Ɗaukaka Ga Allah - Family Radio Worldwide
Ɗaukaka Ga Allah - Family Radio Worldwide
Ɗaukaka Ga Allah - Family Radio Worldwide
Create successful ePaper yourself
Turn your PDF publications into a flip-book with our unique Google optimized e-Paper software.
kuma tushen gaskiya na Littafi Mai-Tsarki, kowacce majami’a tana da<br />
damar ruhaniya ta koyarwa, idan ya yiwu kuma, su gyara duk abin da<br />
wata aya a cikin Littafi Mai-Tsarki take koyarwa, domin Ikklisiya ce jigon<br />
gaskiya. A ɓangare ɗaya kuma, idan <strong>Allah</strong> shine jigo da kuma tushen<br />
gaskiya, hanya guda ɗaya da za mu gane abinda ake koyawa a cikin ayar<br />
da take da wuya shine, ta wajen binciken Littafi Mai-Tsarki a hankali tare<br />
da yin addu’a ga <strong>Allah</strong> domin ya bayyana gaskiyar ta wurin Maganar sa,<br />
Littafi Mai-Tsarki. Babu shakka gaskiyar koyarwar wannan ayar ke nan.<br />
Haka kuma, <strong>Allah</strong> ya ɓoye gaskiya da dama a cikin Littafi Mai-<br />
Tsarki da ke da dangantaka da shirin hukuncin <strong>Allah</strong>. Ayoyi da dama<br />
suna koyaswa a fili kuma daidai, abinda aka saba koyarwa bisa ga al’ada<br />
cewa, a ƙarshen duniya, <strong>Allah</strong> zai tashi dukan waɗanda suka mutu ba<br />
tare da zama zaɓaɓɓu ba, daga mattatu domin su bayyana a gaban<br />
shari’ar Kristi. Za a same su da laifi a kuma yanke masu hukunci maitsanani,<br />
su kuma sha azaba can gaba a wani wurin da ake kira<br />
jahannama.<br />
Za a kuma iya fahimtar waɗannan ayoyin da kyau a kan cewa<br />
suna koyarwar da ta amince da koyaswar cewa za a shafe duniya baki<br />
ɗaya tare da dukan waɗanda ba zaɓaɓɓu ba da basu da ceto a ranar 21<br />
ga watan Octoba shekara ta 2011.<br />
Misali, Litttafi Mai-Tsarki, ya yi Magana kan “Madauwamiyar hallaka” ko<br />
‘‘ƙorama ta wuta marar mutuwa’’. Za a iya fahimtar waɗannan kalmomin<br />
da cewa irin wannan hukumcin ko kuma wutar tana da tsanani da zata<br />
shafe wanda aka yankewa irin wannan hukumcin, yadda ba zai sake<br />
rayuwa ba.<br />
Ta yaya zamu gane ko menene daidai? Zamu san abinda ke<br />
daidai yayin da muka bincike Littafi Mai-Tsarki muka tarar cewa ba a yi<br />
amfani da wannan kalmar ‘‘rai’’, ko ‘‘rayuwa’’ dangane da waɗanda suka<br />
mutu ba tare da sun tuba ba, da kuma waɗanda aka ta da su daga<br />
matattu (ka dubi: Tashin waɗanda basu da ceto daga matattu a shafi ...).<br />
Tilas mu tuna cewa sai mutum yana da rai kafin ya daure azaba.<br />
Bugu da ƙari, <strong>Allah</strong> a cikin yalwar alherinsa ya bamu misalin<br />
wutar har abada. Lokacin da aka hallaka Sodom wutar ta ci gaba da ci na<br />
’yan kwanaki ƙalilan kawai. Duk da haka, an yi magana a kan wutar da ta<br />
hallaka Saduma da <strong>Ga</strong>muratu a matsayin ‘‘wuta ta har abada’’. Mun<br />
karanta a cikin wasiƙa ta yahuda sura 7 cewa:<br />
Kamar yadda Saduma da <strong>Ga</strong>murata, da birane na wajensu, da shi<br />
ke tare da su suke, bada kansu ga fasikanci, suka biɗi kwaɗai ba<br />
irin na tabi’a ba, an nuna su, kamar misalin wuta ta har abada,<br />
cikin hukunci da suke har abada.<br />
Saboda haka, zamu iya tabbatar da cewa bisa ga waɗannan<br />
dalilai da waɗansu dalilai na Littafin Mai-Tsarki, zamu iya gane cewa<br />
fahimta irin wadda aka saba bisa al’ada bata da madogara. Idan wanda<br />
5