Ɗaukaka Ga Allah - Family Radio Worldwide
Ɗaukaka Ga Allah - Family Radio Worldwide
Ɗaukaka Ga Allah - Family Radio Worldwide
Create successful ePaper yourself
Turn your PDF publications into a flip-book with our unique Google optimized e-Paper software.
’ya’ya. Waɗannan ’ya’yan su ma zasu yi tsawon rai har su kai ga lokacin<br />
da zasu haifi ’ya’ya da sauransu. Har sai an haifi dukan waɗanda <strong>Allah</strong> ya<br />
zaɓa ya kuma ceto daga hukuncin mutuwa sakamakon zunubi. Da shike<br />
ba za a haifi da dama daga cikin waɗanda aka zaɓa domin a cece su<br />
daga zunubai ba sai kusan ƙarshen shekaru 13,000 bayan hallitta,<br />
duniya za ta ci gaba daga wancan lokacin.<br />
Saboda haka gaskiya ne cewa iyayenmu na farko, da kuma dukan<br />
bil’adama da suka fito daga jikunansu, sun mutu da shike ba mu da<br />
sauran rai a cikin Kristi wanda muke kira rai na ruhaniya. Kuma mun<br />
karɓi hukuncin mutuwa ta jiki lokacin da Adamu da Hauwa’u suka yi<br />
zunubi. Amma <strong>Allah</strong> ya tanada cewa mutane zasu kasance a raye suna<br />
da ruhu na wani lokaci daga lokacin ɗaukar ciki zuwa bayan shekaru 900<br />
na rayuwa ta jiki. Amma a cikin ruhaniya dukan su matattu ne. Rai cikin<br />
Kristi wanda ya zama rai na har abada yayin da aka ceci zaɓaɓɓen, baya<br />
cikin rayuwar waɗanda ba a cece su ba. Illar zunubi da ya shiga cikin<br />
’yan adam lokacin da Adamu da Hauwa’u suka yi zunubi ya bi kan duk<br />
zuriyarsu. Zunubi yana mulki a cikin jikinsu da kuma ruhaniya.<br />
Littafi Mai-Tsarki ya nace cewa ’yan adam sun mutu cikin<br />
zunubi. Shaidar wannan mutuwa ta ruhaniya shine babu mutumin da bai<br />
taɓa aikata zunubi ba sai Yesu kaɗai. (Romawa 5:12, II Korintiyawa 5:21,<br />
I Bitrus 2:22). Kowanne zunubi yana sa hukumcin mutuwa ta jiki da aka<br />
zartas a kan mai zunubi ya fita fili.<br />
Muna amfani da kalmomin nan “mutuwa ta ruhaniya” yayin da<br />
muke magana akan wanda basu da ceto; Littafi Mai-Tsarki ya ambace su<br />
da cewa sun “mutu cikin zunubi” (Afisawa 2:5, Kolosiyawa 2:13) An raba<br />
su da rai a cikin <strong>Allah</strong> ta jiki da kuma ruhaniya, wanda shine rai na<br />
ruhaniya da suke da shi daga farko kafin Adamu yayi zunubi. Ka iya<br />
tunawa duk ’yan adam daga tsatson Adamu suka fito, saboda haka<br />
lokacin da yayi zunubi, dukan mu muka yi zunubi (Korintiyawa I 15:22).<br />
Ko da shike an yanke su daga rai cikin <strong>Allah</strong>, zasu ci gaba da rayuwa ta<br />
jiki (rayuwa da sanin abinda ke faruwa kewaye da su), a cikin jiki da<br />
kuma ruhu. Rayuwa ta jiki ta kan zo ƙarshe lokacin da mutum ya mutu,<br />
kuma idan ba ya da ceto, cikin jiki da kuma ruhaniya, zai yi mutuwa ta<br />
har abada. Tilas ne a ba mutum sabon ruhu da sabon jiki kafin ya sami<br />
rai cikin Kristi ko rai na har abada.<br />
An bada wannan ran cikin Kristi ga kowane mutum da <strong>Allah</strong> ya<br />
zaɓa domin ya sami ceto. Ana ba da shi ga mutumin da aka zaɓa yayin<br />
da <strong>Allah</strong> ya yi amfani da Maganar <strong>Allah</strong> a rayuwar mutumin. A daidai<br />
lokacin za a maye tsohon jiki da ruhun mutumin da sabon rayayyen<br />
ruhu madauwami wanda ba zai so ya sake aikata zunubi ba (IYohanna<br />
3:9). Zai ci gaba da rayuwa a cikin mattacen jikinsa na ruhaniya amma<br />
yana da tabbacin cewa a lokacin fyaucewa, za a sake mattacen jikinsa na<br />
ruhaniya nan da nan zuwa rai na har abada a cikin jikin Kristi<br />
(Tassalonikawa I 4:13-17, Korintiyawa 15:51-52).<br />
45