11.01.2013 Views

Ɗaukaka Ga Allah - Family Radio Worldwide

Ɗaukaka Ga Allah - Family Radio Worldwide

Ɗaukaka Ga Allah - Family Radio Worldwide

SHOW MORE
SHOW LESS

You also want an ePaper? Increase the reach of your titles

YUMPU automatically turns print PDFs into web optimized ePapers that Google loves.

Alkawari. Mun gane da cewa yanayin da aka yi amfani da kalmar ya<br />

danganta daga waɗannan.<br />

1. Azabar marasa bi yayin da suke jin bisharar gaskiya (Ruya ta<br />

Yohanna 11:10).<br />

2. Azaba irin ta rashin lafiya (Matta 8:6, Matta 4:24).<br />

3. Azaba ta harbin kunama (Ruyata Yohanna 9:5).<br />

4. Kalmar Helenanci da aka fassarata “Azaba” an kuma fassara<br />

ta da ‘‘ɓacin zuciya’’ ko kuma ‘‘fushi’’, lokacin da Littafi Mai-<br />

Tsarki yayi Magana game da ruhun Lutu mai-adalci da ya<br />

‘‘fusata’’sabili da zunuban Saduma. (Bitrus II 2:8).<br />

5. A helenanci wannan kalmar “azaba” an fassarata “Baƙin ciki”<br />

(Luka 2:48, Ayyukan manzani 20:38).<br />

6. Azaba da wuta (Ruya ta Yohanna 14:10, Luka 16:24).<br />

Mun koyi cewa ƙarshen shari’ar <strong>Allah</strong> mutuwa ce. Littafi Mai-<br />

Tsarki ya goyi bayan wannan bayanin ta wajen amfani da kalamai kamar<br />

“lalacewa” “hallakarwa”. Za a kuma iya gane cewa an yi amfani da<br />

kalamai kamar, ‘‘mutuwa’’, da ‘‘mutu’’, fiye da sau 1,300 a cikin Littafi<br />

Mai-Tsarki. Ba abin mamaki bane da Littafi Mai-Tsarki ya bayyana da<br />

cewa maƙiyi na ƙarshe da za a hallaka shine mutuwa. (Korintiyawa<br />

15:26)<br />

Mai Arziki Da La’azaru<br />

Yanzu zamu sake nazarin misalin mai-arziki da La’azaru wanda<br />

ke cikin Luka 16. Rashin fahimtar wannan misali ya kawo rashin<br />

fahimtar tsarin shari’ar <strong>Allah</strong>.<br />

Misalin yayi bayani a kan mutane biyu. Mai-arziki yana da duk<br />

abin jin daɗi da wadata da wannan duniya zata iya kawowa, amma ba shi<br />

da ceto. Matalauci La’azaru baya da waɗannan abubuwan jin daɗi na<br />

wannan duniya amma yana da ceto. Daga ƙarshe dukansu suka mutu,<br />

aka binne mai-arziki shi kuma La’azaru mala’iku suka ɗauke shi zuwa<br />

ƙirjin Ibrahim (Luka 16:22). Kasancewa a ƙirjin Ibrahim hoto ne na<br />

kasancewa a wuri mafi albarka a gaban <strong>Allah</strong>. A binne kuma shine a sa<br />

mutum a kabari.<br />

Misali kuma ya ci gaba da magana tsakanin mai- arzikin da ya<br />

mutu da Ibrahim (<strong>Allah</strong>) wanda yake cikin sama. Ka tuna mun koya cewa<br />

kabari da mutuwa daidai suke da jahannama. Saboda haka ba kuskure<br />

bane a ce mai arziki yana jahannama (Luka 16:23). Amma tilas ne mu<br />

gane cewa ɗaga idanunsa ya ga la’azaru a ƙirjin ibrahim, ya kuma yi<br />

magana da Ibrahim duka misali ne. Watau, <strong>Allah</strong> ya shimfiɗa waɗansu<br />

jadawalin tunani ko kuma hotuna masu kusurwai uku, domin ya koya<br />

gaskiyar ruhaniya. Waɗannan gaskiyar sun ƙunshi koyaswa kamar haka:<br />

31

Hooray! Your file is uploaded and ready to be published.

Saved successfully!

Ooh no, something went wrong!