Ɗaukaka Ga Allah - Family Radio Worldwide
Ɗaukaka Ga Allah - Family Radio Worldwide
Ɗaukaka Ga Allah - Family Radio Worldwide
You also want an ePaper? Increase the reach of your titles
YUMPU automatically turns print PDFs into web optimized ePapers that Google loves.
tilas a hukumta shi kamar wanda har yanzu yake ɗauke da zunuban<br />
waɗanda aka kiraye su zuwa ga ceto domin ya nuna yadda ya sha<br />
wahala sabili da waɗannan zunuban. Abin mamaki shi ne babban firist<br />
ɗin ne ya yankewa Yesu hukumci. Matta 20:18 ta ce:<br />
<strong>Ga</strong>shi zamu Urushalima, kuma za a ba da Ɗan Mutun ga hannun<br />
manyan malamai da marubuta, zasu hukunta masa mutuwa.<br />
Yahanna 11:50-51 ta ce:<br />
Ba ku lura kuma yana da amfani a gare ku mutun da ya mutu<br />
saboda jama’a kada al’umma duka ta lalace wannan batu fa ya<br />
faɗa ba bisa kansa ba amma domin shi baban malami ne<br />
shekaran nan yayi annabci Yesu zaya mutu saboda al’umman.<br />
kuma a cikin Yohanna 19:17 mun karata cewa:<br />
Yahudawa suka amsa suka ce masa muna da doka bisa ga<br />
wannan doka kwa ya kamata shi mutu domin ya maida kansa<br />
Ɗan <strong>Allah</strong>.<br />
A ko ina cikin Littafi Mai-Tsarki babban Limami misalin Yesu ne<br />
babban Limami. Hakin babban Limami ne ya yanka rago.<br />
Saboda haka Bilatus gwamna ne, wanda yake da ikon yankewa<br />
Yesu hukuncin kisa domin ya farantawa Yahudawa rai, ya bada umarni<br />
cewa a kashe Yesu ta hanyar giciyewa. Giciyewa bisa ga dukan alamu, ita<br />
ce hanyar kisa mafi kunyatarwa da mutum ya shirya. Mun koyi<br />
muhimman darussa guda uku game da giciye Yesu. Da waɗannan:<br />
1. Kunya, da la’ana da azaba da Kristi ya daure don zunuban<br />
mu.<br />
2. Kunya da la’ana da tilas za a ɗora bisa waɗanda ba a cece su<br />
ba da kuma ƙarin azaba da za’a jimre ga waɗanda zasu shiga<br />
da rai ranar sharia.<br />
3. Abin mamaki na gafara na dab da ƙarshe.<br />
Lokacin da aka giciye Kristi, ya zama abin nuni ga jama’a na<br />
mutumin da yake ƙalƙashin la’anar <strong>Allah</strong>. Domin mu gane<br />
muhimmancin la’ana, bari mu dubi itacen ɓauren nan da Yesu ya la’anta<br />
(Markus 11:14). An la’anta itacen ɓauren da yake wakiltar al’umar Isra’ila<br />
duk zamanin Tsohon Alkawari lokacin da Kristi ya ce “kada kowa ya ci<br />
‘ya’ya daga wurinka, nan gaba har abada.’’ Saboda haka la’anar itacen<br />
ɓauren yana koya mana cewa an hallaka al’umar Isra’ila har abada, ba<br />
kuma za a sake amfani da ita ba a matsayin hanyar samun albarka ta<br />
ruhaniya.<br />
39