br />

martaba da girma da Allah SWT ya basu.<br />

Ko da a cikin Annabawa, Allah SWT ya maida wasu sun dara wasu ta hanyoyi da<br />

dama. Allah SWT ya ce a cikin Surat al Baqarah aya ta 253:<br />

" Wadansu manzanni ! mun fifita wasunsu a kan wadansu ".<br />

A nan wadannan guraren bauta ba su da wani matsayi banda Allah SWT ya sanya<br />

sun zarce wadan su. Allah SWT ya sake cewa a suratul Baqarah aya ta 115:<br />

" Na Allah ne gabas da yamma duk inda ya juya akwai fuskar Allah. Hakika Allah<br />

ya isa ga bukatar ababen halittar shi".<br />

Saboda da haka ba wani waje bane amma gwada da mika wuya ga al'ummar<br />

Allah SWT shine mafi muhimmanci da bin Kibla.<br />

Wanann sauyin Kibla ya dada fiddowa a bayyane masallacin Kuds da masallacin<br />

Kuds da masallacin Baitul Haram ba wasu irin gumaka bane, amma dalili na<br />

hakika shine mika wuya ga al'amurran Allah SWT. Al'amurran Allah SWT za su<br />

kasance kai tsaye ga masallacin Kuds da masallacin Baitul Haram, mika wuya ga<br />

bin umarni da cikakkiyar zuciya wannan dole.<br />

Kuma akwai wani amfani sauya Al Kibla shine a tsame munafukai da Musulmi na<br />

hakika. Allah SWT yace cikin suratul Baqarah, aya ta 143 :<br />

" Mun maida Kibla wanda kuka kasance kuna bi, domin kawai a jarrabai wadanda<br />

suke bin Annabi Muhammad SAW da wadanda suka juya baya".<br />

Kamar yadda ya zo a Hadisi a cikin Musnad Ahmad wanda aka karbo daga A'isha<br />

RA, cewa Annabi Muhammad yace " Mabiya littafi suna bakin ciki da Musulmi a<br />

kan dalilai guda uku.<br />

Na farko: Allah SWT ya tsaida rana ta ibada kowane sati ga al'umma da suka<br />

wuce, asabar ga yahudawa, ranar lahadi ga kiristoci, sai kuma juma'a an zabe ta<br />

ga Musulmi. Abu na biyu, wannnan sauyin Al Kibla. Abu na uku, shine cewa Amin<br />

da ake yi bayan liman. Mabiya littafi basu sami wadannan abubuwa ba.<br />

Ka rike wani lokaci Al Qur'ani yana shafe Sunnah, idan kuma ba a shafe ta ba<br />

hukuncin daya dana Al Qur'ni. A misali, da farko Kibla ba a ambace ta ba a Al


Qur'ani Musulmi suna bin Sunnah. Sai kuma Al Qur'ani aka sauya ta amma Al<br />

Qur'ani ya tabbatar da salloli da aka yi ta bin Sunnah ba a yi asarar su ba.<br />

Kamar yadda ya zo a Hadisin Bukhari da Muslim, sauyin Kibla ya faru ne yayin da<br />

Annabi Muhammad SAW yake yin sallar Asr. Ko da yake wadansu ruwayoyin sun<br />

ce Zuhr (kamar yadda ya zo a IBN KATHEER)<br />

Wadansu sahabban sun kamala sallar su da Annabi Muhammad SAW, sai suka<br />

gani cewa wadansu 'yan uwan su dake makwabtakan su suna yi sallar suna dubar<br />

Al Kuds, sai sahabban daga murya suka ce masu " Mun yi salla da Annabi SAW<br />

muna dubar Baitullah sai suka juya yayin da suke yin salla. Ba tare da wani jinkiri<br />

ko tambayoyi da sauransu ba. Wannan abinda ya afku ya fiddo cewa a dalilin<br />

mutum a matsayin shaida ya isa a wadasu abubuwa.<br />

Sauyin Al Qur'ani yaje Quba a wannan rana. Kamar yadda aka ce a Bukhari da<br />

Muslim mutanen Quba' ma sun juya Al Kibla wajen salla a lokacin da suka sami<br />

sanarwa daga bakin mutum daya. Wananna ya gwada yadda mutuntawa da<br />

aminci da amana da sahabban Annabi AS suke yi.<br />

Ya zo a Hadisin Bukhari a ruwayar Ibn Azib lokacin da aka sauya Al Kibla zuwa<br />

masallacin Baitil Haram, mutane suka tambayi Annabi SAW game da Musulmi<br />

wadanda suka mutum kuma suna bin a Al Kibla. Allah SWT ya amsa wannan a<br />

aya ta gaba ta cewa sallar su ba zata kasance asara ba Allah ya karbe ta. Suratul<br />

Baqarah aya ta 143:<br />

" Allah ba zai taba maida imanin ku (sallar ku) ta kasance asara".<br />

Yana da ban-sha'awa mu sani cewa imani an amfani da shi a maimakon salla a<br />

wannan ayar. A nan babu imani matukar babu tsaida salla. A wata fadar salla ita<br />

ce abinda yake gwada imanin mutum.<br />

Ya Allah SWT ka bamu ikon yin salla koda yaushe domin mu kara imanin mu ya<br />

Allah SWT da hada kan Musulmin duniya wadanda suke bin Al Kibla daya, Amin.

Hooray! Your file is uploaded and ready to be published.

Saved successfully!

Ooh no, something went wrong!